tarbiyyar `ya`ya a musulunci
DESCRIPTION
This book describes the Islamic manner of upbringing based on the teachings of the Qur'an and Sunnah in the light of the salaf saaliheenTRANSCRIPT
1
ABUBUWAN DA KE CIKIN LITTAFIN
Muqaddima 3
Ma’anar tarbiyya 6
Hukuncin tarbiyya 9
Manufar tarbiyya a Musulunci 14
Himmar Magabata wajen tarbiyyar `ya`ya 16
Vangarorin tarbiyya 23
Wuraren da a ke samun tarbiyya 26
Hanyoyin koyar da tarbiyya 34
Haxarin sakaci game da tarbiyyar `ya`ya 42
Yadda a ke yin tarbiyyar `ya`ya 51
Qalubalen da ke fuskantar tarbiyya 152
Kammalawa 175
Daga cikin littafan da aka yi amfani da su 176
FA’IDODIN DA KE QASAR LAYI (HASHIYA)
Siffofin mace ta qwarai da hanyoyin faranta wa miji rai 18
Hukuncin auren mace fiye da huxu 20
Faxakarwa game da littafin Tarbiyyatul Awlād na Ulwān 23
Falalar masallaci 30
Huxubar Juma’a ko idi cikin harshen Hausa 31
Fa’idodin auren wuri 48
Matsayin auren dole 49
Ladubban da suka shafi jariri/jaririya 53
Daidaituwar Allah a kan Al’arshi 59
Sharuxxan kalmar shahada da abubuwan da ke warware ta 62
Wajibcin riqo da Alqur’ani da Sunnah 65
Siffofin Ahlus-Sunnah da asasin da’awarsu 67
Matsayin Manzon Allah (SAW) 69
Alamomin son Allah (Maxaukaki) da ManzonSa (SAW) 70
Hukuncin zagin Manzon Allah (SAW) 71
2
Aqidar Ahlus-Sunnah game da Sahabbai 72
Ma’anar Ahlul-Baiti da matsayinsu a wajen Ahlus-Sunnah 73
Hanyoyin neman na kai 74
Hukunce-hukuncen addu’a 78
Haxarin zunubi ga rayuwar Musulmi 80
Ma’anar bidi’a, da illolinta, da siffofin `yan bidi’a 82
Bidi’o’in da a ke yi a cikin watannin shekara 86
Hukuncin rawa ko kixa a wurin zikiri 89
Rigakafin Shan Inna (Polio) 90
Falalar zikiri da ladubbansa 94
Muhimmancin ilmi a rayuwar Musulmi 97
Wajibcin dogaro da kai, da haramcin maula da barace-barace 100
Hukunce-hukuncen jinin al’ada 108
Kyawawan xabi’u 111
Munanan xabi’u 112
Shan taba sigari 115
Amsa sallamar kirista ko bayahude 118
Falalar Salati ga Manzon Allah (SAW) 121
`Yan’uwantakar Musulunci da hanyoyin tabbatar da ita 126
Ladubban savani 127
Haxarin sanya tufafi ya wuce idon qafa a haqqin maza 138
Sharuxxan hijabin mace Musulma 141
Savanin malamai game da niqabi 142
Fa’idodin sanya hijabi 145
Muhimmancin lokaci a rayuwar Musulmi 147
Haxarin finafinai 148
Matsayin da’awa da yadda a ke gudanar da ita 150
Matsalar talauci da hanyoyin magance ta 153
Munanan aqidun da ke karen-tsaye ga tarbiyya 154
Haqqoqin ma’aura da hanyoyin warware savani a tsakaninsu 164
Matsayin mace da gudummuwar ta a Musulunci 168
Hanyoyin kyautata mu’amala da `ya`ya 172
Matsalar maraici 173
3
MUQADDIMA
Godiya ta tabbata ga Allah; muna gode maSa, muna neman
taimakonSa, muna neman gafararSa, kuma muna neman
tsarinSa daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu.
Wanda Allah Ya shiryar babu mai vatar da shi, wanda Ya
vatar babu mai shiryar da shi. Kuma ina shaidawa babu
wanda a ke bauta wa bisa cancanta sai Allah, Shi kaxai, ba
Shi da abokin tarayya. Kuma ina shaidawa Muhammad
bawanSa ne kuma ManzonSa.
‚Ya ku waxanda suka yi imani! Ku bi Allah da taqawa, a
kan haqqin binSa da taqawa, kuma kada ku mutu face kuna
masu sallamawa (Musulmi)‛1
‚Ya ku mutane! Ku bi Ubangijinku da taqawa, Wanda Ya
halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi,
ma'auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza masu yawa
da mata. Kuma ku bi Allah da taqawa, Wanda kuke roqon
juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta. Lalle ne Allah Ya
kasance, a kanku, Mai tsaro ne.‛2
‚Ya ku waxanda suka yi imani! Ku bi Allah da taqawa,
kuma ku faxi magana madaidaiciya. Ya kyautata muku
ayyukanku, kuma Ya gafarta zunubanku. Kuma wanda ya yi
xa'a ga Allah da ManzonSa, to, lalle, ya rabanta, babban
rabo mai girma.‛3
Bayan haka: Lallai, mafi kyawun magana, (shi ne) littafin
Allah, kuma mafi kyawun shiriya, (ita ce) shiriyar
Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).
Kuma mafi munin al'amura, (su ne) abubuwan da aka qago 1 Aal Imrān, 3:102
2 Nisā, 4:1
3 Ahzāb, 33:70-71
4
(a cikin addini). Domin dukkan qagaggun abubuwa
(waxanda ba su da asali a cikin Alqur'ani da Sunnah) bidi'a
ce, kuma dukkan bidi'a vata ce, kuma dukkan vata
(makomarta) cikin wuta.
Bayan haka:
Daga lokacin da littafi na, Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci, ya fito, mutane sun nuna matuqar
buqatar hanzarta fitar da littafin da na rubuta a kan tarbiyyar
`ya`ya, wanda na yi ishara zuwa gare shi a cikin wancan
littafi, don ya zamanto cikamaki gare shi. Kasancewar,
mutane sun nuna gamsuwarsu da wancan, da kuma
matsuwarsu ga wannan, na ga dacewar in sake yin bitar
littafin, duk da irin yawan ayyukan da ke gabana, domin a
fitar da shi ga `yan’uwa Musulmi, musamman waxanda
suka ba al’amarin tarbiyya muhimmanci.
Na yi amfani da tsarin rubutu a qasar layin da ke qarshen
shafi, wato, hashiya, domin qara fito da waxansu mas’aloli,
da kuma bayyana waxansu fa’idodin da suka shafi vangarori
na musamman a cikin littafin. Ina ba mai karatu shawarar
bin hashiyar littafin a lokacin da ya ke karantawa,
kasancewar za ta taimaka masa wajen kyautata fahimtar
saqon da ke ciki.
Ina roqon Allah (Mai girma da xaukaka) Ya karvi wannan
xan aiki a matsayin ibada, Ya ba ni ladan da Ya tanadar wa
waxanda ke qoqarin karatu da karantar da addininSa, kuma
Ya yi sakamakon alhairi ga waxanda suka taimaka, ta
kowace hanya, wajen tabbatar littafin. Ina roqon Allah Ya
yafe mani kurakuran da ke ciki.
5
Haka kuma, ina roqon waxanda suka ga kuskure a cikin
littafin, su faxakar da ni, domin a qara kyautata shi idan za a
sake bugawa nan gaba.
Ahmad Bello Dogarawa, Abū Abdir-Rahmān
Al-Muharram, 1430
6
MA’ANAR TARBIYYA
Kalmar ‘tarbiyya ( )’, kalma ce ta larabci, da bahaushe ya
hausantar, ta yadda da zarar an ambace ta, duk wanda ke jin
Hausa sosai, zai fahimci abin da a ke nufi. Kalmar na da
ma’ana ta harshe, da ma’ana ta Shari’ah.
A harshen larabci, mafi yawan malamai sun ce asalin kalmar
‘tarbiyya’ daga ‘ ’ ne, wato qaruwa da daxuwa, kamar
yadda ma’anar ta zo a cikin Alqur’ani [Hajj, 22:5; Baqarah, 2:276; Rūm, 30:39; Hāqqah, 69:10]; ko kuma daga fi’ilin
‘ ’, wato, ya qara, ya daxa, ko kuma ya rena, kamar yadda
ta zo a cikin Alqur’ani [Isrā, 17:24; Shu’arā, 26:18]. A bisa
waxannan bayanai, kalmar ‘tarbiyya’ na nufin reno, da
kulawa, da ladabtarwa, da karantarwa, da kyautatawa, da
xaukar matakin gina qaramin yaro, kaxan-kaxan, har ya
zama cikakken mutum, a vangaren hankali da tunani, kuma
ya zamanto kammalalle, a wajen mu’amala da wayewa.
A shari’ance, ‘tarbiyya’ na nufin: tattali, da kintsa mutum
domin ya samu cikakkiyar rayuwar da ke qunshe da
walwala; ya zamanto mai qaqqarfar jiki; mai cikakken
hankali; mai cikakken tsarin gudanarwa; mai tausasawa a
cikin mu’amalarsa; qwararre a cikin ayyukansa; kuma mai
jawo amfani ga waninsa. Tarbiyya a musulunci ta qunshi
kyautata al’amarin musulmi, da inganta yanayinsa don ya
zamanto cikakke, a vangaren lafiyarsa, da hankalinsa, da
aqidarsa, da ruhinsa, da xabi’unsa, da mu’amalarsa, da
wayewarsa, ta hanya mafi dacewa, kuma a bisa karantarwar
addinin Musulunci.4
4 Sālih ibn Aliyyu Abu ‘Arrād, At-Tarbiyyatul Islāmiyyah: Al-
Musxalah wal Mafhum, (1426), shafi na 36-37,
http://saaid.net/Doat/arrad/17.htm
7
Bincike ya nuna cewa kalmar ‘tarbiyya’, a yadda a ke
amfani da ita yanzu, ba ta shahara a wajen magabata ba.
Kalma ce da aka fara amfani da ita daga baya. Wannan yasa,
magabata ba su yi amfani da kalmar ba, a cikin rubuce-
rubucensu. A magana mafi qarfi, an fara amfani da kalmar
‘tarbiyya’ ce a cikin qarni na ashirin.5
Kafin wannan lokaci, malamai sun yi amfani da kalmomi
mabambanta, waxanda ke xaukar ma’ana kusan iri xaya da
ma’anar kalmar tarbiyya a yanzu. Daga cikin kalmomin da
aka yi amfani da su, a wancan lokaci, akwai:6
1. At-Tanshi’ah ( ): reno da kulawa ta musamman.7
2. Al-Islāh ( ): canzawa zuwa ga mafifici, da kulawa ta
musamman, da karkata zuwa ga abin da ya fi kyau.
3. At-Ta’adīb ( ): yin ado da siffofi masu kyau, kuma
da koyar da xabi’u da halayen girma, da nisantar
munanan abubuwa.
4. At-Tahzīb ( ): tsaftace zuciyar mutum, da tsarkake
ta, da daidaita ta a kan tarbiyya, a bisa ayyuka masu
daraja, da kyawawan maganganu.8
5. At-Taxhīr ( ): tsarkake rai daga dauxa da abubuwan
qasqanci.
6. At-Tazkiyyah ( ): tsaftace zuciya da tsarkake ta daga
munanan xabi’u da miyagun halaye.
5 Muhammad Munīr Marsī, At-Tarbiyyatul Islāmiyyah: Usuluhā wa
Taxawwuruhā fil Bilādil ‘Arabiyyah, (‘Aalamul Kutub, Al-Qāhirah,
1421), shafi na 48 6 Sālih ibn Aliyyu Abu ‘Arrād, At-Tarbiyyatul Islāmiyyah: Al-
Musxalah wal Mafhum, shafi na 4-18 7 Ibn Khaldun ya yi amfani da wannan Isxilāhi a cikin littafinsa
Muqaddimah 8 Ibn Maskawih ya yi amfani da kalmar a littafinsa Tahzībul Akhlāq wa
Taxhīrul A’arāq, da Al-Jāhiz, a cikin Tahzībul Akhlāq
8
7. At-Ta’alīm ( ): ilmantarwa da zaburarwa zuwa ga
neman ilmi.
8. As-Siyāsah ( ): jagoranci da zurfafa tunani, kafin a
zartar da abin da za a yi.9
9. An-Nushu wal Irshād ( ): shiryarwa zuwa ga
abu mai kyau, ta hanyar lalama da tausasawa.10
10. Al-Akhlāq ( ): gyara xabi’u, da miqar da
karkatattun halaye.11
Kowane xaya daga cikin waxannan kalmomin da suka
shahara a cikin littafan magabata, ya qunshi sashen
ma’anonin da kalmar ‘tarbiyya’ ta qunsa a yau. Ke nan, a
yadda a ke amfani da ita a yanzu, kalmar ‘tarbiyya’ ta
qunshi dukkan ma’anonin da waxancan kalmomi suka
qunsa.
Tarbiyyar Musulunci na da abubuwan da ta kevanta da su,
kuma babu wani tsarin tarbiyya a duniya da ya qunshi irin
abubuwan da tarbiyyar Musulunci ta qunsa. Wannna yasa,
duk da cewa al’ummomin duniya na qoqarin canza tsarin da
su ke bi wajen tarbiyyar mutanensu a halin yanzu, al’ummar
musulmai ba ta buqatar sauyi a cikin nata tsarin.
Tsarin tarbiyyar Musulunci ya kevanta da waxannan
abubuwa:
1. Tsari ne daga Allah da aka gina a bisa asasin Musulunci.
Allah (Maxaukaki) Shi ne da kanSa Ya tarbiyyantar da
malamin farko ga wannan al’umma, wato, Manzon Allah
9 Ibn Al-Jazzār Al-Qairawāni ya yi amfani da wannan isxilahi a littafin
da ya rubuta a kan tarbiyya, Siyāsatu-s-Sibyān wa Tadbīruhum 10
Ibnul Jauzī ya sanya wa littafinsa suna Laftatul Kabad ila Nasīhatil Walad, shi kuma Al-Hārith Al-Mahāsabī ya sanya wa littafinsa suna
Risālatul Mustarshidīn 11
Abu Bakr Al-Aajurri ya sanya wa littafinsa suna Akhlāqul Ulamā
9
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), wanda shi
kuma ya tarbiyyantar da al’ummarsa a bisa shiriya da
karantarwar da Allah (Maxaukaki) Ya yi masa.
2. Gamammen tsari ne, da ya dace da dukkan xan Adam,
ba tare da kevantuwa ga wani gari ko wata al’umma ko
jinsi ba.
3. Tsari ne da ke lazimta wa kowane mutum neman
ilminsa, kuma ya ke lazimta wa kowane malami xaukar
xawainiyar karantar da shi.
4. Tsari ne da ya ba da cikakkiyar kulawa ga dukkan
vangarorin al’umma, da dukkan fannonin ilmi mai
amfani, kuma da dukkan matakan rayuwa.
5. Tsari ne da ke karantar da tsakaitawa, ba tare da
zurfafawa ko taqaitawa ba.
6. Tsari ne mai xorewa, ba tare da yankewa ba.
7. Tsari ne da ya qulla alaqa mai qarfin gaske a tsakanin
tarbiyya da ilmi; ilmi da aiki; rayuwar mutum xaya da
rayuwar al’umma gaba xaya.
8. Tsarin tarbiyya ne da ya kula da al’amuran duniya da
lahira baki xaya.
9. Tsari ne da ya dace da yanayi, da kuma xabi’un da aka
halicci xan Adam a kansu.
10. Tsari ne da ke bi sannu-sannu wajen kai wa ga manufa.
HUKUNCIN TARBIYYA
Tarbiyyar `ya`ya a kan imani da ibada; da xabi’u da
mu’amala; da kula da lafiyar jiki da hankali da tunani; da
tsarin zamantakewa, wajibi ne da Allah Ya xora a kan iyaye
da dangi, da malamai, da shugabanni, da sauran jama’a.
Tarbiyya ba ta samuwa a cikin al’umma, sai kowane xaya
daga waxannan vangarori ya ba da gudummuwarsa, kuma
ya sauke wajibinsa game da tarbiyya.
10
Iyaye su ne a kan gaba wajen wannan al’amari muhimmi,
kasancewar su ne suka haifi `ya`ya, kuma suka fi zama tare
da su. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ba iyaye amanar
`ya`yansu, don su kula da su, su tsare su daga faxawa cikin
haxari, kuma su yi masu kyakkyawar tarbiyya. Allah (Mai
girma da xaukaka) Ya ce: ‚Ya ku waxanda suka yi imani!
Ku kare wa kanku da iyalinku wata wuta (da) makamashinta mutane da duwatsu ne…‛
12 Aliyyu ibn Abi Xālib (Allah Ya
yarda da shi) ya fassara wannan ayar da cewa: ‘Ku ladabtar
da su, wato, ku yi masu tarbiyya, kuma ku ilmantar da su’. Haka kuma, Qatādah (Allah Ya jiqansa) ya fassara da cewa:
‘Ku umurce su da yin xa’a ga Allah, kuma ku hana su savon
Allah’.13
Haka nan, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya ce: ‚Dukkanku masu kiwo ne, kuma za a
tambayi kowa game da kiwonsa: shugaba mai kiwo ne a kan
mutanensa, kuma za a tambaye shi game da kiwonsa.
Mutum (magidanci) mai kiwo ne ga iyalinsa (matansa, da
`ya`yansa, da sauran waxanda ke qarqashinsa), kuma za a
tambaye shi game da kiwonsa. Mace mai kiwo ce ga gidan
mijinta da `ya`yansa, kuma za a tambaye ta game da su.
Bawa makiyayi ne ga dukiyar mai gidansa, kuma za a
tambaye shi game da kiwonsa. Kowannenku makiyayi ne,
kuma za a tambaye shi game da kiwonsa.‛14
`Yan’uwa da dangi na da babban nauyi wajen tabbatar da
tarbiyyar qannensu da danginsu da `ya`yan `yan’uwansu,
kasancewar su ne mafi kusa da su bayan iyayen da suka
haife su. Kasancewar qanne da `ya`yan `yan’uwa na
dangantuwa zuwa gare su, rashin ba da gudummuwarsu
12
Tahrīm, 66:6 13
Ibn Kathīr, Tafsīrul Qur’ānil Azhīm, (Maktabah Anas ibn Mālik,
Makka), 4/362 14
Bukhari da Muslim
11
wajen cinma manufar tarbiyya, da tabbatar da ita gare su, na
iya jawo matsala, musamman idan yara suka aikata wani
mummunar abu. Duk wani aikin assha, da danginsu ko
`ya`yan `yan’uwansu za su aikata, zai shafi mutuncinsu, da
matsayinsu a cikin al’umma. Wannan yasa, Musulunci ya
wajabta wa dangin mutumin da ya yi kisan kai bisa kuskure,
yin haxaka da karo-karo wajen biyan kuxin diyya, idan
wanda ya yi kisan ba shi da dukiyar da zai biya da kansa.15
Ke nan, haxari ne babba ga `yan’uwa, su yi sakaci wajen
tarbiyyar `yan’uwa da danginsu na jini.
Dangane da malamai, Allah (Mai girma da xaukaka) Ya
siffanta su da Rabbaniyyun, wato, malamai na Allah,
waxanda ke yi wa mutane tarbiyya a kan ilmi.16
An ruwaito daga Aliyu ibn Abi Xālib (Allah Ya yarda da shi) ya ce: ‚Su
ne waxanda ke qosar da mutane hikimomi, kuma su ke yi wa mutane tarbiyya a kansu.‛ Haka nan, Mujāhid (Allah Ya
ji qan shi) ya ce: Rabbaniyawa su ne waxanda ke koya wa
mutane qananan ilmi, kafin manya.‛17
Gudummuwar malamai a fagen tarbiyyar al’umma na
qunshe cikin qoqarin yaxa sahihin ilmi; da karantar da
al’umma, da shiryar da ita, da yin mata saiti; da yaqar
bidi’a; da tsaftace ilmi daga hadisai masu rauni, da hadisan
qarya, da ra’ayoyin da babu dalili a kansu; da tarbiyyantar
da al’umma a kan tataccen ilmi; da qalubalantar `yan bidi’a
15
Ana biyan diyya idan an yi kisan ganganci, kuma waliyyan wanda
aka kashe suka ce za su karvi diyya, maimakon a kashe mutumin da ya
kashe masu xan’uwa. Haka kuma, waliyyan mamacin na iya yafe
diyyar gaba xaya, ba tare da la’akari da ko kisan ganganci ne ko na
kuskure ba. Sai dai kuma ko da an yafe diyya, dole ne wanda ya yi
kisan ya `yanta bawa ko ya yi azumin wata biyu, a matsayin kaffara. 16
Aāl Imrān, 3:79; Mā’idah, 5:44 17
Ahmad ibn Abdil-Halīm ibn Taimiyyah, Majmu’ul Fatāwā,
(Maktabah Ibn Taymiyah), 1/62
12
da kuma bidi’o’insu, ta hanyar bayani da rubutu bisa hujjoji;
da kare martabar Alqur’ani da Sunnah, ta hanyar mayar da
martani ga vatattun mutane, da zindiqai, da munafukai, da
sauransu.18
Shugabanni su ne ke xaukar dukkan matakan da suka dace
don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, da bin
doka da oda a tsakanin mutane.19
Haka nan, wajibi ne su
tabbatar da tsaro ga dukiya da rayuka da mutunci da hankali
da addinin jama’a. Waxannan abubuwan ba za su tabbata ba
har sai shugabanni sun yi umurni da kyakkyawa, da hani da
mummuna, kuma sun ba da goyon baya, da qarfafa gwiwa
wajen tarbiyyar mutane. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya
ce: ‚Waxanda su ke idan muka ba su iko (mulki) a cikin
qasa, sai su tsai da salla, kuma su bayar da zakka, kuma su
yi umurni da abin da aka sani, kuma su hana daga abin da ba
a sani ba…‛20
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce: ‚…shugaba mai kiwo ne a kan
mutanensa, kuma za a tambaye shi game da kiwonsa…‛.21
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce: ‚Babu wani bawa da Allah zai ba
shi shugabancin mutane, sannan, ya mutu, yana mai
ha’intarsu, face Allah Ya haramta aljanna gare shi.‛22
Sauran mutanen gari na da rawar da za su taka wajen
tabbatar da tarbiyyar al’ummarsu. Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya wajabta wa muminai
canza duk wani mummunan aiki da suka ga ana aikatawa,
18
www.islamweb.net, Daurul Ulamā fit Tarbiyyatil Islāmiyyah, 98319 19
Wani daga cikin magabata yana cewa:
‚Lallai Allah Yana gusar da varna ta hanyar mulki, irin gusarwar da ba
Ya yi da Alqur’ani‛ 20
Hajj, 22:41 21
Bukhari da Muslim 22
Bukhari da Muslim
13
gwargwadon ikonsu.23
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya tabbatar da cewa
addinin Musulunci ya qunshi nasiha ga kowane musulmi.24
Wannan ke nuna cewa kowane mutum a cikin al’ummarsa,
yana da haqqin taimakawa wajen tabbatar da daidaituwar
al’amura.
Sakaci da rashin tsayuwa da al’amarin tarbiyya, ta hanyar
umurni da kyakkyawa da hani da mummuna, na haifar da
matsaloli ga al’umma baki xaya, waxanda suka haxa da:
Bijirowa ga fushin Allah da azabarSa a duniya. Allah
(Mai tsarki da xaukaka) Ya ce: ‚Kuma ku ji tsoron fitina
wadda ba ta samun waxanda suka yi zalunci daga gare
ku, a keve, kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin
uquba ne.‛25
Dangane da fassarar wannan aya, Ibn Kathīr ya ciro magana daga Ibn Abbās (Allah Ya yarda
da shi) ya ce: ‚Allah Ya umurci muminai da su yi inkarin
dukkan mummuna, ko kuma Ya lulluve su da azaba.‛26
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Idan mutane suka qi hana azzalumi aikata
zalunci, ba wuya Allah Ya lulluve su da uquba.‛27
Haka
kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Babu mutanen da wani daga cikinsu zai
aikata savo, amma su qyale shi, alhali suna da ikon
hanawa, face Allah Ya jarabe su, kafin su mutu.‛28
Qasqanci da wulaqanci za su lulluve su, kuma varna da
gurvacewar al’amura za su bayyana a cikin al’umma.
23
Muslim 24
Muslim 25
Anfāl, 8:25 26
Ibn Kathīr, Tafsīrul Qur’ānil Azhīm, 2/185 27
Abu Dāwud, da Tirmidhi da Ibn Mājah 28
Abu Dāwud da Ibn Mājah
14
Rashin amsa addu’a, kamar yadda Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Ku yi
umurni da kyakkyawa, kuma ku yi hani da mummuna,
tun gabanin ku yi addu’a, amma a qi amsa maku.‛29
MUNAFAR TARBIYYA A MUSULUNCI
Tarbiyyar `ya`ya, ta hanyar koya masu kyawawan halaye da
xabi’u nagari, da karantar da su ilmin addini da ilmin sana’a
yadda ya dace, don su zamanto masu kishin zuci da dogaro
da kai, abu ne da Musulunci ya ba muhimmanci sosai. Da
kyakkyawar tarbiyya ce a ke samar da matasa na gari,
waxanda za su zama tubalan gina qaqqarfar al’umma, masu
kishin Musulunci, masu tsoron Allah, waxanda al’umma za
ta yi alfahari da su, kuma waxanda za su tabbatar da
dokokin Allah a kan qasa.
Haka kuma, da kyakkyawar tarbiyya ce a ke samar da xa na
qwarai, da zai zamanto sanyin ido ( ) ga iyayensa, a nan
duniya, kuma ya yi masu addu’a, idan suka riga shi mutuwa.
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ce: ‚Kuma waxanda su ke
cewa, ‚Ya Ubangijinmu! Ka ba mu sanyin idanu daga
matanmu da zuriyarmu, kuma Ka sanya mu shugabanni ga
masu taqawa.‛30
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce: ‚Idan xan Adam ya mutu, duk
ayyukansa sun yanke, ban da abubuwa guda uku: sadaka
mai gudana; da ilmin da ya bari ana amfani da shi; da xa na
qwarai, da zai yi masa addu’a.‛31
29
Ahmad da Ibn Mājah 30
Furqān, 25:74 31
Bukhari da Muslim
15
Tarbiyyar `ya`ya a Musulunci na da manufofi guda shida:
1. Qoqarin tabbatar da manufar halittar xan Adam. Allah
(Mai tsarki da xaukaka) Ya bayyana cewa Ya halicci
mutane da aljannu ne don su bauta maSa: ‚Kuma Ban
halitta aljannu da mutane ba sai domin su bauta Mini.‛32
Tarbiyya a Musulunci ta qunshi xaukar matakan da suka
dace wajen kyautata al’amarin `ya`ya, da inganta
yanayinsu, a vangaren lafiya, da hankali, da aqida, da
ruhi, da xabi’u, da mu’amala, da wayewa, domin su
zamanto bayin Allah (Mai tsarki da xaukaka) tsantsa,
waxanda za su bi dokokinSa, kuma su tabbatar da
tsarinSa a bayan qasa.
2. Kai wa ga manyan xabi’un girma da halayen qwarai,
waxanda za su taimaka wajen ciyar da al’umma gaba, da
yin mata jagoranci wajen tabbatar da manufar rayuwa.
3. Tattali da qintsi ga rayuwar duniya da lahira, da bin
hanyoyin da suka dace domin samun daddaxar rayuwa a
nan duniya, da babban rabo a lahira.
4. Koyar da hanyoyin dogaro da kai, da kishin addini, da
qoqarin jawo amfani ga al’umma da tunquxe cuta gare
ta, da wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, da
tabbatar da tsaro da kariya ga addini da rayuwa da
dukiya da mutunci da hankali.
5. Gina mafi alhairin al’umma mumina wadda za ta kawo
amfani da jawo ci gaba ga kowa, kuma ta tunkuxe varna
da aibu daga kowa.
32
Zāriyāt, 51:56
16
6. Tabbatar da tsarin gudanarwa da wayewa mafi havaka,
da zaburar da mutane a kan tattalin arziqi mafi bunqasa,
da ilmantar da al’umma tsarin ci gaba da kawo zaman
lafiya da walwala da kwanciyar hankali, da koyar da
shugabanci da jagorancin da ke cike da adalci.
HIMMAR MAGABATA WAJEN TARBIYYAR `YA`YA
Magabata, a cikin al’ummar Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) da waxanda suka gabace ta, sun
ba al’amarin tarbiyyar `ya`yansu matuqar muhimmanci, ba
kawai qananan yara ba, har ma waxanda suka manyanta
daga cikin `ya`yansu. Magabata ba su gushe ba suna
qoqarin tarbiyyantar da su a kan aqida da ibada, da
kyawawan xabi’u da mu’amala, da kyautata alaqa da Allah
(Mai tsarki da xaukaka).
Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya ba mu labarin Annabi Ibrāhīm da `ya`yansa (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare su), da irin matakan da ya xauka wajen ganin ya
tarbiyyantar da su, duk da cewa Allah (Mai tsarki da xaukaka) ya zave su da Annabta.
33 Annabi Ibrāhīm (amincin
Allah ya tabbata a gare shi) ya roqi Allah (Mai tsarki da
xaukaka) Ya azurta shi da salihan `ya`ya;34
Ya nisantar da
shi tare da su daga bautar gumaka;35
kuma Ya sanya shi da zuriyyarsa masu tsai da salla.
36 Haka kuma, Ibrāhīm
(amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya roqi Allah (Mai
girma da xaukaka) Ya sanya zuriyyarsa daga cikin masu yin
jagoranci a cikin imani da taqawa da haquri da da’awa;37
33
Maryam, 19:54; Sāffāt, 37:112 34
Sāffāt, 37:100 35
Ibrāhīm, 14:35 36
Ibrāhīm, 14:40 37
Baqarah, 2:124
17
kuma Ya sanya su masu sallamawa ga Allah (Mai girma da xaukaka).
38 Bayan wannan, Annabi Ibrāhīm (amincin Allah
ya tabbata a gare shi) ya yi wa `ya`yansa wasiyyar su
tabbata a kan addini har zuwa mutuwa.39
Domin ya qara tabbatar da tarbiyyar `ya`yan shi a aikace, Annabi Ibrāhīm ya kasance yana bin diddigin al’amuransu,
hatta bayan sun girma. Misali, Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ba da labarin ziyarar ba zato, wadda Annabi Ibrāhīm ya yi wa xansa Annabi
Ismā’īl (amincin Allah ya tabbata a gare shi) har sau biyu,
domin ya gane wa idonsa halin da xansa ke ciki tare da iyalinsa. A karon farko da Ibrāhīm (amincin Allah ya
tabbata a gare shi) ya kai ziyarar, ya bar wa xansa Ismā’īl
(amincin Allah ya tabbata a gare shi) saqon cewa ya saki
matarsa, kasancewar bai dace ta ci gaba da zama matarsa ba. A karo na biyu kuwa, Ibrāhīm (amincin Allah ya tabbata a
gare shi) ya bar wa xansa wasiyyar cewa ya riqe matar da ya
auro bayan ya saki waccan ta farko, kuma ya kula da ita
sosai.40
Ke nan, a ziyararsa ta farko, Ibrāhīm (amincin Allah ya
tabbata a gare shi) ya fahimci cewa matar da Ismā’īl
(amincin Allah ya tabbata a gare shi) ke aure ba ta dace da
shi ba, kasancewar ba ta da godiya, da sanin ya kamata,
kuma ba ta da rufin asiri a cikin zamantakewarta da mijinta.
Babu shakka, aibi ne babba a samu mace tana da irin
waxannan halaye, musamman saboda mummunar tasirinsu a
kan tarbiyyar `ya`ya. Lokacin da ya koma a karo na biyu, Ibrāhīm (amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya fahimci
38
Baqarah, 2:128 39
Baqarah, 2:132 40
Bukhari
18
cewa xansa ya dace da mace ta qwarai ( ),41
wadda
za ta iya faranta ran mijinta,42
kuma ta taimaka masa wajen
tarbiyyar `ya`ya.
Haka kuma, Allah (Maxaukaki) Ya ba mu labarin addu’ar
da Annabi Zakariya (amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya
yi dangane da samun zuriyya mai kyau,43
wadda za ta yi aiki tuquru domin yardar da Allah;
44 da himmar Annabi Ismā’īl
(amincin Allah ya tabbata a gare shi) wajen umurtar iyalinsa
da salla da zakka da tsare haqqoqin Allah (Maxaukaki);45
da dogon wa’azi da gargaxin da Luqmān
46 ya yi wa xansa a
41
Mace ta qwarai ita ce wadda idan mjinta ya kalle ta, zai yi farin ciki;
idan ya umurce ta, za ta yi biyayya; idan ba ya nan, za ta kiyaye
mutuncinta da dukiyarsa; kuma idan ya yi rantsuwa a kanta, za ta
kuvutar da shi. 42
Faranta wa miji rai ya qunshi abubuwa kamar haka: (1) kyakkyawar
tarba a duk lokacin da miji ya shigo gida (2) lazimtar qamshi mai daxi
da gyara jiki da cava ado (3) daxaxa murya da tsara magana (4)
qwarewa wajen kwanciyar aure da gaggauta ba da kai idan aka fahimci
miji yana da buqatar jima’i (5) wadatar zuci, da yin haquri da kaxan, da
rashin nuna kwaxayin abin duniya (6) godiya da yabawa ga miji a kan
xan abin da ya samu (7) kasancewa tare da miji, musamman a lokacin
tsanani, da taimaka wa miji da kuxi ko kaya, idan da buqatar yin haka
(8) qoqarin zarce sauran mata wajen ilmi da iya abinci da tsafta da
aikin gida da sauransu (9) biyayya a cikin duk abin da bai sava wa
Shari’a ba (10) sanya miji ya huce idan ya yi fushi, ta hanyar ba da
haquri da rarrashi da rashin yin jayayya (11) tsare mutuncin miji da
kulawa da `ya`yansa da gidansa da dukiyarsa, musamman idan ba ya
nan (12) girmama `yan’uwansa da taimaka masu (13) qarfafa masa
gwiwa a cikin biyayya ga Allah (14) tattali, da yin tsuwurwurin
dukiyarsa. 43
Aal Imrān, 3:38 44
Maryam, 19:6 45
Maryam, 19:54-55 46
Luqmān ba Annabi ba ne, kasancewar babu wani dalili a cikin
Alqur’ani ko hadisin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) da ya tabbatar da annabtarsa. Aqidar Ahlus-Sunnah ta ginu a
kan cewa ba a iya tabbatar da annabta ga wani mutum sai ta hanyar
19
kan kaxaita Allah (Mai girma da xaukaka) da bauta, da
wajibcin barin shirka, da muhimmancin taqawa da
muraqaba (kiyaye Allah), da wajibcin tsai da salla da yin
umurni da kyakkyawa da hani da mummuna, da haramcin
wulaqanta mutane ko yin taqama da alfahari gare su, da
sauransu.47
Bayan wannan, ya tabbata cewa Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) da sahabbansa (Allah
Ya yarda da su) sun kasance masu matuqar damuwa da
kulawa game da tarbiyyar `ya`yansu, manya da qanana.
Misali, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya tafi wajen `yarsa Fāximah (Allah Ya yarda da
ita) domin ya sanar da ita cewa zikirorin kwanciyar barci ya
fi muhimmanci a kan kuyangar da ta ke nema a wajensa.48
Kuma ya tabbata cewa yana zuwa gidan Aliyyu ibn Abi Xālib (Allah Ya yarda da shi), ya tashe su daga barci domin
su yi qiyamullaili, wato, sallar dare.49
Haka kuma, yana zuwa ya umurci `ya`yansa su fita sallar īdi.
50
A vangaren sahhabai (Allah Ya yarda da su), ya tabbata
cewa Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ya yi amfani da
sanda wajen ladabtar da `yarsa A’isha (Allah Ya yarda da
ita), matar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) kuma uwar muminai, a lokacin da ta zaunar da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
nassi qarara. A magana mafi qarfi, Luqmān xaya daga cikin bayin
Allah ne, waxanda Allah (Maxaukaki) ya yi wa baiwar ilmi, da hikima,
da fasaha, da himmar tarbiyyar `ya`ya. Duba tafsirin Al-Qurxubi, da Ibn Kathīr, da As-Sa’adiy, a qarqashin Luqmān, 31:13, 16-19, don
qarin bayani. 47
Luqmān, 31:13, 16-19 48
Bukhari 49
Bukhari 50
Ahmad
20
a wajen da babu ruwa, saboda ba ta ga abin wuyanta ba.51
Haka kuma, Umar (Allah Ya yarda da shi) ya shiga wajen
`yarsa Hafsah (Allah Ya yarda da ita), matar Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), domin ya
faxakar da ita cewa kada kishinta52
ga A’isha ya hana ta
51
Muslim 52
Kishi a tsakanin mata yana tasowa ne daga lokacin da namiji ke da
mace fiye da xaya a qarqashinsa. Auren mace fiye da xaya har zuwa
huxu, abu ne da aka shar’anta bisa nassin Alqur’ani da Sunnah da
haxuwar malamai (Ijma’i). Haka nan, auren mace fiye da xaya ya
tabbata a cikin tarihin Annabawa da Manzanni da sahabban Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), kuma ya dace da
xabi’ar xan Adam.
Nassin Alqur’ani da Sunnah, da Ijma’i, da Qiyasi duk sun taqaita
wa kowane musulmi auren mata huxu kawai, ba tare da wuce haka ba.
Haka nan, fatawoyi da tarihi da ayyukan sahabbai (Allah Ya yarda da
su) da tabi’ai da waxanda suka bi hanyarsu, da fahimtar dukkan
malaman tafsiri da malaman hadisi da malaman fiqihu da malaman
usuli sun tabbatar da cewa haramun ne ga kowane musulmi ya tara
mace fiye da huxu a qarqashinsa a lokaci xaya, in ban da qwarqwara, a
lokacin jihadin da aka yi a tsakanin musulmi da kafirai a bisa tsarin da
Alqur’ani da Sunnah da Ijma’i suka tabbatar.
Auren mace fiye da xaya na da dalilai masu yawa. Daga ciki, akwai:
(1) matsalar jinin al’ada ko jinin haihuwa da ke sabbaba wa waxansu
majaze takura (2) mata sun fi maza yawa a duniya (3) kowace macen
da ta balaga tana shirye da yin aure da zarar ta samu miji, savanin
maza, kasancewar namiji sai ya yi shiri da tanadi na musamman (4)
larurar rashin haihuwa (5) yawan tafiye-tafiye.
Sharuxxan auren mace fiye da xaya su ne: ikon yin adalci a tsakanin
mata; da amintuwa daga faxawa cikin fitinar addini a sanadiyyar qara
aure; da ikon biya masu buqatar sha’awa; da ikon ciyarwa. Wanda bai
cika waxannan sharuxxa ba, bai dace ya auri mace fiye da xaya ba.
Kishi a tsakanin mata wani abu ne na xabi’a. A mafi yawan lokaci,
mata na yin kishi ne a tsakaninsu saboda rashin tabbas game da
makomarsu idan miji ya qaro aure; da tsoron juya masu baya ko
wulaqanci daga miji; da tsoron rashin adalci a tsakaninsu da amarya; da
rashin jin daxin yawaita ambaton kishiya a gabansu; da karkatar
`yan’uwan miji da abokansa ga wata daga cikin matan.
21
Ko da ya ke kishi xabi’a ce ta mata, kuma wani abu da ba za a iya
raba mata da shi ba, akwai abubuwan da ba su halatta mace ta aikata ba
saboda kishi: (1) cutar da miji ko hana shi yin sukuni, ko kuma cutar da
`ya`yansa, a matsayin martani a kan sabon auren da ya yi (2) cin
mutunci da yin vatanci ga kishiya (3) cutar da kishiya ta hanyar sihiri
ko tsafi (4) neman a saki kishiya (5) ruxar kishiya ta hanyar nuna mata
kamar miji na fifita ta a kan abokiyar zamanta ko kuma yana bata wani
abu a voye.
Yana daga varnar da aka shigar a cikin mas’alar auren mace fiye da
xaya, da’awar da waxansu ke yi cewa ya halatta mutum ya ajiye mace
fiye da huxu a qarqashinsa a lokaci xaya, a matsayin matan aure.
Asalin wannan da’awar a Nijeriya, ta samo asali ne daga `yan qala-
qato, waxanda babu ruwansu da hadisan Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi). Daga baya, sai aka samu labarin
mutumin da ya ajiye matan aure fiye da tamanin a lokaci xaya. Da aka
ce masa ya zavi guda huxu daga cikinsu, ya saki sauran, sai ya ce ‘an
takura shi ne saboda ba shi da gata, domin kuwa waxansu shaihunnan
xariqa da sarakunan gargajiya na da mata barkatai a qarqashinsu’. Ana
cikin wannan kace-nace, kwatsam sai ga wani matashin xalibin ilmi a
garin Bidda, jihar Neja, da ke da’awar Sunnah-Salafiyyah yana iqirarin
cewa babu ijma’i a kan haramcin zaman aure tare da mace fiye da guda
huxu a lokaci xaya, yana mai kafa hujja da bayanan da ya gani a cikin littafin Nailul Awxār da tafsirin Fat-hul Qadīr na Imam ash-Shaukāni,
da kuma bayanan da Jamāluddīn Al-Qāsimi ya yi a cikin tafsirinsa,
Mahāsinut Ta’awīl, cewa babu ijma’i a kan wannan mas’alar.
Duk da cewa an shirya taron qara wa juna ilmi na kwana biyu, kuma
aka gayyaci mutane daga wurare dabam daban na wannan qasa domin
su gabatar da maqala/qasidu a cikin harshen Hausa da Turanci da
Nufanci dangane da wannan mas’ala, wannan xalibi ya qi zuwa, duk da
an ba mu labarin cewa kafin ranar taron, ya yi alqawarin zai halarta.
Alhamdu Lillah, ina daga cikin waxanda suka gabatar da maqala a
wajen taron. Haka kuma, Dokta Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo, da Shaikh Abdul-Wahhāb Abdullah Kano, da Mal. Aminu Gusau, da
Mal. Auwal Maiduguri, da wakilin kwamitin Shari’a na qasa, da
waxansu `yan’uwa daga wurare dabam daban sun gabatar da bayanai
gamsassu a wajen taron. A qarshe, mutanen Bidda da sauran musulmin
Nijeriya, waxanda suka samu labarin sakamakon taron, sun gamsu
cewa Alqur’ani da Sunnah, da Ijma’i, da Qiyasi, da fatawoyi da tarihi
da ayyukan sahabbai (Allah Ya yarda da su) da tabi’ai da waxanda
suka bi hanyarsu, da fahimtar dukkan malaman tafsiri da malaman
22
kwanciyar hankali, ko ya kai ta ga aikata abin da bai dace
ba.53
Waxannan misalai na nuna irin muhimmancin da magabata
suka ba al’amarin tarbiyya, da irin matakan da suka xauka
wajen tarbiyyantar da `ya`yansu da matansu da sauran
waxanda ke qarqashinsu. Abin sha’awa shi ne, magabata ba
su taqaita tarbiyya a kan qananan yara ba, a’a, har manya
ana yin masu tarbiyya gwargwadon yadda kowannensu ke
buqata.
hadisi da malaman fiqihu da malaman usuli da malaman tarihi duk sun
tabbatar da haramcin ajiye matan aure fiye da huxu a lokaci xaya, kuma maganar da Shaukāni da Jamāluddīn Al-Qāsimi suka yi, babu
hujja a cikinta. Hasali ma, ra’ayin da suka danganta wa wasu daga cikin
malaman Shi’a, kuskure ne, kasancewar bai tabbata daga gare su ba.
Kasancewar an rushe dukkan rikice-rikice da hayaniyar da ya ke
taqama da su, sai kwatsam ya fasa wani sabon bom; ya ce wai Umar ibn Khaxxāb (Allah Ya yarda da shi) ya mutu ya bar matan aure fiye da
huxu a qarqashinsa! Gaskiya ne cewa Umar (Allah Ya yarda da shi) ya
auri mace fiye da huxu a cikin rayuwarsa, amma kuma, bai tava zama
tare da mace fiye da huxu ba a lokaci xaya. Sanannen abu ne cewa, a
cikin sahabbai, akwai waxanda suka auri mata da yawa a cikin
rayuwarsu, amma ba su tava zama da guda uku ba ma a lokaci xaya,
ballantana huxu ko fiye da huxu. 53
Bukhari
23
VANGARORIN TARBIYYA54
54
Mafi yawan bayanan da ke qarqashin wannan sashe na ciro su ne daga littafan Abdullah Nāsih Ulwān, Tarbiyyatul Awlād fil Islām,
(Dārus-Salām lix-Xibā’ah wan-Nashr wat-Tauzi’ wat-Tarjamah, Al-
Qāhirah, 2005), shafi na 132-137; da Mas’uliyyatut Tarbiyyatil Jinsiyyah min Wijhati Nazaril Islam, (Dārus-Salām lix-Xibā’ah wan-
Nashr wat-Tauzi’ wat-Tarjamah, Al-Qāhirah, 2003).
Littafin Tarbiyyatul Awlād fil Islām na Abdullah Nāsih Ulwān na
daga cikin littafan tarbiyya waxanda suka shahara a cikin al’umma,
kuma ana yawan karantar da shi a masallatai da wuraren karatu. Nazari
cikin littafin yana nuna cewa, mawallafinsa, Allah Ya jiqansa, ya yi
kura-kurai masu yawan gaske, musamman a vangarorin tauhidi da
aqida da manhaj. Wannan yasa malamai suka yi rubuce-rubuce don
faxakarwa game da matsalolin da ke cikin littafin, kuma suka yi gyare-
gyaren da ya kamata, don nasiha ga al’ummar musulmai. Misali, Ihsān al-Utaibī, a cikin littafinsa, Kitāb Tarbiyyatil Awlād fil Islām fi Mīzānin Naqdil Ilmī, ya bayyana kura-kuran Abdullah Nāsih
Ulwān a vangarorin tauhidi da aqida, da manhajin Ahlus-Sunnah, da
tsarin da’awa, da mu’amala da `yan bidi’a, da amfani da hadisai masu rauni. Yana daga abin mamaki da ke cikin littafin Tarbiyyatul Awlād,
yawaita yabon waxanda suka shahara da mummunar aqida, da
kwarzanta malaman bidi’a, da kwaxaitar da mutane karanta littafan da
ke cike da kwamacala da ruxani da tsugarara, da kuzuzuta xariqun
sufaye, da rubuta karamomin bogi, da kuma kafa hujja da hadisan qarya ko masu tsananin rauni. Abin bai tsaya nan ba, Abdullah Nāsih
Ulwān, ya yawaita suka da zargi ga Ahlus-Sunnah, `yan Salafiyyah,
waxanda ke bin Alqur’ani da Sunnar Manzon Allah (tsira da aminci su
tabbata a gare shi) bisa fahimtar magabata na qwarai. Ban da wannan, a fakaice, Ulwān, ya yi qoqarin shayar da masu karanta littafin
Tarbiyyatul Awlād gurvatacciyar aqidarsa da karkataccen manhajinsa
da kuma nazariyyarsa mai rauni.
Ya kamata xaliban ilmi su fahimci matsalolin da ke cikin wannan
littafi, don su san irin mu’amalar da za su yi da shi. Haka kuma, kafin a
karantar da littafin a masallaci ko wuraren xaukar karatu, ya kamata a
yi wa mutane bayani game da kura-kuran da ke cikin littafin da kuma
hanyar da mawallafinsa ya bi wajen rubuta shi. Qin bayyana wa xalibai
varnar da ke cikin littafin, musamman wadda ke da alaqa da aqida da
manhaj, dai dai ya ke da ha’intarsu ko kuma cin amanarsu a cikin
harkar ilmi. Allah Ya shiryar da mu.
24
Tsarin tarbiyya a Musulunci, gamammen tsari ne da ya kula
da kowane vangare na addini da rayuwa, ta yadda za a
samar da mutum mai zurfin fahimtar addini, da cikakken
hankali, da qoshin lafiya, da kyakkyawar xabi’a, da
wayewa, da dogaro da kai, da kishin al’umma, da sanin
haqqin kowa. Tarbiyyar `ya`ya na da vangarori guda
bakwai: vangaren imani, da xabi’u, da kula da jiki, da
hankali, da tunani, da mu’amala da zamantakewa, da kiyaye
bambancin jinsi.
A vangaren imani, wajibi ne a tarbiyyantar da `ya`ya a kan
aqida sahihiya, da ilmantar da su hukunce-hukuncen halal
da haram, da koya masu bautar Allah (Maxaukaki), da nuna
masu girman Allah da matsayi da martabar Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da cusa masu
son Allah (Mai girma da xaukaka) da son Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da sanar da su
haqqoqin Allah (Mai girma da xaukaka) da haqqoqin
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi),
da saba masu karatun Alqur’ani da qoqarin hardace shi.
A vangaren xabi’u da halaye, iyaye na buqatar xora `ya`yansu a kan makārimul akhlaq, wato, kyawawan xabi’u,
ta yadda za su taso a kan xabi’u na qwarai da halaye
managarta; da bayyana masu haxarin munanan xabi’u,
waxanda yara ke saurin xauka a wajen wasa tare da
sa’o’insu, kamar qarya da sata da zage-zage da cuxanya a
tsakanin maza da mata. Wannan zai samu ne idan iyaye suka
ba da kulawa ta musamman ga irin wasan da `ya`yansu ke
yi, da waxanda `ya`yansu ke yin wasa da su, da irin
maganganun da su ke yi a wajen wasa, da lokacin fitarsu da
kuma lokacin dawowarsu.
A vangaren tarbiyyar gangar jiki, `ya`ya na buqatar kulawa
ta musamman game da abincinsu da lafiyarsu, da koya masu
25
tsafta da tsarki, da nisantar da su daga dukkan abubuwa
masu cutarwa, da hana su yin wasa da abin da zai haifar
masu da matsala, da tarbiyyantar da su a kan lura da jikinsu
da tufafinsu. Haka kuma, a wannan vangare, akwai buqatar
iyaye su sanya ido a kan `ya`yansu domin tabbatar da cewa
ba su auka cikin munanan xabi’un da yara ke koyo daga
abokai/qawaye, musamman, a lokacin da suka fara girma.
Irin waxannan munanan xabi’un sun haxa da: shan taba
sigari; da qoqarin fitar da maniyyi a asirce, ta hanyar wasa
da al’aura ko kallon finafinan batsa ko aikawa da hotunan
tsiraici ta hanyar wayar tafi da gidanka; da shan abubuwan
da ke sanya maye; da zina; da luwaxi. A wannan vangare,
wajibi ne iyaye su mayar da himma wajen ganin `ya`yansu
sun taso a cikin qoshin lafiya.
Tarbiyyar `ya`ya a vangaren hankali, ta qunshi karantar da
su ilmin addini da rayuwa, da ba su nagartaccen ilmi, da
ladabtar da su a kan ayyuka da xabi’u masu kyau, da
faxakar da su al’amuran rayuwa, da saitin tunaninsu, da
tabbatar da lafiyar qwaqwalwarsu, da horar da su a kan
sana’a.
A vangaren tunani, tarbiyyar `ya`ya ta qunshi koyar da su
xabi’ar jarumta da sadaukantaka; da jin girma da martabar
addini a cikin zukatansu; da qimanta wayewa da ci gaban
Musulunci; da nisantar da su daga xabi’ar sangarci da
ragwantaka, da tsoro ko firgici mara dalili, da jin kasawa da
naqasu da kuma tawayar zuciya.
A vangaren zamantakewa da mu’amala da jama’a, `ya`ya na
buqatar tarbiyya a kan kyakkyawar mu’amala da halin
girma da karamci, da muhimmancin taqawa, da
`yan’uwantaka, da tausayi, da jin qai, da rangwame, da
yafewa, da jarumta; da sanar da su haqqoqin iyaye da
`ya`ya, miji da mata, `yan’uwa da dangi, maqwabta,
26
shugabanni da waxanda a ke shugabanta, dukkan musulmi
da waxanda ba musulmi ba, da haqqoqin dabbobi da
tsuntsaye da sauran halittar Allah (Maxaukaki); da
tarbiyyantar da su a kan ladubban Musulunci, kamar
ladubban cin abinci, da yin sallama, da neman izni kafin a
shiga gida, da ladubban zaman majalisi, da magana, da taya
murna ko yin jaje, da ladubban gaishe da mara lafiya.
A vangaren bambancin jinsi, wajibin iyaye ne su
tarbiyyantar da `ya`yansu a kan sanin bambancin da ke
tsakanin namiji da mace, da abubuwan da suka yi tarayya,
da irin mu’amalar da mace za ta iya yi da namiji, da
abubuwan da ba za su yi ba a tsakaninsu. Haka kuma, a
wannan vangare, `ya`ya na da buqatar sanin hukunce-
hukuncen kallon muharramai, da wadda a ke nemanta da
aure, da hukunce-hukuncen kallo a tsakanin ma’aura, da
hukuncin kallo a tsakanin namiji da matar da ya halatta ya
aura (ajanabiyyah) ko a tsakanin namiji da namiji, ko mace
da mace, ko kafiri da musulma. Bayan wannan, vangaren
tarbiyyar jinsi na wajabta karantar da `ya`ya hukunce-
hukuncen balaga, da alamomin balaga, da yadda matasa za
su yi mu’amala da tashen balaga.
WURAREN DA A KE SAMUN TARBIYYA
Tarbiyya na da wuraren da a ke samunta. Malaman tarbiyya
sun ce an fi samun tarbiyya a wurare uku: (1) gida (2)
makaranta (3) masallaci. Ko da ya ke ana iya samun
tarbiyya a waxansu wuraren daban, wuraren nan guda uku
sun fi tasiri a kan tarbiyya, kuma sun fi ba da gagarumar
gudummuwa wajen tabbatar da tarbiyyar `ya`yan Musulmi.
27
Gida
Gida ya qunshi wurin da aka haifi mutum kuma ya taso a
cikinsa har zuwa wani lokaci a rayuwarsa, ko da ba a gina
ba, da kuma sauran wuraren da ke maqwabtaka da gidan
iyaye. Musulunci yana xaukar gida a matsayin ginshiqin
farko a rayuwar kowace al’umma; kasancewar nan ne
cibiyar koyar da tarbiyya mafi girma, kuma nan ne wuri
mafi tasiri a cikin rayuwar kowane mutum.
Ana xaukar shekarun da yaro ke yi a cikin gidansu tun a
farkon rayuwarsa kafin ya fara mu’amala da sauran jama’ar
gari ko a tura shi makaranta, a matsayin shekaru mafi tasiri a
kan shi wajen tsara makomarsa, da kuma irin rawar da zai
taka a cikin al’umma. A waxannan shekaru, yaro na tare da
iyayensa, musamman mahaifiya, da sauran `yan’uwansa, a
mafi yawan lokaci, kuma yana dogaro da su wajen koyon
addini da xabi’u da al’adun da al’ummarsa ta ginu a kai.
Iyaye su ne mafi kusanci ga `ya`yansu, kuma su ne mafi
tasiri a cikin zukatansu. Tasirin iyaye a kan `ya`yan ya kan
ba su damar su canza su zuwa ga wani addini daban, savanin
tsarin da Allah (Mai girma da xaukaka) Ya halicce su a
kanta, kamar yadda Hadisi Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya tabbatar.55
A cikin gida ne yaro ke fara koyon mafi yawan abubuwan
da suka shafi rayuwarsa da sauran abubuwan da ke da tasiri
ga makomarsa. A bisa qiyasi, yara na yin kusan kashi biyu bisa uku (⅔) na rayuwarsu a tsakanin gidan iyayensu da
gidajen `yan’uwa da maqwabta, tun daga lokacin
haihuwarsu har zuwa shekara goma. Wannan yasa malaman
tarbiyya ke xaukar gida a matsayin wurin da ke hukunta irin
rawar da yaro zai taka, da gudummuwar da zai ba
55
Muslim
28
al’ummarsa nan gaba. Haka kuma, suna xaukar gida a
matsayin ginshiqin dukkan tarbiyya, kasancewar, makaranta
da masallaci da sauran wuraren da a ke samun tarbiyya, na
qarasa abin da aka gina ne a gida.
Samun tarbiyya daga gida na dogara ne a kan asasin da aka
gina gida a kansa. Idan iyaye sun kula da haqqoqin
`ya`yansu, kuma suka tsayu wajen yin masu tarbiyya a
dukkan vangarorin da suka dace, `ya`yan za su taso cikin
tarbiyya ta qwarai. Uwa tana da matsayi mafi girma a
wannan fage. Shi yasa malaman tarbiyya ke cewa lallai ne a
samu uwa ta gari ga `ya`yan da za a haifa, kuma a yi tattalin
uwar domin ta iya xaukar wannan babban nauyi.
Makaranta
Makaranta ce wuri na biyu da a ke samun tarbiyya domin
gina al’ummar Musulmai mai qarfi da kishin zuci da sanin
ya kamata. Yara na daxewa a makaranta irin daxewar da ba
su yi a wani wuri in ban da gidajensu. A kusan kowace rana,
in ban da lokacin hutu, `ya`yan da ke zuwa makarantar
islamiyya da boko, suna yin awa shida ko fiye da haka a
makaranta.
Kasancewar nan ne yara ke zuwa domin koyon ilmi da
sauraren karatu daga malamai dabam daban, da gogayya da
`yan’uwansu xalibai waxanda suka fito daga wurare
mabambanta, makaranta tana da tasiri mai yawa a kan
aqidar yara da xabi’unsu da mu’amalarsu da tunaninsu da
wayewarsu. Idan iyaye suka zava wa `ya`yansu makaranta
ta qwarai, inda a ke koyar da ilmi da tarbiyya a haxe, za su
taso cikin kyakkyawar tarbiyyar da za ta qarfafi qoqarin da
iyaye ke yi a gida. Idan kuwa suka yi sakaci game da zaven
makarantar da ta dace, hakan zai haifar da mummunar tasiri
ga tarbiyyar `ya`yansu.
29
Gudummuwar makaranta wajen tarbiyyar `ya`ya na da
fuskoki guda uku:
1. Gina al’umma a bisa tsarin daidaito da rashin fifiko a
cikin rayuwa, ta yadda za a daidaita matsayin xalibai, ba
tare da fifiko a tsakaninsu ba, sai ta hanyar ilmi ko
kyawun xabi’a. Hakan na taimakawa wajen zaburar da
yara a kan mayar da himma cikin karatu, da dagewa
wajen ganin sun zarce sa’o’insu ko abokan karatunsu,
tun da za su fahimci cewa nasabarsu ko matsayin
iyayensu ba su iya taimaka masu wajen samun ilmi ko
matsayin da ba su cancanta ba, a fagen ilmi.
2. Karantar da ilmi sahihi da gina kyawawan xabi’u ga
xalibai, matuqar an samu malamai amintattu kuma
qwararru, masu tsoron Allah, waxanda ke lazimtar
Shari’ar Allah (Maxaukaki) a cikin karantarwarsu, kuma
aka dace da abokan karatu na qwarai.
3. Tattalin yara a kan kyakkyawar wakilcin da za su yi wa
al’umma a kowane vangare na rayuwa bisa la’akari da
qoqari da qwazonsu, da fahimtarsu da qwarewarsu, da
jinsinsu da shekarunsu; da fahimtar da su qalubalen da
ke fuskantar al’ummarsu, da irin gudummuwar da za su
ba da wajen tunkararsa; da nusar da su zuwa ga wajibcin
da ke kansu na zama matasa masu tarbiyya, da iyaye
masu kulawa, da shugabanni masu adalci, da ma’aikata
qwararru, da dattijai masu kamun kai da tausayi idan sun
girma.
Tarbiyya ba ta samuwa daga makaranta yadda ya kamata har
sai idan iyaye sun nuna wa `ya`yansu muhimmancin ilmi da
qimar malaman da ke karantar da su, tare da bin diddigin
karatun da su ke koyo domin sanin halin da a ke ciki. Haka
30
nan, kasancewar makaranta na tattara xalibai da malamai
waxanda suka fito daga wurare mabambanta, wajibi ne
iyaye su sanya ido a kan karatun `ya`yansu; su yi qoqarin
sanin malaman da ke koyar da `ya`yansu, da abokan
`ya`yansu a makaranta, don gudun kada a rusa tarbiyyar da
su ke ba su a gida.
Masallaci
Masallaci56
na daga cikin manya-manyan wuraren da a ke
samun tarbiyya, kasancewar shi ne matattarar Musulmi a
zamanin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) da sahabbansa (Allah Ya yarda da su) da sauran
halifofi da sarakunan da suka biyo bayansu. A wancan
lokaci, a cikin masallaci ne a ke shawarwari game da
al’amuran siyasar al’umma, da tsarin gudanarwarsu da
tattalin arziqi, da tsaro, da jihadi, da sauran al’amuran yau
da kullum, xoriya a kan gyara aqida, da tsarkake rai, da yin
salla da zikiri da wa’azi da karantarwar da a ke gudanarwa a
cikinsa. Masallaci na ci gaba da ba da gagarumar
gudummuwa wajen tabbatar da tarbiyyar al’ummar
Musulmi har yanzu. Daga cikin ayyukan tarbiyya da a ke
gudanarwa a cikin masallaci, akwai:
56
Masallaci na da matsayi mai girma da falala mai yawa a Musulunci:
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ambaci masallaci a wurare goma sha
takwas a cikin Alqur’ani. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya danganta
wa KanSa masallaci, dangantawar da ke nuna xaukaka da girman
masallaci a wajenSa [Baqarah, 2:114; Taubah, 9:18; Jinn, 72:18;
Muslim]; masallaci shi ne mafi soyuwar wurare ga Allah [Muslim]; son
masallaci da lazimtarsa na wajabta wa bawa shiga cikin inuwar Allah a
ranar da babu wata inuwa sai ta Shi [Bukhari da Muslim]; gwargwadon
tafiyar da aka yi zuwa masallaci a nan duniya, gwargwadon masaukin
da za a tanadar wa mutum a cikin aljanna [Bukhari da Muslm]; kuma
yin tattaki zuwa masallaci na kankare kurakurai kuma yana xaukaka
darajoji [Muslim].
31
1. Sallar farilla cikin jam’i, da karatun Alqur’ani da
nau’o’in zikirin Allah (Maxaukaki).
2. Huxubobin Juma’a, waxanda a ke gabatarwa domin cin
ma manufar wa’azi da tunatarwa game da Allah (Mai
girma da xaukaka) da ranar lahira, da matakan gyaran
zukata, da kiran mutane zuwa ga alhairi, da umurni da
kyakkyawa da hani da mummuna; da ilmantar da
Musulmi game da haqiqanin addininsu da kyawawan
xabi’u a bisa karantarwar Alqur’ani da sahihiyar Sunnar
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi), kamar yadda magabata na qwarai suka fahimta; da
daidaita fahimtar mutane game da Musulunci, da mayar
da martani game da ruxanin da mavarnata ke kawowa;
da faxakar da al’umma game da abubuwan da ke faruwa
a yau da kullum, da yadda za a tunkare su; da faxakar da
mutane game da wata munasaba ko wani lokaci na
musamman, kamar azumin Ramadan da aikin Hajji; da
tabbatar da ma’anar `yan’uwantakar Musulunci a
tsakanin Musulmi; da rayar da ruhin jihadi a cikin
zukatan al’umma.57
57
Wannan na qara nuna muhimmancin gabatar da huxubar juma’a ko īdi cikin harshen da mafi yawan mutane ke fahimta. Babu yadda za a yi
jama’a su amfana daga huxubar da ba su fahimta, kasancewar an
gabatar da ita cikin harshen larabci. Ko da ya ke akwai savani a
tsakanin malamai dangane da halaccin yin huxuba cikin wani harshe
savanin larabci, magana mafi qarfi da dacewa da manufofin Shari’ar
Musulunci dangane da huxubobi, ita ce, babu wani sahihin dalilin da ya
hana a yi huxuba cikin harshen da mutane za su fahimta, tun daga farkonta har zuwa qarshe, kuma ba dole ne a yi huxubar juma’a ko īdi
cikin larabci ba. Wannan ita ce fatawar mafi yawan malamai da
kwamitotin fatawa a wannan zamani. Sun kafa hujja da faxin Allah
(Maxaukaki): ‚Ba mu aiko wani Manzo ba face (yana magana) da harshen mutanensa domin ya yi masu bayani.‛ [Ibrāhīm, 14:4]. Haka
kuma, sun dogara da umurnin da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ba Zaid ibn Thābit (Allah Ya yarda da shi) ya
koyi harshen yahudu domin a kyautata mu’amala tare da su [Ahmad];
32
3. Ayyukan da’awah, da faxakarwa da shiryarwa ga matasa
da dattawa, maza da mata.
4. Wa’azi da darussa dabam daban da muhadarori don
kyautata saqafar Musulmi da wayewarsu.
5. Taron tattaunawa a kan al’amuran da suka shafi
Musulmi, da taron qara wa juna ilmi ko taron bita.
6. Tsare-tsaren da ke taimakawa wajen tabbatar da
tarbiyyar `ya`yan Musulmi, kamar halqar karatun
Alqur’ani; da kwamitotin da ke taimaka wa Musulmi
gudanar da waxansu nau’o’in ibada yadda ya dace,
kamar kwamitin karva da rarraba Zakka, da kwamitin
sulhu, da kwamitin taimaka wa gajiyayyu, da kwamitin
taimaka wa matasan Musulmi wajen fannonin ilmi ko
samar da tallafin karatu ko sana’a ko aikin albashi.
7. Laburaren da zai qunshi littafai da na’urorin yaxa
da’awah irin na zamani.
Babu shakka, waxannan abubuwa da a ke gudanarwa a
masallaci na da tasiri mai yawa a kan tarbiyyar Musulmi a
vangaren aqida da gyaran zuciya, da ilmi da kyawawan
da kuma umurnin da ya ba sahabbai (Allah Ya yarda da su) cewa idan
sun tafi yaqi, kada su auka wa abokan gaba har sai sun kira su zuwa ga
addinin Allah [Bukhari da Muslim]. Malamai suka ce waxannan dalilai
na tabbatar da halaccin amfani da harshen da mutane ke fahimta domin isar da saqo gare su a cikin huxubar juma’a ko īdi. Amma Shaikh Ibn
Bāz na ganin zai fi kyau liman ya karanto ayoyin Alqur’ani da nassosin
hadisi cikin harshen larabci, ko da ya gabatar da huxubar cikin wani harshen daban [Duba littafin Taudīhul Ahkām, 3/581, da Fatāwā Islāmiyyah, 1/405-406; da The Friday Prayer na Jamāluddīn Zarābozo
domin qarin bayani].
33
xabi’u da mu’amala ta qwarai. Wannan yasa, Ibn Taimiyyah
(Allah Ya jiqan shi) ya ce:
[Masallatai sun kasance matattarar al’umma, kuma wuraren
zaman shugabanni. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya assasa masallacinsa mai albarka a kan
taqawa, kuma ya kasance a cikinsa a ke salla, da karatun
Alqur’ani, da zikiri, da karantar da ilmi, da huxubobi. Kuma
a cikinsa a ke gudanar da tsarin shugabanci, da shirye-
shiryen yaqi, da zaven shugabanni, da bayar da sanarwa.
Haka kuma, a cikinsa Musulmi ke taruwa duk lokacin da
wani al’amarin da ya shafi addininsu da duniyarsu ya bijiro].
Wajibi ne iyaye su xauki matakan da suka dace domin ganin
sun alaqanta `ya`yansu da masallaci, kuma sun qaunatar
masu da zuwa masallaci a kan lokaci, da qoqarin zama a
cikinsa, da sauraron darussan da a ke gudanarwa, da yin
tarayya da sauran mutane a cikin ayyukan tsaftace masallaci,
da ba da gudummuwa domin havaka tsare-tsarensa. Daga
cikin hanyoyin da iyaye za su bi wajen cusa wa `ya`yansu
son masallaci, da fahimtar da su gagarumar gudummuwarsa
wajen tabbatar da tarbiyya, akwai:
1. Fahimtar da su girman masallaci da muhimmancinsa a
rayuwar Musulmi ta hanyar xora su a kan saurare da
kwaikwayon mai kiran salla duk lokacin da aka yi kira.
2. Zuwa masallaci tare da su da zarar sun xan yi wayo, da
shiryar da su cikin sauqi da tausasawa idan suka yi wasa
ko surutu a masallaci, maimakon a yi masu tsawa ko a
buge su ko a daina zuwa da su gaba xaya.
34
3. Limamin masallaci da sauran masallata su yi
kyakkyawar mu’amala da yaran da ke zuwa masallaci, ta
hanyar jawo su a jika; da yin masu sallama; da yin
musafaha da su; da yabonsu a kan qoqarin zuwa
masallaci; da ba su kyauta wani lokaci; da kau da kai ga
kurakuran da ba su yi tsanani ba; da sakar masu fuska; da
yin masu murmushi; da tambayar labarinsu idan sun
kwana biyu ba su zo masallaci ba; da rashin kora su can
bayan sahu, matuqar sun zo masallaci da wuri.58
4. Saba masu da halartar halqar Alqur’ani da yin
musharaka cikin karatun Alqur’ani da sauran darussan
da a ke gudanar da su a keve.
5. Halartar darussa da muhadarorin da a ke gabatarwa a
masallaci tare da su.
HANYOYIN KOYAR DA TARBIYYA59
Amfani da hanyar da ta dace ko usulubin da ya fi cancanta
wajen tarbiyyantar da `ya`ya wajibi ne. Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) shi ne shugaban
masu tarbiyya kuma wanda ya fi kowa iya karantar da
tarbiyya, ta hanyar magana da aiki, da nuni da ishara, da
sauran hanyoyi da usulubai mafi dacewa. Bin diddigin
Sunnarsa na nuna cewa Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya yi amfani da hanyoyi guda
58
Yana daga kura-kuran da a ke yi a waxansu masallatai, tura yara can
baya, da kuma hana su shiga cikin sahu, ko da sahun farko ko sahu na
biyun bai cika ba, a lokacin da za a fara salla. 59
Mafi yawan bayanan da ke qarqashin wannan sashe na ciro ne daga littafin Muhammad Ad-Duwaysh, Al-Asālibut Tarbawiyyah inda Rasūlil Bashariyyah, www.quran.maktūb.com/vb/quran22761
35
goma wajen tarbiyyantar da al’ummarsa, irin tarbiyyar da
duniya ba ta tava gani ba, kafin wancan lokaci da kuma
bayansa. Hanyoyin su ne:
1. Amfani da qissa, kasancewar mutane na son qissa, kuma
suna jawuwa zuwa gare ta, kamar yadda su ke saurin
koyon darasi da xaukar wa’azi daga gare ta. Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi amfani da irin wannan usulubi a lokacin da Khabbāb ibn
Al-Arat (Allah Ya yarda da shi) ya koka game da tsanani
da wahalar da su ke sha a hannun kafiran makka.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ba shi labarin waxansu mutane da suka rayu kafin
wannan lokaci; sun fuskanci nau’o’in azaba da kuma
kisar gilla, amma hakan bai sa sun bar addinin Allah
(Mai tsarki da xaukaka) ba.60
Bayan wannan, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi amfani da usulubin qissa a
wurare da dama domin isar da saqo na musamman.
Misali, ya ba da qissar mutane uku waxanda suka shiga
kogo, sai dutse ya toshe ramin kogon, har sai da suka
roqi Allah, ta hanyar yin tawassuli da kyawawan
ayyukansu, domin ya tarbiyyantar da al’ummarsa a kan
ikhlasi (yin kowane abu domin Allah);61
da qissar
mutumin da ya kashe mutane xari, sannan ya tuba, kuma
Allah Ya karvi tubarsa, domin ya nuna muhimmancin
tuba;62
da qissar makaho da kuturu da mai qwaiqwaido,
waxanda Allah Ya yi wa ni’ima bayan jarabawa, amma
biyu daga cikinsu suka butulce wa Allah, domin ya nuna
haxarin butulci ga Allah (Maxaukaki), da kuma amfanin
60
Bukhari 61
Bukhari da Muslim 62
Bukhari da Muslim
36
gode wa Allah (Maxaukaki) a kan ni’imominSa;63
da qissar as-hābul ukhdūd, waxanda sarkinsu ya tirsasa su
shiga cikin wuta saboda sun yi imani da Allah
(Maxaukaki), domin ya karantar da muhimmancin
haquri a kan cutarwar da mumini zai fuskanta a dalilin
riqo da addini.64
2. Amfani da hanyar wa’azi, saboda tasirin wa’azi a cikin
zukata, tare da lura da yanayin mutane da kuma
buqatarsu ga irin wannan usulubi, ta yadda ba za a gundurar ko a gajiyar da su ba.
65 Al-Irbād ibn Sāriyah
(Allah Ya yarda da shi) ya ba da labarin wani wa’azin da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya yi a kan wajibcin biyayya ga shugaba da kuma
riqo da Sunnah, har idanuwa suka zubar da hawaye,
kuma zukata suka raurawa, kamar dai wa’azin mai ban
kwana da mutanensa.66
3. Usulubin kwaxaitarwa da tsoratarwa, bisa la’akari da
xabi’ar xan Adam ta fuskantowa da juyawa, da kuma
karsashi da gajiyawa, a lokaci zuwa lokaci. Misali,
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya yi amfani da hanyar tsoratarwa, a lokacin da ya
ce: ‚Da kun san abin da na sani, da kun yi dariya kaxan,
kuma kun yi kuka mai yawa‛;67
kuma ya yi amfani da
hanyar kwaxaitarwa, a cikin hadisin da ya ce: ‚Ba wani bawa da zai ce ‘Lā ilaha illallāh, sannan ya mutu a kan
haka, face ya shiga aljanna.‛ Abu Zarr (Allah Ya yarda
da shi) ya ce, ‘ko ya yi zina, ya yi sata’? Manzon Allah
63
Bukhari da Muslim 64
Muslim 65
Bukhari 66
Tirmidhi da Ibn Mājah 67
Bukhari da Muslim
37
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚ko
ya yi zina, ya yi sata‛.68
4. Usulubin gamsar da tunani da hankalin mai saurare, ta
yadda mutum zai sallama wa abin da aka gamsar da shi a kai. Abu Umāmah (Allah Ya yarda da shi) ya ruwaito
cewa wani saurayi ya je wajen Annabi (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce, ‘Ka ba ni iznin yin
zina’, sai mutane suka daka ma shi tsawa, suka ce ‘mah, mah’69
. Sai Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce ya matso kusa da shi, sannan ya
ce masa: ‚Za ka so a yi zina da mahaifiyarka?‛ Ya ce,
‘wallahi, a’a’. Ya ce: ‚Haka nan sauran mutane ba za su
so a yi zina da uwayensu ba.‛ Ya ce: ‚Za ka so a yi da
`yarka?‛ Ya ce, ‘wallahi, a’a’. Ya ce: ‚Haka nan ma
sauran mutane ba su son a yi da `ya`yansu‛. Ya ce: ‚Za
ka so wa `yar’uwarka?‛ Ya ce, ‘wallahi a’a’. Ya ce:
‚Haka nan, mutane ba za su so wa `yan’uwansu ba‛. Ya
ce: ‚Za ka so a yi da guggonka?‛ Ya ce, ‘wallahi, a’a’.
Ya ce: ‚Mutane ma ba za su so haka ga guggonninsu
ba.‛ Ya ce: ‚Za ka so a yi da innarka?‛ Ya ce, ‘wallahi,
a’a.’ Ya ce: ‚Haka nan ma sauran mutane ba za su so a yi zina da innoninsu ba…‛
70 Abu Umāmah (Allah Ya
yarda da shi) ya ba da labarin cewa a qarshen al’amari,
wannan saurayi ya nemi a yi masa addu’ar Allah
(Maxaukaki) Ya nisanta shi daga zina, kasancewar ya
gamsu da muninta, kuma ya fahimci illarta.
5. Amfani da hanyar tattaunawa da munaqasha, domin a
faxakar da mutane game da abin da ba su fahimta ba, ko
a shiryar da su zuwa ga abin da ya fi dacewa, kamar
68
Bukhari da Muslim 69
Kalma ce ta tsawatarwa da nuna tir ga wanda ya faxi wani
mummunan abu. 70
Ahmad
38
yadda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi tare da mutanen madina, Al-Ansār, a
lokacin da suka nuna rashin jin daxinsu, saboda ya raba
ganimar da aka samu a yaqin Hunain, ba tare da ya ba su
komai ba. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi huxuba, kuma ya ce: ‚Ya ku
mutanen madina! Ashe ban same ku a kan vata ba,
amma Allah Ya shiryar da ku ta hanyata? Na same ku a
rarrabe, amma Allah Ya haxa ku wuri xaya ta hanyata?
Kuma na same ku cikin talauci, amma Allah Ya azurta
ku ta hanyata?...71
6. Hanyar zafafawa da yin uquba ko bayyana zargi ga
wanda ya yi abin da bai dace ba, matuqar yin hakan zai
fi kawo gyara. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya bayyana vacin rai, kuma ya zafafa
matuqar gaske, a lokacin da aka kawo qarar wani
sahabin da ke tsawaita wa mutanensa a cikin salla.72
Haka kuma, a lokacin da wani mutum ya yi tambaya
game da hukuncin tsintar raqumin da ya vace, Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Ina ruwanka da shi…!‛73
Bayan wannan, Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya fisge
zinaren da ya gani a hannun wani, sannan ya ce:
‚Xayanku kan yi gangancin xaukar garwashin wuta, ya
sanya a hannunsa‛,74
kuma ya yi mummunar addu’a ga
mutumin da girman kai ya hana shi cin abinci da
hannunsa na dama.75
71
Bukhari da Muslim 72
Bukhari da Muslim 73
Bukhari da Muslim 74
Muslim 75
Muslim
39
7. Qaurace wa wanda ya yi laifi, har sai ya tuba, kamar
yadda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi wa su Ka’ab ibn Mālik (Allah Ya yarda
da shi), a lokacin da ba su fita yaqin Tabuk tare da
Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ba.76
Sai dai kuma ba a kowane lokaci ba ne Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ke
amfani da wannan hanyar.
8. Amfani da usulubin da zai haxa kowa da kowa, ba tare
da an ayyana waxanda a ke nufi ba, illa iyaka, da zarar
mutanen da abin ya shafa suka ji, za su fahimci saqon;
ko kuma a faxi magana game da wani mutum a bayan
idonsa, don a sanar da shi daga baya. Misali, dangane da waxanda suka xora wa Barīrah (Allah Ya yarda da ita)
biyan kuxin fansa, bisa sharaxin cewa su ne ke da
walittarta, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce: ‚Mene ne ya sa mutane ke
sanya sharuxxan da ba su a cikin littafin Allah …‛77
Haka kuma, a lokacin da waxansu mutane uku suka
shiga gidansa domin sanin irin yadda ya ke ibada a cikin
gida, sannan, xayansu ya ce ba zai yi aure ba, na biyu ya
ce ba zai sake yin barcin dare ba, na ukun ya ce kullum
zai riqa yin azumi, Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Mene ne ya samu mutane,
suka ce kaza da kaza …‛78
Wani lokaci, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) na faxin magana domin a sanar da
wanda abin ya shafa. Misali, Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce wa matarsa
Hafsah bint Umar (Allah Ya yarda da ita): ‚Madalla da 76
Bukhari 77
Bukhari da Muslim 78
Bukhari
40
Abdullah (ibn Umar), ina ma da yana yin sallar dare.‛79
A wani lokacin, yana faxin magana a cikin mutane
domin wanda a ke yi da shi ya fahimci saqon. Misali,
waxansu mutane guda biyu sun yi kace-nace a gaban
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi). Sai, a cikin fushi, xaya daga cikinsu ya zagi xayan. Sai Manzon Allāh (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Na san kalmar da zai faxi, wannan fushin ya gushe. Da zai ce, ‘A’ūzu billah minash-shaixānir rajīm’, shi ke nan‛. Sai aka ce wa mutumin,
‘ka ji abin da Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce kuwa? Sai mutumin ya ce, ‘(na ji mana)
ai ni ba mahaukaci ba ne!80
9. Amfani da wata dama ko fursa, saboda la’akari da
munasabar lokacin ko yanayin ko kuma wurin. Irin
wannan hanya ta qunshi yin wa’azi a maqabarta; da yin
jim-kaxan bayan wani tashin hankali ya auku; da amfani
da lokacin farin ciki; da lokacin musiba; da lokacin
rashin lafiya; da lokacin mutuwa ; da lokacin aukuwar
wata aya, kamar girgizar qasa ko kisfewar rana; da
lokacin da wani abin tausayi ko abin jimami ya faru.
Abin da aka faxa wa mutane a irin wannan lokaci ya kan
yi tasiri sosai a zukatansu.
10. Usulubin qarfafa gwiwa, da yin yabo saboda qoqarin da
aka yi. A lokacin da Abu Hurairah (Allah Ya yarda da
shi) ya tambayi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) game da wanda zai fi rabauta da
cetonsa a ranar qiyama, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Da ma na yi zaton
babu wanda zai riga ka yin wannan tambayar saboda
79
Bukhari 80
Bukhari da Muslim
41
kwaxayin da ka ke da shi game da ruwayar hadisi.‛81
Haka kuma, a lokacin da Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya yi wa Ubayyu ibn Ka’ab
(Allah Ya yarda da shi) tambaya game da ayar da ta fi girma a cikin littafin Allah, Ubayyu ya ce, Āyatul Kursiyy, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce masa: ‚Madalla da yawan ilminka, yā Abā Munzir.‛
82
Iyaye na buqatar bin hanyoyin da suka fi dacewa wajen
tarbiyyar `ya`yansu, bisa la’akari da yanayi, lokaci, wuri,
shekaru, da jinsi. Rashin la’akari da waxannan abubuwa zai
haifar wa iyaye rashin fahimtar irin matakin da ya kamata su
xauka, a duk lokacin da `ya`yansu suka yi abin da bai dace
ba.
Bayan wannan, wanda zai yi tarbiyyar `ya`ya, yana buqatar
mallakar siffofi guda tara domin ya kai ga yin nasara:83
1. Gwargwadon ilmin addini, da ilmin abubuwan da ke
faruwa yau da kullum don tsai da wajibin koyar da
tarbiyya.
2. Riqon amana a cikin ibada da mu’amala, da qoqarin kula
da addini, da lazimtar Shari’ah a voye da bayyane, ta
yadda zai zamanto abin koyi ga wanda ya ke yi wa
tarbiyya.
3. Qarfi da ikon yin jagoranci ga waxanda a ke koya wa
tarbiyya.
81
Bukhari 82
Ahmad da Muslim 83
Duba littafin Kaifa Turabbi Waladaka na Lailā bint Abdir-Rahmān
Al-Jarībah
42
4. Adalci a tsakanin waxanda za a yi wa tarbiyya, ba tare
da nuna bambanci ko fifiko ba, sai idan da larurar da za
ta halatta yin haka.
5. Kwaxayin shiryuwa da tarbiyyantuwar wanda a ke yi wa
tarbiyya, da zame masa jagora, kuma kyakkyawan abin
koyi, da yin masa addu’a, da bibiyar halin da ya ke ciki,
lokaci zuwa lokaci.
6. Himmar ganin an lazimta wa yaro abubuwan da za su
kiyaye masa addini da hankali da jiki da dukiya, da
nisantar da shi daga abubuwan da za su cutar da shi ta
kowane vangaren tarbiyya, bisa qa’idar ajiye kowane
abu a wurin da ya dace, ba tare da la’akari da jin daxin
yaron ko rashin jin daxinsa ba, a lokacin da a ke yin
masa tarbiyya.
7. Yi wa kai tarbiyya, da kuma qoqarin tabbatar da
kyakkyawar yanayi a wurin da za a gudanar da tarbiyya.
8. Amfani da hikima da kuma usulubin da ya dace wajen
yin tarbiyya.
9. Lazimtar gaskiya da kuma nisantar riya a cikin magana
da aiki.
HAXARIN SAKACI GAME DA TARBIYYAR `YA`YA84
`Ya`ya kyauta ce daga Allah (Mai tsarki da xaukaka),85
kuma ni’ima ce wadda ta dace da xabi’a, da yanayin xan
84
Mafi yawan bayanan da ke qarqashin wannan sashe na ciro su ne
daga littafi na Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci 85
Shūrah, 42: 49 – 50
43
Adam. Wannan yasa xan Adam ke jin daxi, kuma ya ke yin
farin ciki, idan aka haifar masa `ya`ya. Haka kuma, yana
roqon Allah Ya azurta shi da `ya`ya, idan bai samu haihuwa
ba.86
Haihuwa arziqi ne,87
kuma tana daga cikin fa’idodin aure.
Su kuma `ya`ya, ado ne88
da aka qawata wa mutane
sha’awarsa.89
Fatan kowane mutum shi ne ya samu `ya`ya
nagari, masu albarka, masu biyayya, masu tausayi; waxanda
za su tsaya a makwafinsa, su cike gurbinsa, kuma su ci gaba
daga wajen da ya tsaya, idan Allah Ya xauki ransa.90
Burin
kowane uba nagari, shi ne, Allah Ya sa `ya`yansa su wakilce
shi a ko’ina, su zamanto sanyin ido a gare shi, su tausaya
masa, kuma su xauki nauyinsa idan ya tsufa, sannan su yi
masa addu’a idan ya mutu.91
`Ya`ya amana ce babba a wuyan iyaye, kuma wasiyya ce
daga Allah (Mai tsarki da xaukaka).92
Babu shakka, za a
tambayi kowane uba da uwa game da wannan amana da
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ba su, kuma za a tambaye
su game da wannan wasiyya.93
Haka kuma, `ya`ya da dukiya jarabawa ce daga Allah. Babu
mai cin wannan jarabawa sai wanda ya tsayu da haqqoqin
da ke rataye da ita, kamar yadda Musulunci ya shar’anta.
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ce: ‚Kuma ku sani cewa
abin sani kawai, dukiyoyinku da `ya`yanku, wata fitina
86
Aal Imrān, 3:38 87
Nahl, 16:72 88
Kahf, 18:46 89
Aal Imrān, 3:14 90
Maryam, 19:5 – 6 91
Furqān, 25:74 92
Nisā, 4:11 93
Muslim
44
(jarabawa) ce, kuma lalle ne Allah, a wurinSa, akwai ijara
(lada) mai girma.‛94
Yin kyakkyawar tarbiyya ga `ya`ya na daga cikin manya-
manyan hanyoyin nuna godiya ga Allah a bisa ni’imar
haihuwa, da xaukar matakan cin wannan babbar jarabawa.
Kyakkyawar tarbiyya kuwa, tana samuwa ne ta hanyar
kiyaye qa’idodin Shari’a, da aiki da ladubbanta,
gwargwadon hali, a cikin dukkan abubuwan da za a yi wa
`ya`ya, tun kafin a haife su, da kuma bayan an haife su, har
su girma.
Abin mamaki, da yawa daga iyaye ba su damu da shiriyar
`ya`yansu ba, alhali kuwa muhimmin abu ne a cikin
tarbiyya. Saboda muhimmancinsa ne ma, Annabawa da
Manzanni suka riqa roqon Allah Ya ba su zuriya ta qwarai
tun kafin su samu haihuwa. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ba mu labarin addu’o’in da Annabi Ibrāhīm da Zakariyya
suka yi domin samun `ya`ya nagari. Haka kuma, waxansu
iyayen ba su damu da sanin halin da `ya`yansu ke ciki ba: ba
su tambayar ina suka je, ko ina za su, ko yaushe suka je, ko
yaushe suka dawo; su wane ne abokan hirarsu ko abokan
zuwa yawonsu; `ya`yansu na zuwa makaranta ko a’a, suna
mai da hankali a wajen karatu ko a’a, suna kula da addini ko
a’a; `ya`yansu na cikin qoshin lafiya da kuzari ko a’a; sun ci
abinci ko ba su ci ba; waxanne irin tufafi suka sanya; suna
yin wanka da sauran al’amuran tsafta ko ba su yi.
Irin wannan sakaci da mafi yawan iyaye suka samu kansu a
ciki, yana haifar da tavarvarewar tarbiyya, kamar yadda a ke
gani a yau; al’umma ta rasa qima da matsayin da aka santa
da su; rashin tausayi da biyayya sun zama ruwan dare; ci
94
Anfāl 8:28
45
baya da tawayar zuciya da rashin kishin kai sun dabaibaye
ta.
A vangaren iyaye, sakaci wajen tarbiyyar `ya`ya na haifar da
qiyayya a tsakanin su da `ya`yan. Haka kuma, `ya`yan da ba
su samu cikakkiyar tarbiyya ba, na zamantowa fitina ga
iyayensu, kuma su zamanto dalilin shagalar iyaye daga abin
da Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ke so. Da ma Allah
(Mai girma da xaukaka) Ya ce: ‚Ya ku waxanda suka yi
imani! Lalle ne daga matanku da `ya`yanku akwai maqiyi a
gare ku, sai ku yi hattara…‛95
Kuma Allah (Mai girma da
xaukaka) Ya ce: ‚Dukiyoyinku da `ya`yanku fitina ce
kawai. Kuma Allah, a wajenSa akwai wani sakamako mai
girma.‛96
Haka nan, Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ce:
‚Ya ku waxanda suka yi imani! Kada dukiyoyinku da
`ya`yanku su shagaltar da ku daga ambaton Allah. Kuma
wanda ya yi haka, to, waxannan su ne masu hasara.‛97
Babu
shakka, yin sakaci game da tarbiyyar `ya`ya na da haxari
mai girma.98
Ibnul Qayyim (Allah Ya jiqan shi) ya ce: ‚Wanda ya qi
karantar da xansa abin da zai amfane shi, ya bar shi haka
kawai, ya munana matuqa. Mafi yawan `ya`ya na lalacewa
ne saboda sakacin iyaye da rashin karantar da su farillai da
sunnoni na addini; ta haka, sai iyaye su tozartar da (`ya`yan)
su tun suna qanana, ta yadda `ya`yan ba za su amfanar da
kansu ba, kuma ba za su amfani iyayen ba idan sun
girma.‛99
95
Taghābūn, 64: 14 96
Taghābūn, 64:15 97
Munafiqūn, 63:9 98
Duba Tafsīrul Qur’anil Azīm na Ibn Kathīr, 4/344, da 4/47 don qarin
bayani 99
Duba littafin At-Taqsīr fi Tarbiyyatil Aulād: Al-Mazāhir, Subulul Wiqāyah wal Ilāj na Muhammad ibn Ibrahim Al-Hamd
46
Abu Hāmid Al-Ghazāli (Allah Ya jiqan shi) ya ce: ‚Xa,
amana ce a wajen iyayen shi, kuma zuciyarsa tsarkakakkiya
ce, wadda babu wani zane ko hoto a cikinta; zai dace da duk
irin zanen da aka yi masa, kuma yana shirye da ya karkata
ga duk inda aka juya shi. Idan aka xora shi a kan alhairi
kuma aka karantar da shi, zai girma a kan haka, kuma ya ji
daxin rayuwa a duniya da lahira, kuma iyayensa da
malamansa su yi tarayya da shi cikin lada. Idan kuwa aka
saba masa da sharri, kuma aka yi watsi da shi kamar dabba,
zai tave, ya halaka, kuma zunubin na kan waxanda nauyinsa
ke kansu.‛100
A cikin littafin At-Taqsīr fi Tarbiyyatil Aulād, Shaikh
Muhammad ibn Ibrahim Al-Hamd ya lissafa alamomin
sakaci game da tarbiyyar `ya`ya. Daga cikinsu akwai:
1. Tarbiyyantar da `ya`ya a kan tsoro da ragwantaka da
yawan fargaba, da lalaci da kasala da jin naqasu da
tawayar zuci, da zaman banza ko rashin amfani da lokaci
yadda ya kamata, da son na banza da rashin moriya.
2. Samar wa `ya`ya duk abin da su ke so, da sayo masu duk
abin da suka nema, ko da kuwa ba su da buqatar haka,
saboda qarancin shekarunsu ko yanayinsu.
3. Sayen masu mota tun suna qanana, ta yadda za su samu
damar yin sharholiya da bin `yan mata da abokan banza,
ko kuma su rasa natsuwar yin karatu.
4. Tsananta masu, da zafafawa a gare su fiye da qima, da
rashin tausasa masu.
100
Duba littafin At-Taqsīr fi Tarbiyyatil Aulād: Al-Mazāhir, Subulul Wiqāyah wal Ilāj na Muhammad ibn Ibrahim Al-Hamd
47
5. Tsananin rowa, da qanqame hannu, da tsuke bakin aljihu
wajen ciyar da su, ko xaukar nauyin karatunsu ko kuma
koyon sana’a.
6. Rashin tausasawa da tausayawa da nuna jin qai a gare su,
bisa la’akari da shekaru da yanayinsu, da kuma rashin
damuwa da halin da su ke ciki.
7. Mayar da himma ga al’amuran `ya`ya na zahiri ko kuma
ruxuwa da abin da su ke bayyanarwa a fili, ba tare da
qoqarin gyara zukatansu da kyautata al’amuransu na sirri
ba.
8. Wuce iyaka wajen kyautata zato ko munana zato ga
`ya`ya.
9. Nuna bambanci a tsakanin `ya`ya, a wajen kyauta ko
xaukar nauyin karatu, ba tare da wani sahihin dalilin
Shari’ah ba.
10. Kiransu da munanan suna ko sanya masu sunayen banza,
waxanda ba su da kyakkyawar ma’ana.101
11. Yin mummunar addu’a a kansu ko yawan la’antarsu, da
yin masu mummunar fata.
12. Doguwar hira a qofar gida ko majalisa ko dandali,
maimakon zama tare da iyali don sanin halin da su ke
ciki.
101
Karanta littafi na Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci don qarin bayani game da ladubban sanya suna, da
qa’idodin zaven suna.
48
13. Aikata munanan abubuwa a gabansu, ta yadda za su yi
koyi da ayyukan assha waxanda suka ga iyayensu na yi.
14. Kawo munanan abubuwa a gida, ko barin abubuwan da
ke vata tarbiyya a cikin gida.
15. Tilasta wa `ya`ya maza su auri matan da ba su so, ba tare
da la’akari da abin da zai iya biyo baya ba.
16. Jinkirta aurar da `ya`ya mata, waxanda mutanen kirki
suka zo don su aura, bisa hujjar sai sun kammala
makaranta.102
102
Sanannen abu ne cewa aure ba ya hana karatu, haka kuma, karatu ba
ya hana aure. Ya kamata iyaye su hanzarta aurar da `yarsu idan ta kai
munzalin aure, matuqar mutumin kirki, wanda aka yarda da addininsa
da xabi’unsa ya fito. Kuskure ne iyaye su dage a kan sai `yarsu ta
kammala karatu, musamman idan ta nuna cewa tana buqatar
auren.Wallahi da yawa daga cikin `yan matan jami’a, da waxanda ke
sakandare, waxanda iyayensu suka hana su yin aure bisa hujjar sai sun
kammala karatu, na yin zina tare da samarin da ke nemansu. Saboda
qarancin ilmin waxansu `yan matan, har cewa su ke yi ai duk zinar da
suka yi, zunubin na kan iyayensu, tun da an hana su aure, alhali suna da
tsananin buqata.Waxansu iyayen kuma, saboda sakarci, sun yarda a yi
ta zuwa wajen `ya`yansu mata, da sunan zance, amma da zarar wani
daga cikin samarin ya nemi a ba shi damar turo wakilansa domin a yi
maganar aure, sai iyayen su ce allanbaran ba za su aurar da `yarsu a
wannan tsakani ba, bisa hujjar cewa tana yin karatu! Tambayar ita ce:
me ya sa aka bar ta tana hira da maza, tun da an san ba za a aurar da ita a lokacin ba? Sau da yawa irin waxannan `yan mata su kan fuskanci
matsaloli masu yawa idan sun kammala karatu, kasancewar waxansu
mutane za su riqa qyamar su neme su da aure, ko dai saboda tsufa ko
kuma saboda zargin cewa sun yi ballagazanci a makaranta. Ya kamata
iyaye su ji tsoron Allah!
Waxansu iyayen na kafa hujja da cewa idan sun aurar da `ya`yansu,
alhali suna karatu ko kuma suna gab da fara karatun, sau da yawa
mazajen na hana su ci gaba. Ko da ya ke hakan yana faruwa a tsakanin
matasa, wannan ba zai zame wa iyaye hujjar qin aurar da `ya`yansu ba,
musamman idan `ya`yan sun nuna buqatar yin aure. Rashin yin haka,
49
17. Auren dole ga `yan mata.103
ya kan haifar wa iyaye da abin kunya, domin kuwa waxansu `yan
matan ba su iya haquri. Kafin a farga, sun yi cikin shege, ko kuma su
riqa amfani da qwayoyin hana xaukar ciki, ta yadda za su ci gaba da
holewarsu.
Babu shakka, auren wuri, ga wadda ta samu mutumin kirki, wanda
ke son ya aure ta, yana da fa’idodi masu yawa. Daga cikinsu: (1) samun
`ya`ya da wuri, ta yadda iyaye za su yi farin ciki a lokacin tsufarsu (2)
yawaita al’ummar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) (3) tsare matasa daga karkacewar tunani, da kare su daga
fitinar sha’awa (4) kiyaye mutuncin musulmi, da tsare al’umma daga
faxawa cikin yawan zinace-zinace (5) samar da aminci da tsaftataccen
yanayi ga al’umma (6) taqaita tazarar da ke tsakanin shekarun iyaye da
na `ya`yansu, domin samun damar yin kyakkyawar tarbiyya ga `ya`ya. 103
Malamai sun qara wa juna sani dangane da matsayin auren dole.
Waxansu malamai na ganin cewa za a iya tilasta wa budurwa ta auri
mutumin da ba ta so, ko da ta balaga, amma ba za a yi wa bazawara
tilasci ba, ko da ba ta balaga ba. Waxansu malamai suka ce za a iya
tilasta budurwa komai girmanta, haka nan ma, bazawarar da ba ta
balaga ba. Waxansu malamai kuma suka ce ba za a iya tilasta yarinya a
kan ta auri mutumin da ba ta so ba, ko da kuwa ba ta tava yin aure ba,
kuma ko da qarama ce, wadda ba ta balaga ba. Amma magana mafi
qarfi, wadda Ibn Taimiyyah da waxansu malamai suka qarfafa, ko da
ya ke ta sava wa mazhabar malikiyya, ita ce, ba a yi wa mace auren
dole matuqar ta balaga, ko da kuwa ba ta tava yin aure ba. Dangane da bazawara, sun dogara da hadisin Khansā Al-Ansāriyyah, wanda
Bukhari da Abu Dāwud da Nasā’i da Ibn Mājah suka ruwaito cewa
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Bazawara ita ce ke da haqqin (zavar wa) kanta (miji) fiye da
waliyyinta (uba ko waninsa).‛ Dangane da budurwa, sun kafa hujja da hadisin Ibn Abbas (Allah Ya yarda da su), wanda Abu Dāwud da Ibn
Mājah suka ruwaito, cewa wata yarinya (budurwa) ta kawo qarar
mahaifinta wajen Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) cewa ya aurar da ita ga wanda ba ta so. Sai Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‘Idan kin amince a
zartar da auren, za a zartar; idan kuwa ba ki amince ba, za a warware
shi. Ta ce: ‘Na amince. Da ma dai ina son iyaye su san cewa `ya`yansu
na da haqqi wajen aurar da su.‛ Amma yarinyar da ba ta balaga ba a
50
18. Barin `ya`ya mata su fita su kaxai, ba tare da muharrami
ba, ko su fita ba tare da sun sanya cikakken hijabi ba,
musamman daga lokacin da suka balaga.
19. Sayen wayar sadarwa ga qananan yara, ko kuma a qyale
`yan mata su yi amfani da wayar da samari suka ba su.
20. Wulaqanta `ya`ya da qasqantar da su idan sun yi
kuskure, da kuma rashin qarfafa masu gwiwa idan sun yi
abin kirki.
21. Rashin ladabtar da `ya`ya ta hanyoyin da suka dace, idan
sun yi abin da ya kamata a hore su.
22. Rashin saba masu da xaukar nauyin kansu ko xaukar
nauyin wasunsu, gwargwadon iko, tun suna qanana.
23. Rashin qoqarin fahimtar yanayinsu da xabi’unsu, ta
yadda za a san hanyoyin magance matsalolinsu na
tarbiyya.
lokacin da za a aurar da ita, ba dole ne a ba ta zavi ba, kasancewar
sayyidina Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ya aurar da A’isha (Allah
Ya yarda da ita) ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ba tare da ya shawarce ta ba. Sai dai kuma, har a hakan, idan
ta balaga, kuma ta qi yarda da matsayin da babanta ya xauka a
madadinta, waxansu malamai na ganin dole a warware auren.
Wannan ke nuna cewa iyaye ba su da damar su yi wa `ya`yansu
mata auren dole, matuqar dai `ya`yan sun balaga. Idan kuwa suka aurar
da su a bisa tilas, `ya`yan suna da damar su kai qara kotu, domin a
warware. Amma idan `ya`yan suka yi haquri da hukuncin da iyayensu
suka zartar a kansu, shi ya fi, matuqar babu cutarwa a ciki. Idan kuwa
saboda kwaxayi ko kuma wani dalili mara qarfi ne yasa iyayen suka
tilasta masu auren wanda ba su so, musamman idan ba a amince wa
aqida da xabi’ar mutumin ba, ya kamata `ya`yan su qi yarda.
51
24. Rashin ba su damar gyara kuskuren da suka yi, ko
kyautata abin da suka yi shi batsa-batsa, bayan an nuna
masu yadda ya kamata su yi.
25. Rashin damuwa da irin makarantar da su ke zuwa, ko
malaman da ke karantar da su.
26. Qin haxa kai da masu karantarwa a makaranta ko kuma
hukumomi wajen tabbatar da tarbiyyar `ya`ya.
27. Barin al’amarin tarbiyya gaba xaya a hannun iyaye mata,
da watsi da haqqoqin `ya`ya, musamman `yan mata.
28. Barin tarbiyyar `ya`ya a hannun mai reno, musamman
waxanda ba musulmi ba, ko kuma musulmin da ba su
san yadda a ke yin tarbiyya ba.
29. Yawan savani a tsakanin iyaye a gaban `ya`ya, ta yadda
`ya`yan za su koya.
30. Sava wa abin da a ke tarbiyyantar da `ya`ya a kansa, ta
yadda za a nuna masu muhimmancin wani abu, amma su
ga an aikata savaninsa.
YADDA A KE YIN TARBIYYAR `YA`YA
Musulunci gamammen addini ne; babu wani al’amarin da ya
shafi addini da rayuwa, face an yi bayaninsa dalla dalla. An
rattaba dalilan da ke jawo qasqanci da lalacewa a cikin
al’umma, kamar yadda aka bayyana hanyoyin samun nasara
da kuvuta daga kowace irin matsala. An samar da tanade-
tanaden da suka shafi tarbiyya, wadda za ta kai mutane ga
cin nasara. Tanade-tanaden musulunci dangane da tarbiyya
sun haxa da:
52
1. Ba da muhimmanci ga zaven uwa/uba ta/na qwarai, a
lokacin yin aure, a bisa asasin addini da kyawawan
xabi’u, kasancewar hakan na taimakawa wajen samar da
tarbiyya ga `ya`yan da za a haifa, idan Allah Ya kawo.
Uwa ta qwarai, mai riqo da addini, tana da tasiri wajen
tarbiyyar `ya`yanta. Haka kuma, uba na qwarai, mai
addini da kyawawan xabi’u, yana xaukar dukkan
matakan da suka dace, don ganin `ya`yansa sun samu
tarbiyya, da ilmin addini da ilmin sana’a.
Zaven iyaye na qwarai na daga haqqoqin `ya`ya tun
kafin a haife su, kuma yana daga kyautatawar da iyaye
za su yi wa `ya`yansu. Abul Aswad Ad-Du’ali ya ce wa
`ya`yansa:
[Na kyautata maku, kuna qanana da bayan kun girma, da
kuma kafin a haife ku. Suka ce: ‘ta wace hanya ka
kyautata mana kafin a haife mu? Ya ce: ‚Na zavo maku
uwar da ba za a zage ku ba saboda ita]
Haka kuma, Ar-Rayāshi ya ce wa `ya`yansa:
[Farkon kyautatawa ta a gare ku shi ne da na zavar maku
(uwa) mai girmar nasaba da daraja, wadda ta yi fice a
wajen kamun kai]
2. Roqon Allah (Mai girma da xaukaka) zuriyya ta qwarai,
kamar yadda Annabawa da Manzanni (tsira da aminci su
tabbata a gare su) suka kasance suna yi;104
tare da neman
taimakon Allah a cikin yin tarbiyyar `ya`ya. Misali,
104
Aal Imrān, 3:38; Furqān, 25:74
53
Annabi Ibrāhīm (amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya
roqi Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya azurta shi da
salihan `ya`ya;105
Ya nisantar da shi tare da su daga
bautar gumaka;106
kuma Ya sanya shi da zuriyyarsa masu tsai da salla.
107 Haka kuma, Annabi Ibrāhīm (amincin
Allah ya tabbata a gare shi) ya roqi Allah (Mai girma da
xaukaka) Ya sanya zuriyyarsa daga cikin masu yin
jagoranci a cikin imani da taqawa da haquri da
da’awa;108
kuma Ya sanya su masu sallamawa ga Allah
(Mai girma da xaukaka).109
Haka kuma, Annabi
Zakariya (amincin Allah ya tabbata a gare shi) ya roqi
Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya ba shi zuriyya mai
kyau,110
wadda za ta yi aiki tuquru domin yardar da
Allah.111
3. Farin cikin samun haihuwa, da nisantar yin fushi ko
kuma jin xacin rai da baqin ciki, saboda an haifi mace ko
kuma saboda tsoron talauci.112
Yin baqin ciki saboda an
haifi `ya mace, ya qunshi matsaloli guda biyar: jayayya
da qaddarar Allah; da qin karvar kyautar Allah; da
kamanceceniya da xabi’ar mutanen jahiliyya; da
bayyana alamar wawanci da sakarci da jahilci da raunin
hankali; da kuma wulaqanta matsayin `ya mace.
Iyaye su yi qoqarin kiyaye ladubban da suka shafi jariri,
tun kafin haihuwarsa, da bayan an haife shi,113
da
105
Saffāt, 37:100 106
Ibrāhīm, 14:35 107
Ibrāhīm, 14:40 108
Baqarah, 2:124 109
Baqarah, 2:128 110
Aal Imrān, 3:38 111
Maryam, 19:6 112
Isrā, 17:31; Shūrā, 42:49 113
Ladubban sun haxa da: zaven abokan zama na qwarai tun lokacin da
a ke nufin yin aure bisa asasin addini da kyawawan xabi’u; da yin
54
ladubban yin tahnīk,114
da ladubban sanya suna,115
da
yanka dabbar aqiqa,116
da aski,117
da kaciya.118
Babu
addu’a a lokacin kwanciyar aure; da kula da lafiyar uwa a lokacin da ta
ke goyon ciki; da nisantar abubuwan da ke iya kawo haxari ga abin da
ke cikin mahaifa (kamar shan giya ko taba sigari); da yin kyakkyawar
addu’a da zarar an haihu; da godiya ga Allah a kan kyautar da Ya yi
masu. 114
Tahnīk na nufin tauna dabino ko dandaqa shi don sanyawa a cikin
bakin jariri/jaririya bayan haihuwa. Idan an dandaqa ko an tauna
dabinon sai a xiba da yatsar hannun dama, a sanya a cikin bakin jariri, a
jujjuya, dama da hagu, don kowanne vangare ya samu. Bayan haka, sai
a yi addu’ar alhairi da neman albarka da shiriyar Allah gare shi. An so a yi tahnīk da zarar an yi haihuwa, ba tare da dogon jinkiri ba.
Haka Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) da
sahabbansa (Allah Ya yarda da su) suka kasance suna yi. Ba daidai ba
ne a jinkirta wannan aiki zuwa kwana uku, a haqqin namiji, ko kwana
huxu, a haqqin mace, bisa hujjar cewa za a yi huxuba ga jariri/jaririya. Tahnīk ne ya tabbata a cikin Sunnah, ba wai wata huxuba ba.
Ana amfani da busasshen dabino wajen yin tahnīk. Amma Ibn Hajar
ya ce: ‚Idan mutum bai samu busasshen dabino ba, sai ya yi amfani da
kowane irin dabino. Idan bai samu ba, ana iya amfani da duk wani abu
mai zaqi. Sai dai kuma ana fifita zuma a kan sauran abubuwa masu zaqi.‛ [Ahmad bn Aliyyu bn Hajar, Fat-hul Bāri Sharh Sahīh al-Bukhārī, (Dār al-Fikr, Beirut, Lebanon, 1379AH), 9/588]
Da yawa daga malamai na ganin cewa a dandaqa dabinon ya fi a
tauna. Suka ce, tauna dabino ya kevanci Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ne saboda albarkar da ke cikin
yawunsa. Wannan ya sa ba a samu sahabbai sun tauna ba bayan
rasuwar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sai
dai dandaqawa.
Iyayen jariri (uwa ko uba) ko kuma wani daga cikin mutanen kirki ne ya kamata su yi wa jariri tahnīk. Ana iya neman wani bawan Allah,
mai ilmi da taqawa, wanda ya fahimci Sunnah kuma ya ke aiki da ita
gwargwadon iko, wanda a ke sa ran karvar addu’arsa saboda biyayyarsa ga Allah, ya yi tahnīk da addu’a ga jariri ko jaririya a
madadin iyayen.
Huxubar da mutane ke yi wa jarirai bayan kwana uku (a haqqin
namiji) ko kwana huxu (a haqqin mace) wadda ta qunshi kiran salla a
kunnen dama, da yin iqama a kunnen hagu, ko kuma kiran salla a
kunnen dama da hagu, ba ta da inganci. Hadisin da ke magana a kan
55
kiran salla a kunnen dama, da yin iqama a kunnen hagu, ba shi da
inganci ko kaxan. Hasali ma, malamai sun tabbatar da cewa hadisi ne
na qarya (maudu’). Shi kuma hadisin da ke magana a kan kiran salla kawai, ba tare da iqama ba, mai rauni ne (da’īf). Ke nan, ba za a iya
kafa hujja ko a yi aiki da shi ba a cikin wannan muhimmiyar mas’ala.
Don haka, kiran salla da iqama, ko kuma kiran salla kawai da a ke yi
wa jarirai, da sauran abubuwan da a ke yi, da sunan huxubar haihuwa,
ba su tabbata ba. Abin mamaki shi ne yadda mutane da yawa suka jahilci Sunnar tahnīk. Mutane da yawa ba su yi, kuma ba su sanyawa a
yi wa `ya`yansu. Maimakon haka, sai su nemo liman ko wani dattijo
don ya yi huxuba, wani lokaci ma a haxa da surkulle, kai har da sanya
baki a cikin kunnen jariri, a ce: sunanka wane. 115
Wajibi ne iyaye su sanya wa `ya`yansu suna mai kyau, kuma a
lokacin da ya dace. Nazari cikin hadisai ingantattu na tabbatar da lokuta
biyu da a ke iya sanya wa jarirai suna: ranar bakwai ko kuma tun daga
lokacin da aka haihu har zuwa ranar bakwai. Dalili a kan haka yana
qunshe cikin ingantattun hadisai da yawa. Misali, Samurah (Allah Ya
yarda da shi) ya ce: Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Kowane yaro (da aka haifa) jingina ce ga aqiqarsa
(dabbar da a ke yankawa). Za a yanka masa a ranar bakwai, a sanya masa suna, kuma a yi masa aski‛ [Ahmad da Abu Dāwud]. Haka
kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
yi umurni da sanya suna ga abin da aka haifa a rana ta bakwai, da kawar da qazanta (gashi) gare shi, da yanka masa dabba [Tirmidhī].
Haka kuma, Anas (Allah Ya yarda da shi) ya ce: Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚An haifar mani xa
namiji a daren yau, kuma na sanya masa sunan babana (kakana) Ibrāhīm‛ [Muslim]. Haka nan, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya sanya wa Abdullah ibn az-Zubair, da Abdullah ibn Abi Xalhah, da Ibrāhīm ibn Abi Mūsa al-`Ash’arī, da al-Mundhir,
suna a ranar da aka haife su [Bukhari da Muslim].
Daga hadisan da suka gabata, za a fahimci cewa Shari’a ta ba da
damar sanya suna ga jarirai tun daga lokacin da aka haife su har zuwa rana ta bakwai. Baihaqī na ganin cewa hadisan da suka yi magana
game da sanya suna a lokacin da aka yi haihuwa sun fi hadisan da ke
magana a kan jinkirtawa zuwa ranar bakwai inganci. Amma da yawa
daga malamai sun ce jinkirtawa zuwa rana ta bakwai mustahabbi ne,
saboda la’akari da maganar da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi. Sanya suna a ranar da aka yi haihuwa kuwa,
56
halal ne saboda aikin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya tabbatar da hakan.
Waxansu malamai na ganin cewa jinkirta sanya suna har zuwa ranar
bakwai shi ne ya fi idan akwai halin yanka dabbar aqiqa (ragon suna).
Idan kuwa ba za a yanka dabbar ba, sai a sanya sunan tun daga lokacin
da aka yi haihuwar. Amma dai magana mafi qarfi ita ce an so a jinkirta
sanya suna zuwa rana ta bakwai, amma ya halatta a sanya sunan tun
daga ranar haihuwa, ba tare da la’akari da cewa za a yanka dabba ko ba
za a yanka ba. Wannan shi ne abin da hadisan suka tabbatar qarara.
Uba (mahaifi) shi ne ke da haqqin zavar wa xansa suna mai kyau ta
hanyar yin shawara da uwa (mahaifiya). Idan suka yi savani game da
sunan da za a sanya, haqqin sanyawar na ga uba. Idan ya so ya zava da
kansa, idan ya so ya bar uwar ta zava, ko ya yi quri’a a tsakaninsu, ko
ya ba wani mutum damar zavar sunan gare su.
Zaven suna mai kyau, na daga haqqoqin `ya`ya a kan iyayensu.
Sanya wa `ya`ya sunan da ya dace, zai haifar masu da jin daxi, kuma
zai sanya su kazarkazar duk lokacin da aka kira su da shi. Rashin sanya
suna mai kyau yana dakushe tunanin yara da tauye matsayinsu a cikin
al’umma, musamman idan suka fahimci ma’anar sunan, bayan sun
girma. Don haka, wajibi ne iyaye su sanya wa `ya`yansu suna mai
ma’ana, da kyakkyawar lafazi.
Malamai sun bayyana matakai guda biyar waxanda iyaye za su bi
wajen zaven suna mai ma’ana ga `ya`yansu. Kowane mataki ya fi
wanda ke qasan shi daraja. Matakan su ne: sanya sunan Abdullah da Abdur-Rahmān, kasancewar su ne sunayen da Allah (Mai tsarki da
xaukaka) Ya fi so [Muslim da Abu Dawud]; sanya sunan da ke nuna bauta ga Allah, kamar Abdur-Rahīm, Abdul-`Azīz, Abdul-Karīm, da
Abdur-Razzāq; sanya sunan xaya daga cikin Annabawa da Manzanni
(tsira da aminci su tabbata a gare su); sanya sunayen magabata na
qwarai (maza ko mata), kamar sahabbai da tabi’ai da shahidai da
malaman Sunnah; da sanya duk wani suna da ya qunshi lafazi da
ma’ana mai kyau, wanda ke nuna sadaukantaka, ko kamun kai, ko
taqawa. 116
Aqīqah ita ce dabbar da a ke yankawa a rana ta bakwai, ko goma
sha huxu, ko ashirin da xaya, bayan haihuwa. Yanka dabba (rago ko
tunkiya ko bunsuru ko akuya) ga wanda aka haifa, na daga ladubban
Shari’a, waxanda a ke son iyaye su aikata, saboda murna da godiya ga
Allah bisa ni’imarSa da baiwar da Ya yi masu ta samun qaruwa.
Malamai sun yi savani game da hukuncin dabbar da za a yanka wa
wanda aka haifa. Waxansu na ganin cewa wajibi ne a kan duk wanda
57
ke da iko. Sun kafa hujja da maganar Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi): ‚Tare da yaro akwai aqiqar (da za a yanka
masa), don haka, ku zubar da jini a madadinsa…‛ [Abu Dawud da
Tirmidhi]; da hadisin: ‚Kowane yaro jingina ce ga aqiqarsa: za a yanka
masa a rana ta bakwai, kuma a sanya masa suna, a yi masa aski a
wannan rana‛ [Ahmad, Abu Dawud, Tirmidhi, Nasa’i da Ibn Majah].
Suka ce: a cikin hadisin farko, akwai umurnin da Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi game da yanka dabba ga
wanda aka haifa. Sananniyar qa’ida ce cewa umurni na nuna wajibci,
matuqar ba a samu wani dalilin da ke nuna savanin haka ba. Hadisi na
biyu ya nuna qarara cewa kowane yaro na matsayin jingina ce har sai
an yanka masa dabba kafin a fanshe shi. Wannan ra’ayi ya fi qarfi, in
sha Allah. Saboda haka, yanka dabba ga wanda aka haifa, wajibi ne a
kan uba, matuqar yana da iko. Ibn Hazm na daga cikin malaman da ke
ganin wajibci, kuma ya kawo dalilai masu yawan gaske don qarfafa
wannan fahimta. Haka kuma, Ibn al-Mundhir ya ruwaito daga Yahya al-Ansāri cewa salaf (sahabbai da taba’ai) ba su gushe ba, suna ganin
wajibcin yanka dabba ga wanda aka haifa.
Sunnar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ta tabbatar cewa ana yanka wa xa namiji dabbobi guda biyu,
madaidaitan shekaru; `ya mace kuma a yanka mata guda xaya. Wannan ya dace da fatawar Ibn Abbās (Allah Ya yarda da su), da mafi
yawan malamai, kamar Imam as-Shāfi’ī da Ahmad ibn Hanbal.
Hujjojinsu na qunshe a cikin hadisan da Aa’ishah da Umm Kurz da
Amr ibn Shu’aib (Allah Ya yarda da su) suka ruwaito. Ibn Umar (Allah Ya yarda da shi) da Imam Mālik na ganin cewa dabba xaya ce za a
yanka wa xa namiji ko `ya mace.
Haka kuma, Sunnah ta tabbatar da cewa ana iya yanka rago ko
tunkiya ko bunsuru ko akuya. Duk dabbar da aka yanka daga cikin
waxannan, ta wadatar. Amma ba a yin amfani da sauran nau’o’in dabbobi, kamar raquma da shanu, a wajen aqīqa.
Ana yanka dabbar aqiqa ce a ranar bakwai, ko da kuwa an sanya wa
jaririn ko jaririyar suna kafin ranar bakwai. Magana mafi qarfi ita ce za
a fara qirga ranakun ne daga ranar da aka yi haihuwa, ba wai daga
kashegarin ranar haihuwa ba. 117
Aske kan jariri/jaririya na daga cikin abubuwan da a ke son a yi a rana ta bakwai ga haihuwa. Da zarar an yanka aqīqa, sai a gabatar da
aski, a bisa hadisan da suka gabata. Malamai sun yi savani game da `ya
mace: shin za a yi mata aski kamar namiji? Magana mafi qarfi ita ce:
hukuncin wannan aski ya shafi namiji da mace, kasancewar babu wani
58
shakka, kiyaye waxannan ladubba na da matuqar tasiri a
kan tarbiyyar `ya`ya.119
4. Koya masu magana ta hanya mai sauqi. An so kalmar
shahada, wato, , ta zamanto abin da za
dalili mabayyani da ya kevance xaya, ya bar xayan. Hadisan da suka zo
da lafazin ‘yaro’ ( ), na xaukar ma’anar namiji da mace, kamar yadda
kalmar ‘wanda aka haifa’ ( ), ta ke xauka. 118
Kaciya na xaya daga cikin abubuwan da a ke buqatar a yi wa jariri/jaririya a ranar bakwai da haihuwa. Kaciyar maza (khitān) ta
qunshi yanke fatar da ke kewaye da kan azzakari. Kaciyar mata kuwa
(khafd), ta qunshi rage fata ko xan tozon (clitoris) da ke kan farji, wato
tsele. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
sanya kaciya a matsayin xaya daga cikin ayyukan fixrah (xabi’un
addinin Musulunci waxanda Allah Ya halicci mutane a kansu) da a ke
buqatar kowane Musulmi ya kula da su.
Malamai sun yi savani game da hukuncin kaciya. Magana mafi qarfi
ita ce, kaciya wajibi ne a haqqin xa namiji, kuma Sunnah a haqqin `ya mace. Wannan ita ce fatawar Imam Mālik, as-Shāfi’ī da Ahmad ibn
Hanbal. Kuma wannan shi ne abin da ya shahara tun daga zamanin
sahabbai (Allah Ya yarda da su) har zuwa tabi’ai da tabi’ut-tabi’in
(Allah Ya jiqansu), da waxanda suka biyo bayansu.
Mafi yawan malamai na ganin cewa babu wani lokaci na
musamman da aka iyakance don yin kaciya. Kowane lokaci aka so, sai
a yi. Amma waxansu malamai sun ce mustahabbi ne a yi wa
jariri/jaririya kaciya a ranar bakwai. Abin lura shi ne binciken likitanci
ya tabbatar da cewa, kaciya ta fi saurin warkewa idan aka yi ta a ranar
bakwai ko kafin wannan rana, fiye da idan an jinkirta, kasancewar jiki
na samun kariya ta musamman a wannan tsakani. Haka kuma, waxansu muhimman sanadaran jiki, kamar white blood cells da anti-bodies na
yin aiki cikin sauri da sauqi, a wannan tsakani, don kare jiki daga
kamuwa da cututtuka, a sanadiyar yanka ko rauni. Bayan wannan, blood coagulation, da kuma zuciya (liver) na yin aiki sosai, kuma
vitamin K na samuwa a makon farko na haihuwa. Ke nan, yin kaciya a
ranar bakwai ya fi fa’ida, matuqar babu wata larurar da za ta hana a
gudanar da ita a wannan rana. 119
Karanta littafi na Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci
59
a fara koya wa yaro a cikin rayuwarsa, ta yadda zai saba
da ita sosai. Kuma da zarar ya fara wayo, a sanar da shi
ma’anarta, da abin da ta qunsa. Ibn al-Qayyim ya ce:
Farkon abin da za a koya wa yara idan lokacin da za su
fara magana ya zo shi ne: , wato, ya
kasance farkon abin da zai fara shiga cikin kunnuwansu
shi ne: sanin Allah da tauhidinSa, kuma da sanin cewa
Allah Yana sama, Ya daidaitu a kan al’arshinSa;120
Yana
120
Ayoyin Alqur’ani masu yawa, da hadisai ingantattu, da maganganun
Salaf sun tabbatar da cewa Allah (Maxaukaki) Yana sama (al-Uluw), kuma Ya daidaita a kan al’arshinSa (al-Istiwā), daidaituwar da ta dace
da Shi. Daga cikin ayoyin Alqur’ani da suka tabbatar da haka, akwai:
1. Kuma Shi ne al-Qāhir (Mai rinjaya) bisa ga bayinSa…‛
[An’ām, 6:18, 61].
2. Suna tsoron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin
da a ke umurnin su‛ [Nahl, 16:50].
3. Zuwa gare Shi magana mai daxi ke hawa, kuma aiki na qwarai Yana xaukar ta‛ [Fāxir, 35:10].
4. A lokacin da Allah Ya ce: ‚Ya Isa! Ni Mai karvar ranka ne, kuma Mai xauke ka ne zuwa gare Ni..‛ [Aal Imrān, 3:55].
Daga cikin hadisan da suka tabbatar da cewa Allah (Maxaukaki)
Yana sama, kuma Ya daidaita a kan al’arshinSa, daidaituwar da ta
dace da Shi, akwai:
1. Hadisin da Bukhari ya ruwaito daga Anas (Allah Ya yarda da
shi) cewa Zainab bnt Jahsh (xaya daga cikin matan Annabi) ta
kasance tana yin alfahari ga sauran matan Annabi (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) cewa iyayensu ne suka
aurar da su ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi); amma ita, Allah (Mai girma) ne da kanSa Ya aurar
da ita ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) tun daga bisan sama bakwai.
60
2. Hadisin da Muslim ya ruwaito daga Mu’āwiyah bn al-Hakam
cewa ya zo da wata baiwarsa zuwa ga Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi). Sai Annabi (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya tambaye ta: ‚Ina Allah
Yake? Sai ta ce: ‚Yana sama‛. Sai ya ce: ‚Wane ne ni‛? Ta ce:
‚Manzon Allah‛, sai ya ce: ‚`yanta ta, domin kuwa mumina
ce‛.
3. Hadisin da Bukhari da Muslim suka ruwaito cewa Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Yanzu ba za ku amince mani ba, alhali kuwa ni ne wanda
(Allah da) ke sama Ya amince wa?‛
4. Hadisin da Bukhari da Muslim suka ruwaito daga Abu
Hurairah (Allah Ya yarda da shi), Annabi (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Bayan Allah Ya kammala
halitta, sai Ya rubuta a cikin littafin da ke wajenSa a saman
al’arshinSa: ‘Rahamata ta rinjayi fushina‛.
5. Hadisin da Muslim ya ruwaito daga Jābir (Allah Ya yarda da
shi), da ke magana a kan Isra’i da Mi’irajin da Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi daga
Makkah zuwa Masjid al-Aqsa, daga nan kuma, zuwa wajen
Allah a can bisan sama ta bakwai‛.
6. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
ce: ‚Ku yi jin qai ga (bayin Allah) waxanda ke qasa, sai (Allah) Wanda ke sama Ya ji qanku‛ [Tirmidhī ya ruwaito
kuma ya ce: Hasan Sahīh].
7. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
ce: ‚Babu wata macen da mijinta zai kira ta zuwa ga
shimfixarsa, amma ta qi zuwa, face (Allah) Wanda ke sama Ya
yi fushi da ita har sai mijinta ya yarda da ita‛ [Muslim].
Daga cikin bayanan da aka ruwaito daga Salaf dangane da wannan
mas’ala, akwai:
1. Maganar da ‘Abdullah bn Ahmad, da Ibn Abi Shaybah, da al-Lālakā’ī, da Ibn ‘Abdil-Barr, da al-Mundhirī suka ruwaito
61
cewa Abu Bakr, da Umar, da Uthmān, da Aliyyu, da Ibn
Abbās, da Ibn Mas’ūd, da sahabbai masu yawan gaske sun
tabbatar da cewa Allah (Mai girma) Yana sama [Duba littafin Ithbāt Siffah al-Uluw na Ibn Qudāmah al-Maqdisī, shafi na 45-
73, da at-Tuhfah al-Madaniyyah fi al-`Aqīdah as-Salafiyyah na
Hamd bn Nāsir bn Uthmān Aali Ma’amar, shafi na 29-50]
2. Bayanai ingantattu da aka ruwaito daga Sufyān at-Thaurī, da
al-Hasan al-Basarī, da al-Auzā’ī, da Imām Abu Hanīfah, da
Mālik, da ash-Shāfi`ī, da Ahmad, da ad-Dahhāk, da Rabī`ah bn
‘Abdir-Rahmān, da malamai masu yawa daga cikin tabi’ai da
tabi’ut-tābi’in cewa Allah Yana sama [Duba littafin Ithbāt Siffah al-Uluw na Ibn Qudāmah al-Maqdisī, shafi na 110-132 ;
da at-Tuhfah al-Madaniyyah fi al-`Aqīdah as-Salafiyyah na
Hamd bn Nāsir bn Uthmān Aali Ma`amar, shafi na 71-101].
Dangane da daidaituwar Allah (al-Istiwa) a saman al’arshinSa,
daidaituwar da ta dace da Shi, ayoyin Alqur’ani guda bakwai sun tabbatar da haka. Ayoyin su ne: A’arāf, 7:54; Yunus, 10:3; Ra’ād, 13:2;
Xāha, 20:5; Furqān, 25:59; Sajdah, 32:4; da Hadīd, 57:4.
Daga bayanan da suka gabata, za a fahimci cewa Allah (Mai girma
da xaukaka) Yana sama, kuma Ya daidaita a kan al’arshinSa,
daidaituwar da ta dace da girmanSa. Amsar da waccan baiwa ta ba da, a
lokacin da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ya tambaye ta wurin da Allah Ya ke (ta ce: Yana sama), ita ce amsar da
ya kamata kowane musulmi na qwarai ya karva, matuqar dai ba yana
ganin ya fi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
sanin tauhidi ba ne. Imam adh-Dhahabī ya tattara maganganun Sahabbai da Tabi’ai da
Tabi`ut-Tābi`īn da waxanda suka bi hanyar magabata na qwarai (Salaf) waxanda ke tabbatar da cewa Allah Yana sama, kuma Ya daidaita a
kan Al’arshinSa. Ya ruwaito irin wannan fahimta daga magabata fiye da xari biyu (200) a cikin littafinsa mai suna al-Ulū lil `Alī al-Ghaffār. Abu Ismā`īl al-Ansārī ya ruwaito, a cikin littafinsa ‘al-Furūq’, cewa
an tambayi Imam Abu Hanīfah game da mutumin da ya ce bai san inda
Allah Ya ke ba. Sai Abu Hanīfah ya amsa da cewa: ‘ya kafirta’, domin
kuwa Allah Ya ce: ‚Mai Rahama, Ya daidaita a kan Al’arshi‛ [Xāha,
20:5], kuma Al’arshinSa yana bisan sama bakwai’. Sai aka ce masa to
idan mutum ya ce Allah Yana saman Al’arshi amma kuma bai san inda Al’arshin ya ke ba (a sama ne ko a qasa) fa? Sai (Abu Hanīfah) ya ce:
62
ganinsu, Yana jinsu, kuma Yana tare da su (da ilminSa,
da jinSa, da ganinSa, da ikonSa, da qudurarSa) a duk
inda su ke.‛121
5. Dasa masu imani da aqida sahihiya tun suna qanana, da
tsoratar da su daga munanan aqidu da haxarin shirka da
bidi’a a cikin addini. Idan yara suka taso da fahimtar
sahihin tauhidi da aqida ta qwarai, wadda ta dace da
Alqur’ani da Sunnah ingantacciya, bisa fahimtar
magabata na qwarai, a na fatan su kafu a cikin addini,
kuma su goge a kan karantarwarsa.
Babu shakka, koya wa yara kalmar shahada da
sharuxxanta, da rukunan imani, da abubuwan da suka
qunsa, da abubuwan da ke warware kalmar shahada, da
sauran vangarorin tauhidi, waxanda mutane ke sakaci
game da su, abu ne muhimmi.122
Idan yaro ya fahimci
‘ya kafirta’, domin kuwa ya yi musun cewa Allah Yana sama. Wanda
duk ya yi musun haka kuwa, ‘ya kafirta’‛ [Duba littafin at-Tuhfah al-Madaniyyah fil `Aqīdah as-Salafiyyah na Hamd bn Nāsir bn Uthmān
Aali Ma’amar]. Imam Mālik ya tabbatar da kasancewar Allah Yana sama, kuma Ya
daidaita a kan al’arshinSa, daidaituwar da ta dace da Shi. Haka kuma, Abul Hasan ‘Aliyyu al-Ash`arī, wanda mutane da yawa ke da’awar
koyi da shi a cikin aqidar sufanci, ya tabbatar da cewa Allah Yana sama, a cikin littafansa ‘al-Ibānah an usūl ad-Diyānah’ da ‘al-Maqālāt al-Islāmīyīn’. Ban da waxannan, Ibn Abi Zayd al-Qīrawānī al-Mālikī,
ya tabbatar da daidaituwar Allah a kan al’arshinSa a sama, a cikin mashahurin littafinsa ar-Risālah. 121
Tuhfah al-Maudūd, shafi na 158 122
Vangaren farko na kalmar shahada, wato, na da sharuxxa
guda tara (9). Waxannan sharuxxa su ne mabuxin kai wa ga duk wata
falala da aka tabbatar wa kalmar shahada. Sharuxxan su ne: ilmin da
ke kore jahilci [Muhammad, 47:19; Zukhruf, 43:86]; yaqini wanda ke kore shakku [Hujurāt, 49:15]; karvar abin da kalmar ta qunsa, da kuma
yarda da abin da ta ke lazimtawa, a kan harshe, da cikin zuciya [Saffāt,
37:35-36]; miqa wuya da sallamawa da jawuwa zuwa ga kalmar, ta
63
hanyar tabbatar da ita a aikace [Luqmān, 31:22; Zumar, 39:54; Nisā,
46:5; Ahzāb, 33:36]; gasgata kalmar, da karvarta, ba tare da wasa ko
yaudara ba [Ankabūt, 29:1-3; Baqarah, 2:8-10]; tsantsar ikhlasi da
kuma yarda da kalmar saboda Allah, ba tare da munafinci ba [Zumar,
39:2; Bayyinah, 98:2]; son kalmar, da kuma qin duk abin da ya sava ma ta [Baqarah, 2:165; Mā’idah, 5:54; Taubah, 9:2]; kafirce wa duk
wani xagutu, da sauran tsare-tsaren da suka sava wa na Allah [Baqarah,
2:256]; tabbatuwa da dogewa a kan kalmar, har zuwa mutuwa [Aal Imrān, 3:102]
Vangare na biyu na kalmar shahada, wato, na lazimta: (1)
imanin cewa Muhammad ibn Abdillah manzo ne daga Allah (2)
gasgata shi cikin duk abin da ya ba da labari (3) yin masa xa’a cikin
umurni da hani (4) taqaita yin bautar Allah (Mai girma da xaukaka) ga
abin da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
shar’anta (5) qudurce cewa shi ne Annabin qarshe, kuma shugaban
Manzanni (6) qudurce cewa saqon da ya zo da shi daga wajen Allah
(Mai girma da xaukaka) gamammen saqo ne ga mutane da aljannu. Al-walā (soyayya da jivinta al’amari) wal Barā (qiyayya da tawaye)
na daga abubuwan da kalmar shahada ke lazimta wa kowane musulmi a cikin zuciyarsa, kuma tasirin hakan ya bayyana a gavuvvansa. Al-walā ya qunshi son `yan’uwa musulmi, da jivinta al’amari a gare su, saboda
imaninsu da xa’arsu ga Allah, ba tare da la’akari da bambancin ra’ayi ko fahimta ko jinsi ba. Al-barā ya qunshi yin qiyayya da tawaye ga
kafirai da munafikai, saboda kafircinsu ko munafincinsu, da sava wa
Allah da su ke yi, ba tare da la’akari da dangantaka ko zumunci ko
matsayi ba. Al-walā wal-barā, na daga cikin al’amuran tauhidi, wanda kafiran
duniya su ke qoqarin ganin an yi watsi da su a wannan lokaci, ta yadda
Musulmi zai daina kishin addininsa gaba xaya, kuma ya daina qyamar
kafirci ko nuna qiyayya ga kafirai. Burin su shi ne, a wayi gari,
Musulmi ya daina ganin bambanci a tsakanin xan uwansa Musulmi da
kuma arne, ko kuma ya riqa ganin cewa babu bambanci tsakanin
Musulunci da kafirci. Wannan ya sa suka xauki matakan qyamatar wa Musulmi alamomin da ke tabbatar da Al-walā ga muminai da kuma Al-barā ga kafirai.
Yana daga alamomin da ke tabbatar da al-walā ga muminai: yin
qaura daga qasashen kafirai zuwa qasashen musulmi; da taimakon
musulmi ta hanyar amfani da dukiya da jiki da harshe; da tausaya wa
musulmi a duk lokacin da wani abin baqin ciki ya same su, da yin farin
ciki a duk lokacin da wani alhairi ya same su; da yin masu nasiha da ba
64
tauhidi tun yana qarami, zai taso da kyakkyawar
fahimtar addini, ta yadda zai kuvuta daga kwamacala, da
canfe-canfe, da munanan al’adu, da tsoron wanin Allah,
kamar aljannu ko dodo, da sauransu. Kuma a na sa ran
su shawara; da mutunta musulmi da girmama su, tare da nisantar
qasqantar da su ko faxin aibi game da su; da kasancewa tare da su a
cikin kowane irin hali da yanayi; da ziyartar su, da son haxuwa da su;
da girmama haqqoqinsu, da ba su haqqoqin da suka cancanta; da yin
masu addu’ar alhairi, da nema masu gafarar Allah (Mai girma da
xaukaka).
Yana daga alamomin da ke nuna soyayya ga kafirai, maimakon a yi
qiyayya da su: koyi da su wajen tufafi da kevantattun al’adunsu; da
ziyartar qasashensu don yawon shaqatawa da buxe ido; da taimakon
kafirai a kan musulmai; da kare martabar kafirai da yabonsu; da amince
masu, ta yadda za a bayyana sirrin musulmi a gare su; da amfani da
ranakun hutun da ke cikin kalandarsu; da taimakonsu wajen bikin
kirsimati ko taya su murnar kirsimati da sauran bukukuwansu na
addini; da amfani da sunayensu; da yin masu addu’ar neman gafara
bayan sun mutu; da fara yin masu sallama idan an haxu da su. Wajibin kowane Musulmi ne ya tabbatar da manufar Al-walā wal-barā a cikin rayuwarsa gaba xaya, ko da kuwa fanxararrun mutane za
su zarge shi da ta’addanci ko tsanani a cikin addini. Sanannen abu ne cewa, ba domin Al-walā wal-barā ba, ba za a bambance tsakanin
al’ummar musulmai da ta kafirai ba.
Kalmar shahada na warwarewa idan aka aikata xayan waxannan
abubuwa: (1) shirka ko munafinci babba ko kafircin da ke fitar da
mutum musulunci (2) xaukar waxansu mutane a matsayin tsani a
tsakanin bawa da Allah, da dogaro da su, da neman taimakonsu a cikin
abubuwan da babu wanda ke da iko sai Allah (Mai girma da xaukaka)
(3) rashin xaukar mushirikai a matsayin kafirai ko kuma yin shakku
game da kafircin kafirai (kamar maguzawa da kirista da yahudu da
sauransu) (4) xaukar cewa akwai wata shiriyar da ta fi shiriyar Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (5) qin wani abu da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya zo da
shi, ko da kuwa an yi aiki da shi (6) yin izgili ga wani sashe na addinin
musulunci ko wani sakamako da musulunci ya tabbatar (7) sihiri da
tsafi (8) taimakon mushirikai a kan musulmai (9) qudurta cewa akwai
waxanda ba su da buqatar bin shari’ar Allah, saboda matsayinsu a
wajen Allah (Mai girma da xaukaka) (10) juya wa addinin Allah (Mai
girma da xaukaka) baya.
65
ya taso da kishin addininsa, da ganin girman Allah (Mai
girma da xaukaka) da ManzonSa (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi), da rashin damuwa, ballantana,
ruxuwa da tsare-tsaren da suka sava wa na Allah
(Maxaukaki). Wannan yasa Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance yana
koya wa yara mas’alolin tauhidi dabam daban,
musamman waxanda mutane suka fi yin kurakurai a kai.
Hadisi ya tabbata cewa Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya tambayi wata yarinya
(baiwa): ‚Ina Allah Ya ke? Ta ce: Yana sama. Ya ce: Ni
wane ne? Ta ce: Manzon Allah. Sai (Manzon Allah) ya
ce (wa maigidanta): ‚`Yanta ta, domin kuwa mumina ce.‛
123 Haka kuma, ya ce wa Abdullah ibn Abbās (Allah
Ya yarda da su): ‚… Kuma idan za ka yi roqo, ka roqi
Allah; idan za ka nemi taimako, ka nemi taimakon
Allah…‛124
6. Fahimtar da `ya`ya wajibcin son Allah (Mai tsarki da
xaukaka), da son Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi), da sahabbai (Allah Ya yarda da
su) da mutanen gidan Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), da sauran mutane na qwarai,
waxanda ke bin Alqur’ani da Sunnah, sau da qafa, tun
daga tabi’ai (Allah Ya jiqansu) har zuwa yau.125
Ta
123
Muslim 124
Ahmad da Tirmidhi: Sahīh 125
Karatun Alqur’ani da Sunnah da aiki da abin da suka qunsa shi ne
zaman lafiya ga kowane musulmi. Alqur’ani maganar Allah ce da aka
saukar wa Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi),
kuma a ke bauta wa Allah ta hanyar karanta shi. Sunnah ta qunshi duk
wata magana ko aiki ko tabbatarwa ko siffar halitta ko siffar xabi’a da
aka danganta zuwa ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi). Da yawa daga malamai na xaukar ‘Sunnah’ da ‘Hadīth’ da
‘Athar’ da ‘Khabar’ a matsayin abu xaya.
66
Alqur’ani littafi ne da ya qunshi shiriya, da haske, da rahama, da
waraka. Yana qunshe da labarin al’ummomin da suka gabace mu, da
abubuwan da za su zo a bayanmu, da hukunce-hukuncen da ke
tsakaninmu: wanda ya sanya Alqur’ani a gaba, zai yi masa jagoranci
zuwa ga aljanna; wanda ya sanya shi a bayansa, zai tunkuxa shi zuwa
wuta.
Alqur’ani bayani ne na gaskiya, wanda ya qunshi hikima, da wa’azi, da hujjoji mabayyana, da ambato na dindindin [Nahl, 16:89; Isrā, 17:9;
Yunus, 10:57]. Littafi ne da bai qunshi tukka da warwara ba, kuma varna ba ta shigo masa ta kowace fuska [Nisā, 4:82; Fussilāt, 41:42].
Littafi ne da ya yi wa kansa shaidar asali, kuma ya tabbatar da
mu’ujizar kansa, sannan, ya qalubalanci wanda ke da shakku ko kokwanto a kansa [Isrā, 17:88; Hud, 11:13; Yunus, 10:38; Baqarah,
2:23]. Littafi ne da ya ke da sunaye guda biyar [Baqarah, 2:185; Kahf, 18:1; Furqān, 25:1; Hijr, 15:9; Nisā, 4:174] da siffofi fiye da hamsin,
kamar yadda ya zo a cikin littafin Al-Burhān fi Ulūmil Qur’ān na Az-
Zarkashi, kuma Abdullah ibn Fodio ya naqalo a cikin littafin Al-Farā’idul Jalīlah.
Sunnah ita ce wahayi na biyu ( ) da ba a bauta wa Allah ta
hanyar mujarradin karanta shi ( ), savanin Alqur’ani, wanda a
ke bauta wa Allah ta hanyar mujarradin karanta shi. Allah (Maxaukaki)
Ya yi wa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
wahayin Sunnah kamar yadda Ya yi masa wahayin Alqur’ani, kuma Allah Ya kira ta da suna Hikmah [Aal Imrān, 3:164; Nisā, 4:113;
Baqarah, 2:231, 129, 151; Juma’ah, 62:2; Ahzāb, 33:34].
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya saukar da Alqur’ani ga Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), kuma Ya umurce
shi da yin bayani game da abin da Alqur’ani ya qunsa [Nahl, 16:44].
Bayanin da aka umurci Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi, ya qunshi (1) isar da Alqur’ani da karantar da shi gaba xaya [Mā’idah, 5:67] (2) bayanin lafazi ko jumla ko aya, tare
da bayanin hukunce-hukuncen da ke cikin ayoyin Alqur’ani gaba xaya,
ta hanyar qarfafa umurni ko hani, da qarin bayani ta fuskar rarrabe abin
da ya zo a dunqule ko iyakance sakakken hukunci ko keve gamammen hukunci ko bayanin Nāsikh da Mansukh ko bayanin hukuncin da ya zo
savanin zahiri (3) zuwa da wani hukuncin da ba shi a cikin Alqur’ani,
kamar xaure mazinacin da bai tava yin aure ba bayan bulala xari, da
hukuncin saduwa da iyali a lokacin azumi, da haramcin zinare da siliki
ga maza.
67
wannan hanya ce, yara za su taso a matsayin ahlus-
sunnah cikakku, waxanda za su bi hanyar magabata na
qwarai.126
Wajibi ne kowane musulmi ya yi riqo da Alqur’ani da Sunnah,
domin kuwa: (1) su ne wahayin da Allah (Maxaukaki) Ya yi wa
bayinSa umurni da su yi riqo da shi (2) su ne kawai za a riqe domin a
kuvuta daga vata da barin hanyar Allah (3) duk wanda ya bar Sunnar
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya halaka
(4) Sunnar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ta qunshi dukkan abin da ke kai mutane aljanna (5) Alqur’ani da
Sunnah ne kawai za su iya haxa kan musulmi (6) ta hanyar Sunnah ce
kawai za a iya fahimtar bidi’a da musibarta da sharrinta (7) riqo da
Alqur’ani da Sunnah a bisa fahimtar magabata na qwarai shi ne
maganin karkacewar fahimta da shiga ruxu, kuma shi ne rigakafin
bidi’a da vata. ,
126 Ahlus-Sunnah su ne waxanda ba su da wani wanda su ke yi wa
biyayya kai tsaye, ta kowane hali da yanayi, kuma a cikin magana da
aiki, sake ba qaidi, sai Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi), farin jakada. Su ne waxanda suka fi kowa sanin
maganganun Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi), da ayyukansa, da halayensa, kuma su ne waxanda suka fi kowa iya
bambancewa tsakanin abin da ya inganta daga gare shi, da wanda bai
inganta ba. Su ne sahabbai (Allah Ya yarda da su) da tabi’ai da
waxanda suka bi hanyarsu bisa kyautatawa, kuma suka ta’allaqa
fahimtar addini bisa fahimtarsu.
Ahlus-Sunnah su ne Salafiyyun ( ), kamar yadda Ibn Hazm [a
cikin littafin Al-Fisal] da Ibn Taimiyyah [a cikin Majmu’ul Fatāwa]
suka bayyana. Su ne Ahlul Hadīth ( ) ko As-hābul Hadīth (
), kamar yadda As-Sābunī [a cikin littafin Sharhul Aqīdatis
Salafiyyah] ya bayyana, kuma aka ruwaito irin wannan magana daga Imam Ahmad ibn Hanbal da Ibnul Mubārak. Su ne a ke kira Ahlul
Athar ( ) ko Ahlul Ittibā’ ( ), saboda riqonsu ga Sunnah a
bisa fahimtar magabata. Su ne Al-Firqatun Nājiyah ( ), kamar
yadda aka ruwaito daga Ibn Jarīr Ax-Xabarī da Ad-Dahhāk da Ibn
Baxxah. Su ne Ax-Xā’ifatul Mansūrah ( ), kamar yadda aka
ruwaito daga wajen Ibnul Madīnī da Abubakar Al-Ājurriy; su ne
Ahlus-Sunnah wal Jamā’ah ( ), kamar yadda Abdul-Qādir
68
Jīlāni ya bayyana a cikin littafin Al-Gunyah. Kuma su ne Al-Gurabā
( ), kamar yadda aka ruwaito daga Abdān.
Da’awar Ahlus-Sunnah ta ginu ne a kan asasi guda takwas: (1)
tsantsar tauhidi (2) tsantsar biyayya ga Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), da riqo da Alqur’ani da Sunnah, bisa
fahimtar magabata na qwarai (3) barin bidi’a, da nisantar ma’abota
bidi’a (4) neman ilmi mai amfani (wanda aka gina shi a kan dalili
sahihi), da aiki da shi, da karantar da shi (5) at-Tasfiyyah (tsaftace
kowane ilmi daga kwamacala, da surkulle, da hadisan qarya ko masu
rauni, da ra’ayoyin da ba a gina su a kan dalili ba, da tatsuniyoyi) da at-Tarbiyyah (aiki da tataccen ilmi, da koyar da shi ga mutane, da
tarbiyyantuwa a kan abin da ya qunsa) (6) watsi da qungiyanci da
ta’assubanci, wato, maqalqalewar ido-rufe, ga mazhabobi (7) bayyanar
da sharrin da ke cikin dokokin da suka sava wa dokokin Allah, da
qudurce aibobi da sharrin da ke cikin dukkan tsare-tsaren da suka sava
wa Shari’ar Musulunci (8) kiran mutane zuwa ga dukkan nau’o’in
jihadi don xaukaka kalmar Allah, ta hanyar amfani da harshe, da
alqalami, da dukiya, da rayuwa.
Ahlus-Sunnah na da waxansu siffofi da suka kevanta da su: (1) su
ne `yan tsaka-tsaki a cikin aqida, da ibada, da gudun duniya, da
sauransu, ba tare da wuce gona da iri, ko gazawa ba (2) sun taqaita
kansu ga Alqur’ani da Sunnah bisa fahimtar magabata na qwarai (3) ba
su da wani shugaban da su ke karvar kowace magana ya yi, ko su ke
barin duk abin da ya sava masa, sai Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) (4) ba su yin husuma a cikin addini, kuma
suna nisantar jidali da musu a cikin mas’alolin fiqihu waxanda aka yi
savani a kai (5) suna girmama magabata na qwarai (salaf), kuma sun
qudurce cewa hanyar salaf ita ce hanya mafi daidai (6) suna watsi da
tawili a cikin sunayen Allah (Mai girma da xaukaka) da siffofinSa,
kuma suna sallama wa duk wani nassi ingantacce (7) ba su ware wani
nassi shi kaxai, su yi aiki da shi, ba tare da sun haxa shi da sauran
nassosin da suka sava masa ko suka qarfafe shi ba (8) ba su
dangantuwa ga wani abu, face Musulunci da Sunnah da jama’a,
savanin waxanda ke dangantuwa zuwa ga xariqun sufaye, kamar
tijjaniyya da qadiriyya (9) suna da tsananin kwaxayi wajen yaxa
sahihiyar aqida da miqaqqen addini, da karantar da mutane.
Malamai irin su Al-Asbahāni, a cikin ; da Ibn
Taimiyyah, a cikin ; da Az-Zahabi, a cikin ; da
Suyuxi, a cikin , na ganin wajibcin dangantuwa zuwa ga
69
Wajibi ne a kan iyaye su cusa qauna da soyayyar Allah
(Maxaukaki) da ManzonSa (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) a cikin zukatan `ya`yansu, da karantar
da su girman Allah da matsayin Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi), da wajibcin yin
masu xa’a, a cikin tsanani ko sauqi, da qunci ko
walwala.127
Wannan zai sanya `ya`ya su fifita son Allah
, kuma sun bayyana cewa yin haka, alama ce ta . Don haka
ya halatta a siffanta wani da , kamar yadda Az-Zahabi, a cikin
ya danganta Ad-Dāra Quxnī, ko , kamar yadda Suyuxi, a
cikin ya danganta Ibn Salah. Bayan wannan, ya halatta
mutum ya kira kansa , kamar yadda Zainul Irāqī ya yi a cikin
muqaddimar littafinsa , ko kuma , kamar yadda As-
Sam’āni ya yi a cikin littafin . 127
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya girmama Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) da manzanci; Ya keve shi da isar
da saqo, Ya saukar masa da Alqur’ani, kuma Ya bayyana cewa shi ne
Manzon fiyayyar al’umma, Manzon rahama, Annabin qarshe, mai
bushara da gargaxi, wanda ba ya furuci bisa son zuciya.
Matsayin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) abu ne mai girma a wajen duk wani mumini. Allah (Mai girma da
xaukaka) Ya bayyana cewa biyayya ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) wajibi ne [Anfāl, 8:20; Nur, 24:56; Nisā,
4:64; Aal Imrān, 3:132; Nisā, 4:59; Muhammad, 47:33; Hashr, 59:36];
biyayya ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) biyayya ce ga Allah [Nisā, 4:80]; ayyukan da aka yi bisa biyayya ga
Allah (Mai girma da xaukaka) da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) a na samun lada cikakke [Hujurāt, 49:14]; gafarar
zunubi da samun shiriya na rataye ne da biyayya ga Manzo [Nur, 24:54; Aal Imrān, 3:31]; biyayya ga Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ita ce alamar son Allah [Aal Imrān, 3:31];
waxanda suka yi biyayya ga Allah (Mai girma da xaukaka) da
ManzonSa (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) na daga cikin waxanda aka yi wa ni’ima [Nisā, 4:69]; waxanda ba su yin biyayya ga
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ba muminai ba ne [Nisā, 4:65]; waxanda ke sava wa Manzon Allah (tsira
70
(Mai girma da xaukaka) da son Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) a kan son kowa,
kuma su fifita xa’ar Allah (Mai girma da xaukaka) da
xa’ar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) a kan xa’ar kowane mutum.128
da amincin Allah su tabbata a gare shi) sakamakonsu shi ne vata da barin hanyar Allah [Ahzāb, 33:36]; waxanda ke sava wa Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) na cikin haxari, a nan duniya, kuma suna fuskantar azaba a lahira [Nisā, 4:115; Nur, 24:63;
Jinn, 72:23; Ahzāb, 33:66; Nisā, 4:42]; samun nasara da babban rabo a
duniya da lahira na cikin yin biyyaya ga Allah (Mai girma da xaukaka)
da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da sallamawa a gare su [Nur, 24:51-52; Nisā, 4:18]; Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) shi ne abin koyi ga kowane mumini [Ahzāb, 33:21]. 128
Son Allah (Mai girma da xaukaka) da son Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) na da alamomi. Da waxannan
alamomin ne a ke bambance mai soyayya ta gaskiya, daga xan boge:
wanda duk bai siffantu da waxannan alamomi ba, soyayyar da ya ke yi
wa Allah (Mai girma da xaukaka) da ManzonSa (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ba gaskiya ba ne, kamar yadda Al-Qādi Iyād, da
An-Nawawi, da Ibnul Qayyim, da Ibn Hajar suka bayyana.
Alamomin son Allah su ne: (1) tsantsar biyayya ga Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (2) tausasawa ga muminai
da tsanantawa ga kafirai (3) jihadi don xaukaka addinin Allah, ta
hanyar amfani da rai, da hannu, da harshe, da dukiya (4) rashin tsoron
zargi a wajen aikata abu domin Allah (5) ikhlasi a cikin bautar Allah
(6) fifita Lahira (7) son abin da Allah (Maxaukaki) Ya ke so (8) kiyaye
haqqoqin Allah.
Alamomin son Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) sun haxa da: (1) kwaxayin ganinsa da son sahabbantakarsa, da
damuwa a kan rashin ganinsa, da gabatar da shi, da fifita shi a kan
kowa, da koyi da shi (2) ladabi a gare shi, ta hanyar yabo, da salati, da
yawan ambatonsa, da ladabtuwa wajen ambatonsa, da ladabi a cikin
masallacinsa (3) gasgata shi a cikin duk abin da ya ba da labari (4) yin
masa xa’a, da bin hanyarsa, da shiryuwa da shiriyarsa (5) mai da
Sunnarsa a matsayin mai hukunci (6) tsare martabarsa, da matsayin
sahabbansa, da matsayin iyalinsa, da sauran mutanen gidansa (7) kare
Sunnarsa, da tsaftace ta daga abubuwan da ba su inganta ba, da karantar
71
Haka kuma, ilmantar da `ya`ya matsayin sahabbai129
da
mutanen gidan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su da ita, da yaxa ta, da mai da martani ga shubuhohi da ruxanin da
maqiyanta ke shigarwa cikinta.
Zagin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ko faxin kalmomi na izgilanci ko qasqanci ko cin mutunci a gare shi,
kafirci ne. Wanda ya yi haka, ya zama kafiri, kuma jininsa ya halatta. A
cikin littafin , Ibn Taimiyyah ya naqalo maganar Ishāq ibn
Rāhawaih cewa ‚Musulmi sun yi ijma’i a kan duk wanda ya zagi Allah
(Maxaukaki), ko ya zagi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi), ko ya kore wani abu daga cikin abin da Allah
(Maxaukaki) Ya saukar, ko ya kashe wani daga cikin Annabawa, ya
kafirta, ko da ya yarda da dukkan abin da Allah Ya saukar‛. Haka
kuma, Muhammad ibn Suhnun ya ce: ‚Malamai sun yi ijma’i a kan duk
wanda ya zagi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ko ya ci mutuncinsa, kafiri ne; ya cancanci narkon azabar Allah,
kuma manyan malamai sun ba da fatawar kisa a kansa…‛
Malamai sun dogara da ayoyin Alqur’ani da hadisai masu yawan
gaske wajen tabbatar da hukuncin kafirci da kisa ga wanda duk ya yi
haka bisa ilmi. A cikin Alqur’ani, sun dogara da ayoyin Taubah, 9:29, 12; Ahzāb, 33:57; da Taubah, 9:65-66. A cikin hadisan Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), sun kafa hujja da hadisin Ka’ab ibnul Ashraf da Abdullah ibn Ubay ibn Salūl dangane da
umurnin kisa da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ba da a kansu bayan saukar ayar Taubah, 9:57 [Bukhari da
Muslim]; da banzantarwar da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi ga jinin Bayahudiyar da ke zaginsa, bayan
wani makaho ya maqure ta har ta mutu [Abu Dawud]; da hadisin
makahon da ya kashe baiwarsa bayan ya hana ta zagin Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), amma ba ta hanu ba [Abu Dawud da Nasā’i]; da hadisin ‘Asmā bint Marwān Al-khaxamiyyah,
wadda ta yi wa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) zambo, da cin mutunci, a cikin waqa, shi kuma ya ba da umurnin a kashe ta [Al-Qadā’iy]. 129
Sahabi shi ne wanda ya haxu da Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), yana mai imani da shi, kuma ya mutu a
cikin musulunci. Sahabbai (Allah Ya yarda da su) su ne mazajen farko
a cikin wannan addini, kuma manya xibar fari; sun rayu da Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), suka yi imani da
72
tabbata a gare shi), wato, ahlul baiti,130 da karantar da su
falalarsu, da adalcin sahabbai, da qoqarin da suka yi wa
shi, suka taimaka masa, suka aura daga gare shi, ya aura daga gare su,
suka ci tare, suka sha tare, suka fita tare, kuma suka shiga tare. Su ne
mafi gaskiya da karamcin mutane, waxanda suka fifita son Allah (Mai
girma da xaukaka), da ManzonSa (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi), da addininSa a kan rayukansu, da dukiyoyinsu, da `ya`yansu.
Sun ba da rayuwarsu da dukiyarsu da lokacinsu wajen xaukaka addinin
Allah (Maxaukaki); suka bar gidajensu da iyalinsu, suka kekketa
dazuzzuka, suka rarratsa gonaki, suka tsattsallake ramuka, suka
wurwuce tafkuna, suka hahhaye kwazazzabai, suka kukkutsa gabas da
yamma, kudu da arewa na duniya, suka qaurace wa iyalinsu da
`ya`yansu, domin su kare martabar addini kuma su xaga matsayinsa.
Babu shakka, sahabbai (Allah Ya yarda da su) sun kasance masu
gaskiya da ikhlasi, da riqon amana da cika alqawari, kuma da qoqarin
da’awa da isar da saqon Allah.
Aqidar Ahlus-Sunnah game da sahabban Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ta qunshi: (1) qudurce cewa
sahabbai (Allah Ya yarda da su) su ne mafi falalar wannan al’umma
bayan Annabinta (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi); su ne
mafi xaukakar matsayi da girma a wajen Allah (Maxaukaki); kuma su
ne farkon waxanda aka yi wa alqawarin alhairi a lahira (2) qudurce
cewa sahabbai (Allah Ya yarda da su) na da falala mabambanta: a
jumlace, Abubakar shi ne a gaba, sai Umar, sai Uthman, sai Aliyu
(Allah Ya yarda da su); kuma ana gabatar da muhajirai, waxanda suka
yi hijira daga Makka zuwa Madina, a kan ansar, waxanda suka karvi
baquncin muhajirai a Madina, daga nan, sai waxanda suka halarci yaqin Badar da waxanda suka yi mubaya’ar Bai’atul Ridwān, sannan,
sai wanda duk nassi ya tabbatar da wata falala a kansa (3) qudurce
cewa sahabbai adalai ne gaba xayansu, kamar yadda Alqur’ani da
Sunnah da Ijma’ suka tabbatar (4) kamewa daga savanin da ya faru a
tsakaninsu, da fahimtar cewa yaqin da suka yi a tsakaninsu bisa ijtihadi ne (5) qudurce cewa haramun ne a zagi sahabbai ko a soki mutuncinsu
ko a yi ishara zuwa ga abin da zai rage matsayinsu ko ya tauye
darajarsu da xaukakarsu, da qudurce cewa ba kowa ne ya ke sukar
sahabbai ko ya aibanta su ko ya zage su ba, face zindiqi, munafiki,
kuma abin tuhuma a cikin Musulunci. 130
Haqiqanin Ahlul Bait (mutanen gidan Manzon Allah – tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) su ne matansa na aure (Allah Ya
yarda da su). Amma `ya`yansa, da dangin mahaifinsa, da `ya`yan
73
wannan addini, da gwagwarmayarsu, da qarfin imaninsu,
da kai-kawon da suka yi wajen taimakon addinin Allah,
na da tasiri sosai wajen samar da matasa masu kishin
addini, waxanda za su wakilci musulmi a ko’ina, kuma
su amsa sunan Ahlus-Sunnah tsantsa.
7. Ciyar da `ya`yansu yadda ya kamata, kuma a ciyar da su
halal, ba haram ba.131
Sakacin da waxansu iyaye ke yi
dangin mahaifinsa sun shiga cikin lafazin. Ke nan, Ahlul Bait na
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) su ne
waxanda sadaka/zakka ta haramta a gare su; wato: matansa da
zurriyarsa da kowane musulmi, namiji da mace, daga tsatson Abdul Muxxalib, wato, Banu Hāshim ibn Abdi Manāf, da kuma `yantattun
bayin Banu Hāshim waxanda suka musulunta.
Aqidar Ahlus-Sunnah dangane da Ahlul Bait ta qunshi: (1) qudurce
wajibcin son su, da yabo a gare su, da ajiye kowannensu a matsayin da
ya cancanta, bisa adalci (2) qudurce fifikon daraja a tsakaninsu,
gwargwadon yadda nassosi suka tabbatar (3) son Ahlul Bait gwargwadon matsayin kowannensu: Ahlus-Sunnah na son sahabbai
daga cikin Ahlul Bait saboda imaninsu, da taqawarsu, da
sahabbantakarsu ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi), da kusancinsu da shi; kuma suna son waxanda ba sahabbai ne
ba saboda imaninsu, da taqawarsu, da kusancinsu ga Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (4) qudurce wajibcin
girmama su, da kiyaye wasiyyar da Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya yi game da mutunta su, da martaba su,
da kiyaye haqqoqinsu, da shigar da su a cikin salati (5) qudurce cewa
za a iya samun Ahlul Bait a kowane lokaci, matuqar an tabbatar da
haka ta sahihiyar hanya. 131
Musulunci ya kwaxaitar da neman na kai ta hanyar halal domin
mutum ya xauki nauyin kansa da iyalinsa, da sadar da zumunci, da yin
sadaka, da kuma taimakon al’umma. Musulunci ya shar’anta (i) saye da
sayarwa da duk abin da zai iya taimaka wa kasuwanci (ii) sana’o’in
hannu, kamar noma da saqa da qira da jima da gini da sassaqa, da
sauransu (iii) leburanci a qarqashin hukuma ko waninta.
Kasancewar Allah (Mai girma da xaukaka) Ya umurci muminai da
cin halal kamar yadda ya umurci Manzanni [Mu’uminun, 23:51;
Baqarah, 2:172], wajibi ne kowane Musulmi ya tabbatar da cewa duk
hanyar da ya xauka ta neman abin rayuwa bai faxa cikin abin da
74
dangane da abincin iyalinsu ba shi da gurbi a cikin
Shari’ar Musulunci. Haka kuma, nuna halin ko in kula da
waxansu ke yi dangane da irin abin da za su kawo wa
iyalinsu (na halal ko haram), shi ma akwai haxari sosai.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Ya ishi mutum zunubi (a wajen Allah) ya
tozartar da waxanda ciyarwarsu ta ke (wajibi ne) a
kansa.‛132
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Duk wata tsoka (a
jikin mutum) da ta tsiro ta (hanyar cin) haram, wuta ce ta
fi cancantar ta qone wurin (a lahira).‛ A wani lafazin:
‚Duk jikin da ya tsiro ta (hanyar cin) haram, wuta ce ta fi
dacewa (ta qona wurin a lahira).‛133
8. Yin adalci a tsakanin `ya`ya (maza da mata) a wajen
kyauta. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya ce: ‚Ku yi adalci a tsakanin `ya`yanku
cikin (abubuwan da za ku ba su na) kyauta, kamar yadda
ku ke son su yi adalci a tsakaninku (mahaifi da
Shari’a ta hana ba. Misali, a cikin leburanci, haramun ne Musulmi ya yi
aiki a wajen da a ke qera kayan kixa ko a ke sarrafa giya da sauran
abubuwan da ke sanya maye, ko wajen da a ke sana’anta taba sigari; da
wuraren da aka tanada don zinace-zinace ko kuma wajen da a ke yin
mu’amala da riba a galibi. A wajen sana’o’in hannu, an haramta sana’ar
sassaqa gumaka; ko xaukar hoton abubuwa masu rai, ba tare da larura
ba; ko taimakawa wajen samar da wuraren da za a yi fasadi da masha’a.
A vangaren kasuwanci da saye da sayarwa, Musulunci ya hana duk
wani kasuwancin da ya qunshi cutarwa da yaudara ( ) da ruxi
ko rashin tabbas mai yawa ( ) ko rashin sanin haqiqanin ko adadin
abin da za a qulla ciniki a kansa ( ). Haka kuma, an rahamta hada-
hadar da ta qunshi giya da caca da mushe da alade da gunki da kare da
jini da kyanwa da hoto da kayan kixa, saboda haramta aininsu da aka
yi, kamar yadda aka haramta mu’amalar da ta qunshi riba. 132
Ahmad, Muslim da Abu Dāwud 133
Ahmad, Ibn Hibbān, ad-Dārimī da al-Baihaqī: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #4519]
75
mahaifiya) cikin biyayya da tausasawa (da za su yi a gare ku).‛
134 Haka kuma, an-Nu’umān ibn Bashīr (Allah
Ya yarda da shi) ya ce: Babana ya tafi da ni wajen
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: Na ba wannan xa nawa kyautar wani bawa da
na ke da shi (kuma ina son ka zama shaida a kan haka).
Sai Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Ka yi wa duk `ya`yanka irin wannan
kyautar?‛ Ya ce: ‘a’a’. (Sai Annabi) Ya ce: ‚Ku ji tsoron
Allah, kuma ku yi adalci a tsakanin `ya`yanku.‛ Sai
babana ya qwace kyautar da ya ba ni.135
A wata ruwayar,
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Wannan bai halatta ba. Kuma ni ba na yin
shaida sai a kan (al’amari na) gaskiya.‛136
A cikin wata
ruwayar, ya ce: ‚Kada ka sanya ni yin shaida a kan
zalunci. Lallai haqqin `ya`yanka ne a kanka ka yi adalci
a tsakaninsu.‛137
Ibn al-Qayyim ya ce: ‚Magabata na qwarai (as-Salaf as-Sālih) sun kasance suna son yin
adalci a tsakanin `ya`yansu.‛138
Idan mutum ya ba xansa/`yarsa kyautar wani abu a
lokacin da ya/ta ke shi/ita kaxai, sannan daga baya, Allah
Ya ba shi qaruwar haihuwa, ba zai ba `ya`yan da aka
haifa daga baya irin wancan abu da ya ba na farko ba, ko
kuma ya ce zai qwace abin da ya ba da a can baya. Idan
yana son ya ba waxannan na yanzu, sai dai ya haxa
`ya`yansa gaba xayansu, ya yi masu kyautar. Haka
kuma, ba dole ne a daidaita su a wajen biyan buqatar
larura ba. Misali, idan yanayin wani daga cikin `ya`yan
yana buqatar abinci, ko kula da lafiya fiye da sauran, ba
134
Xabarāni: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #1046] 135
Bukhari da Muslim 136
Muslim 137
Ahmad: Sahīh 138
Tuhfah al-Maudūd, shafi na 155
76
za a ce dole a daidaita su wajen kashe masu kuxi ba.
Haka kuma, idan bambancin jinsi ya haifar da
bambancin buqata a tsakaninsu, babu laifi a yi wa wasu
daga cikinsu xawainiyar da ta zarce ta sauran. Misali,
xawainiyar `ya`ya mata a wajen tufafi da kayan ado ta
zarce ta maza saboda bambancin yanayinsu.
Haka nan, ya kamata iyaye su saba wa `ya`yansu son
juna, da fifita juna, a kowane lokaci. Idan aka ba xaya
daga cikinsu kyauta, ko kuma ya samo wani abu a wani
wuri, iyaye su nuna masa cewa wannan abu nasu ne su
duka; su umurce shi da ba `yan’uwansa wani abu daga
ciki. Idan qarami ya ga abin wasa a hannun babba, kuma
ya nuna yana buqata, iyaye su umurci babban ya ba
qaramin aro. Lallai ne iyaye su guji nuna wa `ya`ya
bambanci saboda yanayin zamantakewarsu da iyayensu
mata. Yin haka, zai haifar da gaba, da rashin jituwa a
tsakanin `ya`yan.
9. Iyaye su kiyayi yin mummunar addu’a ga `ya`ya, domin
hakan na da haxari babba. A maimakon mummunar
addu’a, kamata ya yi iyaye su dage wajen yin addu’ar
alhairi da neman shiriya ga `ya`ya. Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Kada ku
yi mummunar addu’a ga kanku, da `ya`yanku, da
dukiyarku; don gudun kada ku dace da lokacin da Allah
Ya ke amsa addu’a, ya zamanto an amsa maku.‛139
Haka
kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Kada ku yi wa kanku addu’a, sai ta
alhairi, domin mala’iku na faxin ‘amin’ ga abubuwan da
ku ke faxi…‛140
139
Muslim 140
Muslim
77
Ke nan, addu’ar neman shiriya, da albarka, da dacewa ya
kamata iyaye su yi wa `ya`yansu a kowane lokaci, ba wai
tsinuwa da la’ana, da faxin tir, da Allah wadai ba.
Kamata ya yi, idan `ya`ya sun yi kuskure, ko sun aikata
wani abu mara kyau, a nuna masu haxarin abin, da
rashin dacewarsa, sannan, a roqi Allah Ya shiryar da su.
Idan kuwa a ka yi masu tofin Allah tsine, kuma Allah Ya
amsa wannan addu’a, za su qara fanxarewa ne. Irin
wannan ne ke faruwa a gidaje da yawa, a wannan lokaci.
Sanannen abu ne cewa Allah Yana amsa addu’ar iyaye
(kyakkyawa ko mummuna) ga `ya`yansu. Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Addu’o’i guda uku ana amsa su (kai tsaye): addu’ar
wanda aka zalunta, da addu’ar matafiyi, da addu’ar
mahaifi (uwa ko uba) ga xansa.‛141
Wannan ya sa Annabawa da Manzanni suka riqa
kyakkyawar addu’a ga kansu da `ya`yansu, kamar yadda
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ba mu labari a cikin Alqur’ani. Misali, Annabi Ibrāhīm ya ce: ‚Kuma ka
nisanta ni, ni da `ya`yana daga bauta wa gumaka.‛142
Kuma ya ce: ‚Ya Ubangijina! Ka sanya ni mai tsayar da
salla. Kuma daga zuriyyata. Ya Ubangijinmu! Kuma Ka karvi addu’ata.‛
143 Haka kuma, Annabi Ibrāhīm da
Ismā’īl sun ce: ‚Ya Ubangijinmu! Ka sanya mu,
waxanda suka sallama (al’amari) gare Ka, kuma daga
zuriyyarmu (Ka sanya) al’umma mai sallamawa zuwa
gare Ka …‛144
Don haka, wajibi ne iyaye su nisanci yin
mummunar addu’a ga `ya`yansu.145
141
Ibn Mājah: Hasan 142
Ibrāhīm 14:35 143
Ibrāhīm 14:40 144
Baqarah 2:128 145
Kalmar addu’a ( ) ta zo da ma’anoni guda bakwai a cikin
Alqur’ani: (1) Bauta [Yunus, 10:106]; (2) Neman taimako [Baqarah,
78
2:23]; (3) Neman buqata [Ghāfir, 40:60]; (4) Kira [Isrā, 17:52]; (5)
Yabo [Isrā, 17:110]; (6) Magana [Yunus, 10:10]; (7) Tambaya [Baqara,
2:68]. A shar’ance, addu’a ibada ce, kuma alama ce ta bauta, wadda
bawa ke yi domin neman kulawar Allah, da qarin taimakonSa, da jawo
rahamarSa, da tunkuxe cuta da azaba, kuma bawa ya ke bayyanar da
tsananin buqata zuwa ga Allah, da neman taimakonSa saboda gajiyawa,
da rashin qarfi.
Addu’a na xaya daga cikin mafi girman ibada; kuma tana da alaqa
mai qarfi da tauhidi, da kuma aqida, domin tana daga cikin manya-
manyan hanyoyin inganta imani da havaka shi. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya kira addu’a da suna addini gaba xaya [Ghāfir, 40:65;
Ahmad da Abu Dāwud da Tirmidhi]; kuma ya bayyana cewa yin
addu’a ga wanin Allah na daga shirka [Jinn, 72:20]. Addu’a ita ce abu
mafi girma da karamci a wajen Allah [Ahmad da Tirmidhi]; kuma ita ce ibada mafi falala [Hākim]. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya yi umurni da yin addu’a, saboda tana amfani ga abin da ya sauka da wanda bai sauka ba [Hākim]. Allah Yana fushi da
duk wanda ya qi yin addu’a, saboda tunanin ya wadatu ga barin Allah [Ahmad da Tirmidhi da Ibn Mājah]; kuma qin yin addu’a, alama ce ta
gajiyawa, kasancewar babu mai barin addu’a sai malalaci [Ibn Hibbān].
Addu’a hanya ce ta samun haquri a cikin tafarkin Allah, da mayar
da al’amura zuwa gare Shi, da tawakkali, da nisantar kasala da
gajiyawa. Addu’a ibada ce mai sauqi, wadda a ke yinta a cikin dare da
rana, a kan tudu, a cikin teku, a sama, a halin tafiya da zaman gida, a
halin wadata da talauci, a halin lafiya da rashin lafiya, a bayyane da
asirce. Lazimtar addu’a na daga sababin xaukewar bala’i, da
tunkuxewar tavewa da rashin arziqi; kuma tsari ne da kariya daga
mahassada da sharrin maqiya. Addu’a na daga abubuwan alhairi,
waxanda ke kai wa ga mamaci; kuma ita ce makamin wanda ke da
rauni, da kuma wanda aka zalunta.
Addu’a na da ladubba da sharuxxa guda ashirin (20): (1) tabbatar da
cikakken tauhidi da kuma nisantar shirka (2) roqon abin da Shari’a ta
yarda da shi, da barin yin addu’a a kan abin da Shari’a ba ta yarda da
shi ba (3) qudurta cewa Allah ne kaxai Ya ke da ikon amsar addu’a, da
kawo amfani, da tunkuxe cuta (4) ikhlasi, da koyi da Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da nisantar bidi’a a cikin
addu’a (5) fuskantar Allah, da qanqan da kai, tare da bayyanar da
gajiyawa da kasawa (6) tabbatar da cewa abinci da abin sha da tufafi da
muhalli duk na halal ne (7) rashin qetare dokokin Allah ko cuxanyar
zunubi da savon Allah, kamar yanke zumunta da sava wa iyaye (8)
79
kada a roqi wani abu na savon Allah (9) rashin qosawa ko tunanin an
samu jinkiri wajen amsa addu’ar, ballantana ma a kai ga dainawa (10)
farawa da yabo ga Allah (Mai girma da xaukaka) da salati ga Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (11) sakankancewa
da qudurce za a amsa addu’ar, matuqar ta cika sharuxxa (12) yin
tawassuli da sunayen Allah mafi kyawu da siffofinSa mafi xaukaka ko
tawassuli da kyawawan ayyukan da aka yi saboda Allah ko tawassuli
da halin da a ke ciki na qasqanci ko talauci ko tsananin buqata (13)
zaven gajejjerun addu’o’i, waxanda ke da cikakkiyar ma’ana (14)
kammala addu’ar da wani suna daga cikin ingantatun sunayen Allah,
wanda ya dace da buqatar da a ke nema wajen Allah (15) xaga
hannuwa a wuraren da suka dace (16) yin alwalla, da kallon alqibla, da
yin kuka wajen addu’a (17) nacewa da maimaitawa sau uku, da kuma
rashin yanke qaunar cewa za a amsa addu’ar (18) asirtawa (19) faxin ‘amīn’ (20) fara yi wa kai addu’a kafin wani.
Yana daga ladubban addu’a a yi amfani da duk wani lokaci ko wuri
ko wani hali, waxanda nassosin Alqur’ani da Sunnah suka tabbatar da
cewa ana amsa addu’a. Daga cikin lokutan da a ke sa ran amsa addu’a,
akwai: ranar arfa; da lokacin ayyukan Hajji; da watan Ramadan,
musamman a cikin goman qarshe; da daren lailatul qadr; da ranar
Juma’a, daga lokacin da liman ya hau kan munbari zuwa lokacin da za
a kammala salla; da cikin dare, musamman kashi xaya bisa ukun
qarshe; da bayan fitowar alfijir; da bayan sallar la’asar a ranar Juma’a.
Daga cikin wuraren da a ke fatan amsa addu’a, akwai: masallaci,
musamman masallacin haramin makka da madina da masallacin qudus da quba; da al-multazām; da maqama Ibrāhīm; da arfa; da safa da
marwa; da mash’arul harām. Haka kuma, nassosi sun tabbatar da cewa
ana sa ran amsa addu’a a waxannan halaye: lokacin haxuwa da abokan
gaba; da lokacin saukan ruwan sama; da lokacin kiran salla; da tsakanin
kiran salla da iqama; da halin sujuda; da bayan sallar farilla; da lokacin
da a ke yin azumi; da lokacin buxa baki; da lokacin da aka zalunci
mutum; da addu’ar iyaye ga `ya`yansu; da lokacin da aka ji carar
zakara; da addu’a ga wanda ba ya nan; da addu’ar matafiyi, da wanda
ke cikin tsanani; da addu’a bayan an kammala alwalla; da addu’a a
lokacin da za a sha ruwan zamzam.
An hana yin abubuwa guda goma sha biyu (12) a cikin addu’a: (1)
nisantar yin addu’a gaba xaya (2) yin addu’a a lokacin talauci ko
tsanani, amma idan wadata ta samu, a watsar da yin addu’a (3) kasala
da nuna gajiya wajen addu’a (4) yin shisshigi ta fuskar iyakance adadi
ko wuri ko yanayi ko hali ko siffa, ba tare da ingantaccen nassi ba (5)
80
10. Nisantar da `ya`ya daga wuraren da a ke aikata zunubi
da nau’o’in savon Allah,146
da bidi’a,147
da sauran
yin mummunar addu’a ga kai ko ga iyali ko ga dukiya (6) addu’ar
savon Allah da yanke zumunci (7) qosawa, da kuma yin gaggawa game
da addu’a (8) jingina addu’a ko sanya wa addu’a sharaxi, kamar a ce:
‚Allah Ka gafarta mani idan Ka so‛ (9) gaggauto da uquba a nan
duniya, kamar a ce: ‚Ya Allah! Azabar da Ka yi nufin yin mani a
lahira, Ka yi mani a nan duniya domin in huta‛ (10) quntata addu’a, da
iyakance ta, ba tare da wani sahihin nassi ba (11) amfani da bayan
hannuwa wajen roqon Allah (12) canza addu’a mai iyakantaccen lafazi. Duba littafin Tashīhud Du’ā na Bakar Abdullah Abu Zaid, da Ad-Du’ā wa Manzilatuhu minal Aqīdatil Islāmiyyah na Jilān Al-‘Arūsi, da
Shurūxul Ibādah wa Mawāni’ul Ijābah na Sa’īd ibn Wahf Al-
Qahaxāni, da Kitābud Du’ā na Husain Al-Awāyishah, da Du’ā: the Weapon of the Believer na Abu Ammār Yāsir Qādi, domin samun
cikakken bayani game da addu’a. 146
Kalmar zunubi ta zo da sigogi, da kuma ma’anoni masu yawan
gaske a cikin Alqur’ani. Haka kuma, kalmomin da sigogin sun
maimaitu a wurare da yawa. Misali, kalmar zanb – savawa, ta zo sau
talatin da biyar (35); ma’asiya – tsaurin kai, da fita daga umurnin Allah,
da qetare iyakokin bauta, ta zo sau talatin da uku (33); Ithm – laifi, sau
arba’in da takwas (48); sayyi’ah – mummunar aiki, sau xari da sittin da biyar (165); Jurm – laifi, sau sittin da xaya (61); Khaxī’ah – kuskure ko
babban zunubi, sau ashirin da biyu (22); Fisq – fita daga hanyar xa’a, sau hamsin da uku (53); Fasād – fita daga madaidaicin yanayi, da yin
varna, sau hamsin (50); Munkar – abin qi, sau goma sha shida (16); Fujūr – keta suturar kunya da halin girma da addini, sau shida (6);
Fāhishah – mummunar magana da ayyukan da ba su da kyau, sau
ashirin da huxu (24); Lamam – kusantar zunubi, sau xaya (1); da Wizr – babban sharri ko aibi, sau ashirin da shida (26).
Zunubi ya kasu gida biyu: babba da qarami. Babban zunubi shi ne
duk wani zunubi ko savon Allah da aka samu nassin da ya nuna
tsananin haramcinsa da haxarin aikata shi; ko dai ta hanyar bayyana
la’ana ko fushi a kan wanda ya aikata, ko narkon azaba ko shiga wuta a
lahira, ko kuma haddi a duniya. Daga cikin manyan zunubai akwai:
shirka, da sihiri, da kisan kai, da barin salla, da hana zakka, da sava wa
iyaye, da zina, da luwaxi, da cin riba, da shan giya, da cin dukiyar
maraya, da girman kai, da taqama, da giba, da annamimanci, da jiji da
81
kai, da shaidar zur, da sata, da rantsuwa a kan qarya, da qazafi, da fashi
da makami, da hana wa mutane aminci a kan hanya, da kashe rai ba da
haqqin Shari’ah ba, da yin hukunci da savanin abin da Allah Ya saukar,
da rashin damuwa game da varna ko fasiqancin da matar aure ke yi, da
kamanceceniya da maza/mata, da ha’inci, da rashin tsarkaka daga
fitsari.
Qananan zunubai su ne waxanda ba su shiga cikin manyan zunubai
ba. Irin wannan zunubi ya haxa da qin amsa gayyatar walima ba tare da
uzuri ba, da qin amsa sallama, da qin gaishe da wanda ya ce ‘Alhamdu Lillah’ bayan ya yi atishawa. Qananan zunubai na komawa manya idan
aka nace ana aikatawa, kuma aka riqa yin farin ciki saboda an aikata,
musamman idan ya zamanto mai aikatawar na daga cikin mutanen da a
ke koyi da su.
Ana sava wa Allah, a aikata zunubi ne saboda jahilci ko bin son
zuciya ko mummunar xabi’a ko rashin imani da lahira. Yawancin
savon Allah na kasancewa ne ta hanyar idanu, da harshe, da hankali, da
gavuvva.
Zunubi da savon Allah na da shu’umanci mai yawa ga wanda ke
aikatawa: yana haifar da baqar zuciya, da la’ana daga zukatan
muminai, da baqin ciki, da hana albarkar ilmi, da hana albarkar arziqi,
da kaxaici a cikin zuciya, da qyama a cikin mutane, da tsanani a cikin
al’amura, da duhun zuciya, da duhun qabari, da raunin jiki, da rashin
albarka a cikin rayuwa, da dabaibayin shaixanun aljannu, da qasqanci
da wulaqanci, da qasqanci a wajen Allah, da lalacewar hankali da
tunani, da jawo wa zuciya karkata da rashin lafiya da tsatsa da
bushewa, da rashin samun addu’ar Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) da mala’iku, da kuma gushewar ni’ima.
Bayan wannan, savon Allah na haifar wa al’umma yawan cututtuka da
annoba, da rashin aminci, da qarancin ruwan sama ko kuma ruwa mai
yawan gaske wanda zai yi masu varna, da bayyanar girgizar qasa da
yaqe-yaqe, da qasqanci, da ci baya. 147
Imam Shāxibi ya fassara bidi’a da cewa: ‚Hanya ce da aka qago a
cikin addini, wadda ta yi kama da hanyar Shari’ah, kuma a ke binta bisa
irin niyyar da a ke bin hanyar Shari’ah‛. Wannan fassarar ta samu goyon bayan Ibn Rajab, da Ibn Hajar, da Az-Zarkashi, da Al-Haithumī,
da waxansu malamai masu yawa. A harshen larabci kuwa, bidi’a na
nufin duk wani abu sabo ko qagagge.
A Shar’ance, idan aka ce bidi’a, ana nufin ma’ana ta Shari’a, ba
ma’ana ta harshe ba, kasancewar Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) ya zo ne don tabbatar da Shari’ah, ba harshen
82
larabci ba. Bidi’a a cikin Musulunci haramun ne bisa nassin Alqur’ani
da Sunnah da Ijma’in sahabbai da Tabi’ai da sauran mutanen kirki.
Bidi’a na gudana ta hanyoyi guda biyar: (1) aqida, kamar qin yarda
da qaddara, da vata siffofin Allah ko tawilinsu; (2) zuciya, kamar
tsoron qabarin wane ko qaunar samun wani abu daga wani matacce; (3)
furuci, kamar zikirin bidi’a da `yan xariqa ke yi, da roqon matacce, da
neman agaji daga waxanda ke cikin qabari; (4) jiki, kamar durquso a
wajen gaisuwa, da sujuda ga wani waliyyi, da yin taron maulidi; (5)
dukiya, kamar kuxin da `yan Shi’ah ke ba limamansu da sunan
khumusi. Bidi’a na faruwa ne a cikin al’umma idan mutane suka jahilci yadda
za a fahimci addini; ko suka jahilci manufofin Shari’ah; ko suka
kyautata zato ga mujarradin tunaninsu, suka dogara ga hankali,
maimakon nassi; ko suka bi son zuciya; ko aka samu waxanda ke yin
magana a cikin addini ba tare da ilmi ba; ko suka jahilci Sunnah; ko
suka yi shisshigi da wuce qa’ida a cikin addini; ko suka bi mutashābihāt. Bidi’a za ta yaxu a cikin jama’a idan malamai suka yi
shiru; ko malamai suka yi aiki da bidi’ar; ko sarakuna suka qarfafa
mata gwiwa, suka ba ta goyon baya; ko mutane suka yi taqalidanci ga
malamai ko shugabanni, a cikin abubuwan da babu dalili a Shari’ah.
Bidi’a na da illoli masu yawa ga wanda ke aikatawa: (1) `yan bidi’a
na zargin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
da yin ha’inci wajen isar da saqo, shi ya sa ma su ke aikata abin da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya qi
bayyana wa al’ummarsa a bisa zarginsu; (2) suna cikin vata; (3) sun bar
hanyar Allah; (4) sun bijiro da kawunansu ga fitinar duniya da lahira;
(5) sun lalata ayyukansu; (6) sun bi son zuciya; (7) suna kawo rarraba a
cikin al’umma; (8) suna haifar da mutuwar Sunnar Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) a cikin al’umma.
`Yan bidi’a na da siffofi guda goma sha huxu (14): yawan savani a
cikin addini; watsi da gaskiya da bin son zuciya; tsarkake waxansu
mutane, da sunan waliyyai ko malamai, da yin shisshigi da wuce iyaka a cikin al’amarin shaihunnai da waliyyai; bin mutashābihāt; sava wa
sahihiyar Sunnah, ta hanyar amfani da mutashābihātul Qur’ān; qiyayya
da gaba ga masu riqo da hadisi; juya wa littafan salaf baya; rashin
komawa ga fahimtar salaf wajen yin aiki da Alqur’ani da Sunnah;
aibanta malaman Sunnah da kiransu da munanan suna; juyar da
gaskiya; alfahari da taqama game da yawan mabiya; cuxanya gaskiya
da qarya; gandara qarya wajen qoqarin kare bidi’arsu; neman suna da
samun yarda a wajen shugabanni da mawadata.
83
wuraren da ba su dace ba, musamman, wuraren alfasha,
da batsa, da munanan maganganu, da kaxe-kaxe, da
raye-raye, da wasannin da ke shagaltarwa, kamar karta,
ludo, caca, da sunuka. Ibn al-Qayyim ya ce: ‚Haka nan
Bayan wannan, `yan bidi’a na da xabi’ar amfani da shubuhohin
qarya wajen ruxar da mabiyansu da sauran jahilai, ta yadda ba za su
fahimci Sunnah ba. Misali, a Nijeriya, ana cewa, ‘Ahlus-Sunnah (`yan
Izala/Salafiyya) ba su yin zikiri da salati, kuma ba su son Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).’ Ana faxin irin wannan
maganar ce, don kada a gane kurakuran da ke cikin waxansu bidi’o’in
da a ke yi, bisa da’awar son Allah (Maxaukaki) da ManzonSa (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi). Manufar ita ce a tsoratar da
mutane, kuma a nisantar da mabiya daga fahimtar Sunnah, da kuma
riqo da Alqur’ani da Sunnah bisa fahimtar magabata na qwarai.
Sanannen abu ne cewa idan aka ce `yan Izala na yin salatin Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) irin wanda ya zo a
cikin ingantattun hadisai, amma ba su yin salatul fatihi, wadda aka ce
Allah (Maxaukaki) Ya yi wa Muhammadul Bakari wahayinta, kuma
wai karanta salatul fatihi sau xaya dai dai ya ke da saukar Alqur’ani sau
dubu shida, babu wani mai hankali da zai yi qiyayya da `yan Izala, ko
kuma ya yarda cewa `yan Izala ba su yin salati. Haka kuma, idan aka ce
`yan Izala ba su yin zikirin wazifar tijjaniya ko qadiriyya ko
naqashabandiyya ko shaziliyya, kuma ba su yin zikirin rawa ko zikirin
dukan qirji da kaxa ganga, amma suna yin duk wani nau’in zikiri da ya
zo a cikin Alqur’ani ko ingantaccen hadisi, mabiya ba za su qullaci
`yan Izala da gaba ba, ko kuma su yarda cewa ba su yin zikiri. Dangane
da son Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
kuwa, an qi fitowa valo-valo a bayyana wa muridai cewa rashin yin
maulidi ne (wanda aka qago bayan shekara xari shida da wafatin
Manzon Allah – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi –) ya sa
aka ce `yan Izala ba su son Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi), ba wai domin ba su yin masa biyayya da xa’a, ko
kuma koyi da shi ba. Mene ne dalilin da yasa a ke voye wa muridai
gaskiyar al’amari? Wajibi ne iyaye su tabbatar da cewa `ya`yansu sun bi Sunnah sak,
kuma su nema wa `ya`yansu rigakafin bidi’a ta hanyar (1) riqo da
Alqur’ani da Sunnah (2) xabbaqa Sunnah a cikin rayuwa gaba xaya (3)
yin da’awah (4) rushe dalilan bidi’a da shubuhohin `yan bidi’a (5)
wadatuwa da fahimtar magabata na qwarai.
84
ma, wajibi ne a nisantar da yaron da ya fara hankali daga
wuraren wasanni na varna, da kixe-kixe, da sauraren
alfasha da bidi’a da munanan maganganu. Domin kuwa,
idan ya saba da waxannan abubuwa tun yana yaro, da
wuya ya barsu bayan ya girma, kuma iyaye za su wahala
matuqar gaske kafin su raba shi da su.‛148
Daga cikin wuraren da ya kamata a nisantar da `ya`ya
daga gare su, akwai wuraren bikin kirsimati (christmas),
kasancewar laifi ne yin tarayya ko taimakawa ko ba da
haxin kai, ta kowace irin hanya, wajen wannan biki. A
da’awar kirista, bikin kirsimati biki ne na tunawa da ranar haihuwar Annabi Isā (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi). Annabi Isā (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi), a irin qaryarsu da kafircinsu, wai xan
Allah ne, ko kuma ma shi Allah ne. To yanzu Musulmi
na gaskiya zai yarda `ya`yansa su yi murnar zagayowar
ranar haihuwar Allah ko xan Allah? Sanannen abu ne,
hatta a wajen kiristoci da yawa, cewa babu wani dalili ko
bayani sahihi da ya tabbatar da cewa haihuwar Annabi Isā (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ta
kasance ne a wannan rana ta 25 ga Disamba, da a ke yin
wannan biki. Bai kamata Musulmi ya bar `ya`yansa su
taya kirista murna, ko su kai yawon ziyara, ko su ba da
kyauta gare su ko karvar wani abu daga gare su, a
wannan rana ba. Yin haka, girmamawa ce ga shirkar da
su ke yi da Allah, kuma taimakawa ce a gare su cikin
kafircinsu.149
Ibnul Qayyim ya bayyana cewa yin
gaisuwar taya kirista murnar kirsimati ya fi tsananin
muni a wajen Allah fiye da gaisuwar taya murna ga
wanda ya sha giya ko ya yi kisan kai ko ya yi zina. Ya
qara da cewa, ‘wanda duk ya yi gaisuwar taya murna ga 148
Tuhfah al-Maudūd, shafi na 162 149
Ibn Taimiyyah, Majmū’ al-Fatāwā (Maktabah Ibn Taimiyyah),
25/332
85
mai savon Allah ko wanda ke aikata bidi’a ko aikin
kafirci, to, haqiqa, ya bijiro wa fushin Allah’.150
Haka kuma, ya kamata a nisantar da `ya`ya daga xabi’ar
nan ta bikin murnar zagayowar ranar haihuwa (birthday).
Wannan biki an samo shi ne daga waxanda ba Musulmi
ba. Malamai sun yi rubuce-rubuce da dama, kuma sun ba
da fatawoyi iri-iri dangane da wannan mas’ala.
Dukkansu sun yi ittifaqi a kan rashin dacewar wannan
biki, musamman da ya ke ya qunshi rashin fahimtar
manufar rayuwa a Musulunci, kuma ya qunshi
almubazzarancin dukiya, da koyi da xabi’un kafirai, da
vata lokaci a banza.151
Yana daga wuraren da ya kamata a nisantar da `ya`ya
daga gare su, wuraren da a ke yin bikin maulidi,
kasancewar maulidin da mutane ke yi a cikin watan
Rabi’ul Awwal, da sunan tunawa da haihuwar Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), a
kowace shekara, ba shi da asali a cikin Alqur’ani da
Sunnah, da ayyukan magabata na qwarai, kuma da yawa
daga manyan malamai magabata sun tabbatar da cewa
bidi’a ce da aka qago a cikin qarni na bakwai, wato
bayan hijira na da shekara fiye da xari shida.152
Wannan
150
Ibnul Qayyim, Ahkāmu Ahliz Zimmah, (Dārul Hadīth, Al-Qāhirah,
2003), shafi na, 154 151
Umm Muhammad, The Observance of Mawlid an-Nabawi and other Birthdays, (Abul-Qāsim Publishing House, Jeddah, Saudi Arabia,
1994), shafi na 41-50 152
Akwai bidi’o’i dabam daban waxanda a ke yi a cikin shekara. Mafi
shahara daga cikinsu su ne:
Al-Muharram: (1) bidi’ar baqin ciki, da marin fuska, da kekketa
tufafi, da zagin sahabbai (Allah Ya yarda da su) da yin qazafi ga A’isha
(Allah Ya yarda da ita), da ihu da kururuwar da zindiqai, maqiya
addinin Musulunci ke yi, a ranar Ashura (goma ga watan Muharram),
da sunan tunawa da ranar karbala, wato, ranar da Sayyidina Husain ibn
86
ya sa ba a samu bayani a kan falalar maulidi ko
Abi Xālib (Allah Ya yarda da shi) ya yi shahada; (2) bidi’ar cika-ciki
da maqiyan Ahlul Bait suka qago don qalubalantar zindiqan da ke yin
baqin ciki, kuma waxansu jahilai da masu qarancin fahimtar addini
suka qaqaba wa kawunansu; (3) bidi’ar taron murnar shiga sabuwar
shekarar Musulunci.
Safar: bidi’ar canfi, da kuma da’awar cewa akwai ranakun da ba a
yin tafiya ko xaurin aure ko aikata waxansu abubuwa a cikinsu.
Rabi’ul Awwal: bidi’ar maulidi, da sunan tunawa da ranar da aka
haifi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi). Al-Fākihāni, da Ibnul Hāj, da Ash-Shāxibi, da Ibn Taimiyyah, da Ibn
Kathīr, da As-Sakkhāwi, da Ibn Hajar, da Ibnul Haffar, da An-
Nafarāwi, da As-Sāwi, sun tabbatar da cewa taron maulidi bidi’a ne.
Rajab: bidi’ar keve watan Rajab da yin azumi ko tsayuwar dare, don
neman samun lada da falala na musamman. Ibn Dihyah, a cikin littafin Adā’u mā wajab min Bayāni wad’il Waddā’īn fi Rajab, da Ibn Hajar, a
cikin Tabyīnul ‘Ajab bimā warad fi Fadli Rajab, sun tabbatar da cewa
duk hadisan da aka ruwaito dangane da falalar yin azumi ko qiyamul laili a cikin watan Rajab masu tsananin rauni ne, ko kuma hadisan qarya. Haka kuma, Al-Harwi, da Ibn Kathīr, da Al-Fairūza Ābādi, duk
sun tabbatar da rashin ingancin hadisan. Wannan ya sa, Umar ibnul Khaxxāb (Allah Ya yarda da shi) ya kasance yana bugun waxanda ke
yin azumin watan Rajab da qwarangamar da ke hannunsa, kuma Ibn Umar da Ibn Abbās (Allah Ya yarda da su) sun kasance suna hana
mutane yin wannan azumi, saboda mutanen jahiliyya ne suka kasance
suna yin azumin. Sha’abān: bidi’ar raya daren sha biyar ga wannan wata.
Ramadān: bidi’ar yin sallar tarawihi bayan sallar magriba, maimakon
bayan sallar isha’, da `yan Shi’a ke yi, don ganin sun sava wa sauran
musulmi na duniya. Shawwāl: bidi’ar canfi game da yin aure.
Dhul Hijjah: bidi’ar Yaumu Ghadīr Khum (ranar sha takwas ga
wata) da `yan Shi’a ke yi, bisa da’awar cewa a wannan rana ce Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ayyana Aliyyu ibn Abi Xālib (Allah Ya yarda da shi) a matsayin wanda zai zamanto
halifar musulmi, bayan shi. Duk da cewa wannan magana qarya ce
tsagwaro, amma `yan Shi’a na amfani da ita wajen kafirta Abubakar da
Umar da Uthman da A’isha da sauran sahabbai (Allah Ya yarda da su),
saboda wai sun ci amanar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi), suka ba Abubakar halifanci, maimakon Aliyyu.
87
shar’ancinsa a cikin Alqur’ani ko wani littafi daga cikin
littafan hadisi da fiqihu, waxanda musulmi ke karantawa
a duniya ba. Maimakon haka, an samu manyan malamai,
musamman `yan mazhabar malikiyya, tun fiye da
shekara xari bakwai, sun qyamaci bidi’ar maulidi, kuma
sun tabbatar da cewa taron maulidi ba shi da asali a cikin
Alqur’ani da Hadisi da maganganun magabata na
qwarai. Daga cikin manyan malaman da suka soki bidi’ar maulidi tun tali-tali, akwai: Tājuddīn Umar ibn
Aliyyu Al-Lakhamī Al-Fākihāni Al-Māliki,153
da Abu
Ishāq Ash-Shāxibi Al-Māliki,154
da Ibnul Hāj Al-
Māliki,155
da Abu `Amr ibn Al-Alā,156
da Abu Abdillah
Muhammad Al-Mihdār,157
da Abu Zur’ah Al-Irāqi,158
da
Zahīruddīn Ja’afar At-Tazamnati,159
da Abu Abdillah Al-
Haffār Al-Māliki,160
da Abux Xayyib Muhammad
Shamsulhaq Al-Azīm Ābādi,161
da Bashīruddīn Al-
153
A cikin littafinsa Al-Maurid fi Amalil Maulid, ya bayyana cewa
maulidi bidi’a ce wadda `yan zaman kashe wando suka qago, kuma
sha’awar rai ce wadda masu son cin na banza ke ba muhimmanci. Ya
mutu a shekara ta 734 AH. 154
A cikin littafin Al-I’itisām da Fatāwal Imāmish Shāxibi, shafi na
203-204, ya tabbatar da bidi’ancin taron maulidi. Ya rasu a shekarar
Hijira 790 155
A cikin littafin Al-Madkhāl, 2/2-10. Ya rasu a shekarar 732 AH 156
Jalāluddīn As-Suyuxi ya naqalo maganarsa a cikin littafin Al-Hāwi lil Fatāwa, 1/190 157
A cikin littafin Al-Mi’iyārul Mu’urib,7/ 99-101 158
A cikin littafin Tanshīful Aazān 159
Duba Al-Mi’iyārul Mu’urib, 7/99 160
Duba Al-Mi’iyārul Mu’urib, 7/99 161
Duba littafin Ar-Raddul Qawiy alar Rufā’i wal Majhūl wabni Alawi wa Bayānu Akhxā’ihim fil Maulidin Nabawi na Hamud ibn Abdillah
At-Tuwaijiri, shafi na 235
88
Qanūji,162
da Abdussalām Khidir Ash-Shuqairi,163
da
Muhammad Ulaish Al-Māliki,164
da Rashīd Rida.165
Abin mamaki, duk waxannan malamai babu xan izala ko
bawahabiye, ballantana waxanda ke qoqarin kare bidi’ar
maulidi su ce maqiyan Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ne suka nuna rashin asalin
bidi’ar maulidi a cikin Musulunci. Hasali ma, malamai irinsu Ibnul Hāj da Ulaish da Al-Haffār masu bin hanyar
sufaye ne.166
Haka kuma, lallai ne iyaye su nisantar da `ya`yansu daga
wuraren da a ke kaxa mandiri ko a ke yin rawa da bugun
qirji da haniniya da hargowa a wajen zikiri, kasancewar
waxannan abubuwa ba su da asali cikin addinin Allah.
Babu shakka, yin haniniya da ihu, da shessheqa, da
kyakkyarma murya, da yin tafi da rawa a yayin da a ke
zikiri, ba shi daga cikin karantarwar Musulunci. Wajibi
ne a kan iyaye su tabbatar cewa `ya`yansu ba su je kallon
irin waxannan ayyukan bidi’a ba, waxanda mutane ke yi,
wai da sunan addini.167
162
Duba littafin Ar-Raddul Qawiy alar Rufā’i wal Majhūl wabni Alawi wa Bayānu Akhxā’ihim fil Maulidin Nabawi na Hamud ibn Abdillah
At-Tuwaijiri, shafi na 235 163
Karanta littafinsa As-Sunan wal Mubtadi’āt 164
A cikin littafin Fat-hul Aliyyil Māliki 165
A wurare da dama cikin Al-Manār, 9/96; 2/74-76; 17/111; 29/664-
668 166
Duba littafina Nau’o’in Ibada a cikin Watannin Musulunci da Bidi’o’in da a ke yi a kowane Wata. Allah Ya ba ni ikon kammala shi,
da kuma fitar da shi ga jama’a. 167
Babu wani malami daga cikin malaman Sunnah, tun daga zamanin
sahabban Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
zuwa yau, da ke ganin halaccin irin wannan mummunan aiki da `yan bidi’a ke yi, da sunan bautar Allah. Hasali ma, Imam Ax-Xurxūshi Al-
Māliki, wanda ya rasu a shekarar hijira 520, a cikin littafinsa Al-Hawādith wal Bida’u, na ganin cewa zindiqai, mutanen As-Sāmiri,
89
waxanda suka yi wa Annabi Musa (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) tawaye, su ne suka fara yin bauta ta hanyar kewaye xan
maraqi, suna rawa, suna tafi, suna layi, da sauransu. Wannan ya sa Al-Qurxubi, a cikin Al-Jāmi’u li Ahkāmil Qur’ān, da Ibnul Jauzi, a cikin
Talbīs Iblīs, da Ash-Shāxibi, a cikin Al-‘I’itisām, da Ibnus Salah, a
cikin Al-Fatāwā, da Ibn Taimiyyah, a cikin Majmū’ul Fatāwā da
Mas’alatus Sama’, da Ibnul Qayyim, a cikin Ighāthatul Lahfān da
Madārijus Sālikīn, da Ibnul Hāj, a cikin Al-Madkhal, da As-Sayyid
Mahmud Al-Alūsī, a cikin Rūhul Ma’āni, da Ibn Hajar Al-Haithumī, a
cikin Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’ Ālātis Samā’ suka nuna bidi’ancin yin
rawa ko layi ko rausaya ko tafi ko kixa ko ihu da haniniya wajen zikiri.
Da yawa daga malamai sun danganta yin tsuwwa da tafi wajen zikiri
ga mutanen jahiliyya, kuma suka danganta rangwaxa da jan sauti a wajen zikiri ga kirista [duba tafsirin Al-Alūsī, Rūhul Ma’āni, a
qarqashin faxin Allah ‚ ‛; da littafin
Risālatus Sama’ na Ibn Taimiyyah]; suka bayyana cewa yin tafi wajen
zikiri, kamanceceniya ce da mata, domin kuwa, mata ne kawai ke yin tafi idan larura ta auku a cikin salla [duba Talbīs Iblīs na Ibnul Jauzi, a
qarqashin ; da Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’
Aalātis Samā’ na Ibn Hajar Al-Haithumī]; suka bayyana cewa yin rawa
da rausaya ko layi da mommotsa jiki da sunan bauta a lokacin zikiri, varna ce babba [duba Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’ Aalātis Samā’ na Ibn
Hajar Al-Haithumī]; Izz ibn Abdis-Salām ya ce wanda ke yin tafi da
rawa a lokacin zikiri ‘xan daudu’ ne, kuma babu wanda ke yin haka, sai wawa ko jahili [duba Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’ Aalātis Samā’ na Ibn
Hajar Al-Haithumī]; Az-Zamakhshari ya ce, a addinance, layi da
rausayawa, addinin yahudawa ne wajen karanta littafin At-Taurah
[duba tafsirin Al-Kash-Shāf, a qarqashin faxin Allah ‚
‛]; Ax-Xurxūshi ya ce, asalin rawa da layi ko tafi ko
rausaya wajen ibada, addinin kafirai ne waxanda suka yi bautar xan
maraqi, kuma hanya ce ta sufaye wajen zikiri, kuma hakan ya qunshi zaman kashe wando da jahilci da vata [duba Al-Jāmi’ li Ahkāmil
Qur’ān na Al-Qurxubī, a qarqashin faxin Allah ‚
‛ a cikin suratu Xāha, 20:88; da Al-Madkhal na
Ibnul Hāj, juz’i na biyu; da Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’ Aalātis Samā’ na
Ibn Hajar Al-Haithumī]; Ash-Shāxibī ya bayyana cewa rawa da
rausayawa ko layi, da sufaye ke yi a wajen zikiri, bidi’a ce da ta sava
wa hanyar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
da sahabbai (Allah Ya yarda da su) da tabi’ai (Allah Ya jiqansu) da
90
11. Iyaye su riqa nema wa `ya`ya tsari da kariya tare da
nisantar da su daga duk wani abu mai cutarwa, kamar
shaixanun aljannu da mutane. Hakan zai samu ne ta
hanyar yin masu rigakafi irin na Musulunci da ya qunshi
addu’o’i, da nisantar waxansu abubuwa ko aikata
waxansu abubuwa.168
Manzon Allah (tsira da amincin
sauran magabata na qwarai [duba littafin Al-I’itisām]; Abux-Xayyib
Ax-Xabarī ya ce, waxanda ke yin kixa wajen zikiri sun sava wa
jama’ar musulmi, domin sun mai da waqa a matsayin addini da xa’a,
kuma suna ganin dacewar bayyana wannan abu a cikin masallaci da wuraren qaburbura [duba Risālatux Xabarī]; Ibn Salāh ya ce waxanda
ke yin zikiri da kixa sun yi wa Allah (Maxaukaki) qarya, kuma sun sava wa ijma’in musulmi [duba Fatāwā Ibn Salāh]. 168
Kashi na 13 (4) na dokar haqqoqin yara, Child’s Right Act, wadda
tsohon shugaban qasar Nijeriya, Obasanjo ya rattaba wa hannu a ranar
31 ga watan Yuli, 2003, ya wajabta wa iyayen kowane yaron da bai kai
shekara biyu ba, cewa su tabbatar an yi masa allurar rigakafi. Idan ba
haka ba, akwai tara ta kuxi da za a yi masu, wadda ba ta wuce N5000
ba, a karo na farko. A karo na biyu, za a iya yanke masu hukuncin
xaurin da bai wuce wata xaya ba, sannan, a tursasa su yin rigakafin.
Wannan sashi na dokar yara, na qoqarin kore dukkan xari-xarin da
musulmi ke yi game da allurar rigakafin da a ke yi wa yara, musamman
rigakafin cutar shan inna (polio). Binciken da aka gudanar a kan
maganin rigakafin shan inna da a ke xiga wa yara a wannan qasa, wato, Oral Polio Vaccination (OPV), ya nuna cewa, an gurvata maganin
rigakafin da qwayoyin hana xaukar ciki, da waxanda ke kashe
qwayayen halitta. Wannan ta’addanci na daga cikin shirin kisan qare
dangi da qasashen yammacin Turai suka daxe suna shiryawa a kan
musulmin Nijeriya. Da yawa daga manyan likitoci, da qwararru a
harkar harhaxa magunguna, da masana tattalin arziqi da gudanarwar
mulki da siyasa, na qasashen duniya, sun tabbatar da makircin da
qasashen yammacin duniya ke qullawa ga qasashen da ke tasowa,
musamman Nijeriya.
Waxanda ba su fahimci siyasar da ke cikin rigakafin polio ba, gani
suke, neman tayar da zaune tsaye a ke yi, duk lokacin da aka soki tsarin
rigakafi. Haka kuma, wasu daga cikin malamai, sukan yi qoqarin
danganta jahilci ko tsattsaurar ra’ayi ga waxanda ke qorafi a kan
91
maganin rigakafin polio, duk da cewa malaman ne ba su fahimci
al’amarin ba yadda ya dace.
Sanannen abu ne cewa, babu wanda ke jayayya game da halaccin
yin rigakafi a Musulunci, ta hanyar karanta addu’o’i, ko yin zikirori, ko
cin dabinon ajwah, ko kuma xaukar waxansu matakan da Shari’ah ta
yarda da su don tsare kai, da kuma samun kariya daga cututtuka. Kace-
nace a tsakanin mutanen Nijeriya ya auku ne a dalilin matsaloli da
illolin da aka gano game da maganin rigakafin. Matsaloli da illolin da
ke tattare da maganin rigakafin sun dace da makircin qasar Amurka da
`yan kanzaginta, da kuma mummunar kaidinsu ga Musulunci da
musulmi, da sauran baqar fata, ko da ba musulmi ba ne.
Tun da aka fara kace-nace dangane da rigakafin polio, akwai wanda
ya tabbatar da rashin sahihancin sakamakon binciken da aka gudanar a
wannan qasa, wanda ya tabbatar da cewa akwai illoli a cikin maganin?
Ina sakamakon binciken da Farfesa Haruna Kaita ya gudanar? Ina sakamakon binciken da Jamā’atu Nasril Islām ta sa aka gudanar? Ina
sakamakon binciken da ma’aikatar lafiya ta tarayya tare da haxin
gwiwar hukumar NAFDAC ta gudanar? Sakamakon binciken da
waxannan vangarori guda uku suka gudanar, ya tabbatar da cewa, an
gurvata maganin rigakafin polio da a ke xiga wa yara, kuma an shigar
da waxansu abubuwa masu haxarin gaske a cikinsa. Mene ne ya hana a
bayyana sakamakon binciken ga `yan Nijeriya? Me ya sa a ke ci gaba
da amfani da shi, duk da cewa an hana xiga wa `ya`yan Amurkawa, a
jihar Lagos? Kuma ko da ya ke daga baya, hukumar Nijeriya ta yi
da’awar magance matsalar gurvacewar maganin, har ma aka tursasa wa
jihohin Kano da Zamfara amfani da shi, wane tabbaci Musulmin
Nijeriya ke da shi game da sahihancin sabon maganin rigakafin? Idan
da gaske ne, mene ne ya hana a nemi su Farfesa Haruna Kaita domin a
sake yin gwaji a kan sabon maganin? Wannan kawai ya isa ya haifar
wa mafi yawan Musulmin Nijeriya xari-xari game da ingancin
rigakafin polio.
Ban da wannan, mene ne yasa qasar Amurka ta yi barazanar qaqaba
takunkumi a kan Nijeriya idan ba a yi rigakafi a jihohin Zamfara da
Kano ba, alhali cibiyar hana yaxuwar cututtuka ta Amurka (Centre for Disease Control), ta ba da shawarar dakatar da xiga maganin rigakafin
polio ga `ya`yan Amurkawa, a ranar 1 ga watan Janairu, 2000, saboda
an gano cewa maganin na haddasa cutar shan inna? Mene ne dalilin
tursasa qasar Saudi Arabia ta yi barazanar hana musulmin Nijeriya
zuwa aikin Hajji, idan ba a yi polio ba, tare da cewa, cutar, ba ta kama
manya, sai dai qananan yara?
92
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Idan dare ya yi (wato
rana ta faxa) ku tsare `ya`yanku (kada ku barsu su fita
gida), domin a wannan lokaci shaixanu (daga cikin
Ina hikimar kururuta al’amarin rigakafin polio, da qungiyar lafiya ta
duniya (World Health Organisation) ke yi, duk da cewa, a jerin gwanon
cututtuka masu saurin kisa, polio ba shi daga cikin cututtuka guda
goma, mafi haxari; amma a xaya vangaren, qungiyar, ba ta kuzuzuta
cutar qyanda (measles), da zazzavin cizon sauro (malaria) ko zazzavi
mai sanya tsananin zafin jiki (typhoid), duk da cewa sun addabi `yan
Nijeriya, kuma suna sanadiyyar mutuwar dubban mutane, a kowace
shekara? Wace hovvasa qungiyar lafiya ta duniya ke yi, wajen kawar
da waxannan cututtukan da ke sahun farko a jerin cututtuka masu kisa?
Ashe ba a wannan qasar ba ce, jaridar Daily Trust, ta ranar 7 ga
Oktoba, 2003, ta bayyana cewa, kusan kashi arba’in bisa xari (40%) na
xaruruwan miliyoyin `yan Afrikan da ke fama da matsalar zazzavin
cizon sauro, `yan Nijeriya ne? Mene ne gwabnatin Nijeriya, da
hukumomin qasashen qetare, da qungiyoyin ba da agaji suka yi, a kan
wannan? A yayin da a ke xiga maganin rigakafin cutar polio kyauta,
duk da yawan kuxin da a ke kashewa, da qyar `yan Nijeriya ke iya
sayen maganin zazzavin cizon sauro, da maganin cutar qyanda! Abin
tambaya a nan shi ne: mene ne yasa gwabnati ke kashe wa kowane
yaron da aka xiga wa maganin rigakafin polio fiye da N300, amma ba
ta iya samar da maganin zazzavin cizon sauro da maganin cutar qyanda
kyauta duk da cewa kuxin da a ke buqata don yin hakan bai taka kara
ya karya ba? Haka kuma, mene ne yasa a ke bi gida-gida domin yin
rigakafin cutar polio har sau huxu a shekara, ba tare da la’akari da
yaran da aka yi masu rigakafin, da waxanda ba a yi wa ba? Sau nawa
ya kamata a yi wa yaro rigakafin cutar shan inna a rayuwarsa? Sau
nawa ya kamata a yi wa yaro rigakafin polio a kowace shekara? Daga
shekara nawa ne ya kamata a daina yi wa yara allurar rigakafin polio?
Bayan wannan, ashe, ba qungiyar lafiya ta duniya ba ce, tare da
taimakon gwabnatin Amurka, ta sa aka qago qwayoyin cutar sida (HIV/AIDS), aka zuba qwayoyin a cikin maganin allurar rigakafin
ciwon agana, aka kai wa mutanen qasar Zaire, Zambia, Tanzania,
Uganda, Malawi, Rwanda, Brundi, Brazil, da Haiti ba, kamar yadda
jaridar The London Times, ta qasar Ingila, ta bayyana, a ranar Litinin,
11 ga Mayu, 1987, kuma Dr. William Doglas, wani qwararren likita, a
Amurka, ya tabbatar da hakan, a cikin mujallar Amurka, mai suna
Health Consciousness, ta watan Disamba, 1987? [Duba littafina
Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci don qarin bayani]
93
aljannu) ke warwatsuwa (don zuwa yawo). Idan aka
samu wani lokaci (bayan faxuwar rana), to ku sake
su…‛169
A wata ruwayar, Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Kada ku saki
dabbobinku da `ya`yanku (qanana) idan rana ta faxi, har
sai duhu ya shiga; domin shaixanu na yawo daga wannan
lokaci zuwa lokacin da duhu zai fara shiga.‛170
Haka
kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya kasance yana yi wa al-Hasan da al-Husain
addu’ar neman tsari, da kiyayewar Allah a gare su. Kuma ya kan ce, Kakanku (Annabi Ibrāhīm) ya kasance
yana nema wa Ismā’īl da Ishāq tsari da irin wannan
addu’ar da nake muku:
[Ina neman muku tsari da kalmomin Allah cikakku daga
dukkan shaixan da wata dabba (ko qwaro) mai dafi, da
kuma dukkan wani mai kambin baka, mai cutarwa]171
.
Haka kuma, yana da matuqar muhimmanci, iyaye su
koya wa `ya`yansu nau’o’in zikirin da a ke yi domin
samun kariyar Allah (Mai tsarki da xaukaka) daga
dukkan wani abu mai cutarwa, musamman bayan sallar
asuba da magriba, da lokacin barci, da lokacin fita gida,
da lokacin shiga bayi.172
169
Bukhari da Muslim 170
Muslim 171
Bukhari 172
Zikiri shi ne abin da ke gudana a kan harshe da zuciya, wanda ya
qunshi tasbihi da hailala da tahmidi, da yabo ga Allah (Maxaukaki), da
karanta Alqur’ani, da yin addu’a, da zartar da umurnin Allah, da tunani
a cikin ni’imominSa da halittarSa. Zikirin Allah igiya ce mai qarfi,
wadda ke qulla kyakkyawar alaqa a tsakanin bawa da Mahaliccinsa,
kuma ta ke sanya bawan Allah ya rayu a cikin kulawa da kariyar Allah,
ta yadda Allah zai tsai da shi a kan alhairi, kuma Ya tabbatar da shi a
kan hanya madaidaiciya.
94
Zikiri shi ne abin da ke yaye wa zukata baqqan ciki, kuma ya goge
zukata fyas. Zikiri shi ne buxaxxiyar qofar Allah (Maxaukaki) mafi
girma, wadda ke tsakanin Allah (Maxaukaki) da bawanSa, matuqar dai
bawa bai gafala ko ya rafkana ga barinta ba. Zikiri shi ne ruhin ayyuka;
idan bawa ya bar zikiri, zai zamanto kamar jiki ne da ba shi da ruhi.
Wannan yasa Allah (Maxaukaki) Ya umurci musulmi da su kasance
daga cikin waxanda ke yin zikirin Allah a cikin dare da rana, a zaune
da tsaye da kwance, a asirce da bayyane, a halin zaman gida da tafiya, a
ruwa ko a tudu, a halin rashin lafiya da lokacin qoshin lafiya.
Ibnul Qayyim ya bayyana fa’idodi da falalar zikiri har guda xari (100) a cikin littafinsa Al-Wābilus Sayyib, (Al-Maktabuth-Thaqāfi, Al-
Qāhirah, 2003), shafi na 41-93. Daga cikin falalar zikiri, akwai: (1)
zuciya na samun babban rabo da natsuwa a cikin duniya da lahira (2)
zikiri na daga mafificin xa’a, kuma yana daga mafi girman ayyukan
samun kusanci zuwa ga Allah (3) waxanda ke yin zikiri, su ne ke
amfana da ayoyin Allah, kuma su ne masu hankali da tunani (4) zikirin
Allah shi ne katangar qarfe da bawa ke tsare kansa da ita daga shaixan
(5) zikiri na daga dalilan samun xaukaka a duniya da lahira (6) zikiri na
daga dalilan da ke jawo arziqi a duniya da lahira ga xaixaikun mutane,
da kuma al’umma baki xaya (7) wanda ke yin zikiri, Allah Yana
ambatonsa a cikin mala’iku (8) dawwama a kan zikiri na wajabta wa
bawa samun aminci daga mantawa da Allah (9) yana kawo wa bawa
kiyayewa da kulawar Allah (10) zikiri alama ce ta kuvutar bawa daga
munafinci (11) zikiri yana yardar da Allah (12) yana gusar da baqin
ciki da damuwa da vacin rai daga zuciya (13) yana jawo wa zuciya
farin ciki da walwala da nishaxi da jin daxi (14) yana qarfafa zuciya da
gangar jiki (15) yana haskaka zuciya da fuska (16) yana jawo wa mai
yinsa kwarjini da girma (17) yana gadar wa bawa da soyayyar Allah
(18) yana kankare zunubi, ya saryar da laifi (19) yana gadar da lada mai
yawa (20) yana gusar da kaxaici (21) yana tserar da mutum daga azabar
Allah (22) dalili ne na saukar natsuwa da lulluvewar rahama da samun
kariya (23) yana shagaltar da harshe daga barin giba da gulma da qarya
da alfasha da tsogararo (24) yana daga mafi sauqin ibada (25) yana
daga cikin ibada mafi falala (26) wuraren da a ke yin zikiri, wurare ne
da mala’iku ke zuwa (27) yana sauqaqe abu mai wahala kuma ya
kawar da tsoro (28) yana maye gurbin taxawwu’in da ba a samu damar
yi ba (29) yana daga cikin nau’o’in ibada mafi karamci a wajen Allah
(30) yana gadar wa bawa xabi’ar mai da al’amura zuwa ga Allah.
Zikiri na da nau’o’i dabam daban. Nau’o’in zikiri sun haxa da: (1)
karatun Alqur’ani (2) zikirin da a ke yi da harshe, kamar tasbīh (
95
), tahlīl ( ), tahmīd ( ), takbīr ( ), hawqala (
), da istirjā ( ), da sauran nau’o’in zikirin da suka
tabbata a ckin Alqur’ani da Sunnah sahihiya (3) addu’a (4) istigfari (5)
tunani a cikin halittun Allah (6) ayyukan xa’a, kamar salla da azumi da
sadaka da ziyara da neman ilmi.
Zikiri na da lokuta iri biyu: sakakken lokaci ( ) da iyakantaccen
lokaci ( ). Duk wani zikirin da ba a iyakance masa lokaci ko wuri ko
adadi ko siffa ba, a cikin Alqur’ani da Sunnah, za a iya yinsa a ko’ina,
kuma a kowane lokaci ko yanayi ko siffa, in ban da abin da nassi sahihi
ya hana. Zikirin da aka qayyade shi da wani lokaci ko hali ko wuri ya
haxa da: zikirin safe (daga fitar alfijir zuwa kafin rana ta fito) da
yamma (bayan la’asar zuwa faxuwar rana), da lokacin barci, da bayan
farkawa daga barci, da shiga gida ko fita, da shiga masallaci ko fita, da
shiga ban xaki ko fitowa daga ban xaki, da lokacin rashin lafiya, da
lokacin baqin ciki ko damuwa, da lokacin aukuwar musiba, da halin
tafiya, da lokacin saukar ruwan sama, da bayan sallar farilla, da bayan
kammala alwalla.
Akwai kurakurai da dama da aka shigar cikin zikiri. Daga cikin
kurakuran akwai: (1) qayyade sakakken zikiri da wata siffa ko adadi ko
yanayi ko lokaci ko wuri, ko kuma rashin iyakance zikirin da nassi ya
qayyade (2) zikiri a cikin jam’i, alhali kuwa ba shi daga cikin Sunnah, kamar yadda Ibn Abi Shaibah ya ruwaito daga Umar ibnul Khaxxāb,
kuma Ad-Dārimi ya ruwaito daga Ibn Mas’ud (Allah Ya yarda da su)
cewa sun yi tsananin inkari ga waxanda ke yin zikiri cikin jam’i (3) yin
kixa da rawa da tafi da rausayawa ko layi wajen zikiri, kasancewar manyan malamai irin su Ax-Xurxūshi a cikin Al-Hawādith wal Bida’, da Al-Qurxubī, a cikin Al-Jāmi’u li Ahkāmil Qur’ān, da Ibnul Jauzī, a
cikin Talbīs Iblīs, da Ash-Shāxibī, a cikin Al-‘I’itisām, da Ibnus Salāh,
a cikin Al-Fatāwā, da Ibn Taimiyyah, a cikin Majmū’ul Fatāwā da
Mas’alatus Sama’, da Ibnul Qayyim, a cikin Ighāthatul Lahfān da
Madārijus Sālikīn, da Ibnul Hāj, a cikin Al-Madkhal, da As-Sayyid
Mahmud Al-Alusi, a cikin Rūhul Ma’āni, da Ibn Hajar Al-Haithumī, a
cikin Kaffur-Ra’a’ ‘Anistimā’i’ Aalātis Samā’ sun nuna haramcin yin
haka (4) xaga murya fiye da buqata, in ban da wajen kiran salla da iqama, da kabbarorin liman a cikin salla, da faxin ‘amīn’ a qarshe
fatiha ko a wajen addu’a, da faxin ‘sami’allahu liman hamidah’ ko
‘rabbana walakal hamd’, da karatun sallar da a ke bayyanawa, da
kabbarorin isarwa ga mamu idan akwai buqata, da sallamewa daga
salla, da yin sallama ko amsa sallama ga musulmi, da faxin ‘Alhamdu
96
Ke nan, wajibi ne iyaye su kula da `ya`yansu, kuma su
tsare su daga dukkan abubuwa masu cutarwa ko
firgitarwa, ta hanyar yin masu addu’a, da hana su zuwa
wuraren haxari. Ibn al-Qayyim ya ce: ‚Ya kamata a
nisantar da yaro daga dukkan wani sauti ko wani abin
kallo mai firgitarwa da tsoratarwa, domin (rashin yin)
hakan na iya cutar da qwaqwalwarsa tun yana
qarami.‛173
Amma abin mamaki shi ne, waxansu iyayen,
tsoratar da `ya`yansu su ke yi ta hanyar kiran sunan dodo
ko kyanwa (mage) ko kura ko kare ko vera ko wani sauti
mai firgitarwa da tsoratarwa, a duk lokacin da su ke son
yara su daina kuka, ko kuma su daina yin wani abu mara
kyau. Ta haka, sai yaro ya taso da tsoron dodo ko aljannu
a cikin zuciyarsa, maimakon ya ji tsoron Allah kuma ya
saba da jarumta da sadaukantaka. Lallai ne iyaye su ji
tsoron Allah game da wannan al’amari.
12. Karantar da `ya`ya ilmin Shari’ah da ilmin sana’a, ko
kuma a tura su makaranta don su koyo. Ta hanyar ba su
ilmin addini, da zaburar da su a kan aiki da shi, iyaye za
su kare kawunansu da na iyalinsu daga wuta, kamar
yadda Allah Ya yi umurni. Haka kuma, ta hanyar ilmin
sana’a ne, `ya`ya za su zama masu kishin zuci, da dogaro
da kai, da amfani ga al’umma.174
lillah’ bayan atishawa ko kuma addu’a ga wanda ya yi atishawa, da kabbarbarin īdi, da zikirin bayan sallar farilla, da talbiyya, da
kabbarbari wajen aikin hajji, da karatun Alqur’ani, da faxin ‘Bismillah’
wajen yanka. Ban da waxannan wurare, ba a buqatar xaga murya da
qarfi a cikin zikiri. 173
Tuhfah al-Maudūd, shafi na 158 174
Ilmi shi ne mafificin abin da ya kamata a yi amfani da dukiya wajen
nemansa, domin kuwa babu abin da ya kai shi daraja. Da ilmi ne a ke
sanin Allah domin a bauta maSa; kuma da ilmi ne a ke sanin haqqoqin
kowa domin a ba shi. Ilmi haske ne da a ke shiryuwa da shi; yana gadar
da taqawa; kuma yana jawo daraja da xaukaka ga wanda ya mallake
97
shi. Ilmi shi ne ma’aunin halal da haram; kuma shi ne maganin cutar
jahilci da rarraba a tsakanin mutane.
Neman ilmi ibada ce, kuma bitarsa tasbihi ne; bincike a kansa jihadi
ne; koyar da shi ga wanda bai sani ba sadaka ce, kuma yaxa shi a cikin
masu shi aikin lada ne. Ilmi mai xebe wa mai shi kewa ne a lokacin
kaxaici, kuma aboki ne a halin tafiya; da shi ne a ke sanin Allah kuma a
bauta maSa; da shi ne a ke sanin matsayin Allah kuma a girmama Shi.
Lafazin ilmi ( ) ya zo a cikin Alqur’ani fiye da sau saba’in da
bakwai, a bisa yanayi dabam daban na jujjuyawar kalmomi a harshen
larabci. Haka kuma lafazin ya zo da ma’anoni mabambanta a wurare
masu yawa a Alqur’ani. Ya zo da ma’anar: sanin abu bisa haqiqanin yadda ya ke [Baqarah, 2:77, 216]; gani [Aal Imrān, 3:142; Baqarah,
2:143]; izni [Hud, 11:14]; addini [Baqarah, 2:120]; dalili da hujja [An’ām, 6:148]; Annabta [Yusuf, 12:22]; rarrabewa/tantancewa [Aal
Imrān, 3:166-167]; falala [Qasas, 28:78]; da kuma ma’anar abin da a ke
zaton cewa ilmi ne alhali kuwa a haqiqa ba shi ba ne [Ghāfir, 40:83;
An’ām, 6:148].
Ilmi na da falala mai yawa da matsayi mai girma. Ilmi haske ne da
ke nuna wa mai shi bambancin gaskiya da qarya [Saba, 34:6]; yana gadar da tsoron Allah [Isrā, 17:107-109]; shi ne mafificin jihadi
[Furqān, 25:52]; alama ce ta masu imani [Munafiqun, 63:8]; ba ya
yankewa saboda mutuwa [Sahīh Muslim]; la’ana ba ta sauka a kan ilmi
[Tirmidhi]; alama ce ta alhairi [Baihaqi]; kuma yana shigar da mutane
hanyar aljanna [Muslim]. Saboda falalar ilmi, Allah (Mai girma da
xaukaka) Ya yi wa Annabi Yusuf da Musa da Isa da Muhammad (tsira
da aminci su tabbata a gare su) gori a kan ilmin da Ya ba su [Yusuf, 12:22; Qasas, 28:14; Mā’idah, 5:110; Nisā, 4:113].
Ilmi ya kevanta da abubuwa guda shida: (1) shi ne gadon Annabawa
(2) shi ne kaxai aka yi wa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) umurni da yin addu’ar Allah (Mai girma da
xaukaka) Ya qara masa (3) Allah Ya siffanta kanSa da ilmi (4) kowane
mutum yana farin ciki idan aka danganta ilmi gare shi, ko da kuwa ba
shi da ilmin; haka nan kowane mutum ba ya son a danganta shi zuwa
ga kishiyar ilmi, ko da kuwa jahili ne (5) shi ne kaxai abin da ba ya
raguwa daga mai shi saboda ya ba wani (6) ilmi ba ya qarewa saboda
yawan karantarwa, shi yasa ba a tava samun wanda aka ce, ‘Allah
sarki, wane ya kasance mai ilmi, amma yanzu ilmin ya qare’, duk da
cewa a kan ce, ‘wane mai kuxi ne, amma yanzu ba shi da komai’ ko
kuma ‘wane mai mulki/sarauta ne, amma yanzu ba shi da komai’.
98
Masu ilmi manyan mutane ne a cikin Musulunci domin su ne
malamai waxanda ke koyo kuma su koyar, su karanta kuma su
karantar. Malamai su ne ke yi wa al’umma tarbiyya a kan ilmi [Aal Imrān, 3:79; Mā’idah, 5:44]; su ne ke yi wa al’umma shugabanci,
matuqar sun lazimci haquri da taqawa [Baqarah, 2:248; Sajdah, 32:24]; suna daga cikin Ulul Amr da aka ce a yi wa xa’a [Nisā, 4:59]; su ne
Ahluz Zikr da aka ce a yi wa tambaya [Nahl, 16:43; Anbiyā, 21:7]; su
ne Allah Ya ce a koma gare su a lokacin da wani abu mai girma ya auku [Nisā, 4:83]; su ne waxanda Allah Ya gwama shaidarsu da
shaidarSa [Aal Imrān, 3:18]; su ne waxanda bin hanyarsu ke kai mutum
ga shiriya [Maryam, 19:43]; su ne magadan Annabawa [Abu Dāwud da
Tirmidhi]; su ne waxanda ke tsoron Allah [Fāxir, 35:28]; suna daga
cikin waxanda Allah Ya ke xaukaka darajarsu [Mujādalah, 58:11];
kuma suna daga cikin waxanda Allah Ya ke nufi da alhairi [Bukhari da
Muslim]; su ne mafi hasken fuska kuma mafi xaukakar mutane saboda
addu’ar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) gare su [Ahmad, Abu Dawud, Tirmidhi da Ibn Mājah]; Allah (Mai
girma da xaukaka) Ya hore masu komai don ya nema masu gafarar Allah kuma ya yi masu addu’a [Abu Ya’alā]; su ne waxanda Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya bar wasiyya game da su [Ibn Mājah].
Neman ilmin Shari’ah domin aikata abin da Allah Ya xora wa kowane bawa wajibi ne [Nahl, 16:43; Anbiyā, 21:7; Muhammad,
47:19; Xabarāni]; idan kuwa wajibin kowa da kowa ne, nemansa wajibi
ne a kan al’umma gaba xayanta [Ibn Abdil-Barr, a cikin At-Tamhīd;
An-Nawawi, a cikin Al-Majmū’; da Ibn Taimiyyah, a cikin Majmū’ul Fatāwā]. Haka kuma, neman ilmin sana’a da kimiyya da fasaha da
sauran na’o’in ilmin rayuwa, wajibi ne al’umma ta samu wakilci,
saboda yana daga cikin tattali da kintsin da Allah (Maxaukaki) Ya yi
umurni [Anfāl, 8:60], kuma ya shiga cikin qa’idar
. Don haka, dole ne Musulmi su shiga makarantar boko domin
samun ilmin fannoni dabam daban, gwargwadon buqatar kowane
zamani, da kuma kowace al’umma.
Ilmi na da muhimmanci a rayuwar Musulmi. Da ilmi ne a ke
tabbatar da tsantsar bauta ga Allah. Sanin halal da haram ba zai yiwu ba
sai da ilmi. Ba za a iya sanin kevance-kevancen Musulunci da falalarsa
ba sai da ilmi. Tunkarar qalubalen da ke fuskantar al’ummar Musulmi,
musamman munanan aqidodi, da al-gazwul fikriy, da koma bayan
Musulmi a fagen ilmi da tattalin arziqi da gudanarwa, ba za ta yiwu ba
sai da ilmi. Bayan wannan, kyakkyawar wakilci ga Musulmi a kowane
99
Mutum zai yi takaici idan ya dubi yadda waxansu iyaye
ke nuna halin ko in kula game da ilmin `ya`yansu.
Waxansu ba su damu da koyar da su, ko tura su
makaranta don koyon ilmin addini ba. Waxansu kuma,
suna tura su, amma ba su ba karatun muhimmanci ba,
kamar yadda suka ba na boko. Wannan yasa waxansu
yaran ke yi wa ilmin addini ko malaman addini kallon
biyu ahu, kuma suna fifita duk wani abin da ya shafi
karatun boko a kansa. Wannan irin qasqanci da iyaye ke
jawo wa ilmin addini, babban bala’i ne. Ya kamata a
nuna wa yara cewa girmama ilmi da malamai bisa
qa’idodin Shari’a, wajibi ne a kan kowa. Sanannen abu
ne cewa malamai su ne magadan Annabawa. Allah (Mai
girma da xaukaka) Ya ce: ‚Ka ce, ‚Ashe, waxanda suka
sani, suna daidaita da waxanda ba su sani ba?‛ Masu
hankali kawai ke yin tunani.‛175
Kuma Allah (Mai girma
da xaukaka) Ya ce: ‚Allah na xaukaka waxanda suka yi
imani daga cikinku da waxanda aka bai wa ilmi, wasu
darajoji masu yawa, kuma Allah Mai qididdigewa ne ga
dukan kome.‛176
A vangaren ilmin zamani, ko koyon sana’a, da yawa
daga iyaye (musamman a qauyuka) na sakaci wajen tura
`ya`yansu. Za ka ga `ya`ya na wasa a gida, ko a kan titi,
a lokacin da ya kamata su je makaranta, ko wajen koyon
sana’a. A qarshe, idan `ya`yan suka taso ba tare da ilmin
vangaren rayuwa ta dogara ne a kan ilmi. Haka kuma, bin umurnin
Allah (Mai tsarki da xaukaka) da ManzonSa (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) yana yiwuwa ne kawai idan akwai ilmi. 175
Zumar, 39:9
176 Mujādalah, 58:11
100
zamani ko ilmin sana’a ba, sai su zama mabarata, ko
`yan bangar siyasa, ko `yan daba.177
177
Tarihi ya tabbatar da cewa al’ummar Musulmi ta kasance abar
alfahari saboda bunqasar da ta yi a fagen ilmi, da shugabanci, da
tattalin arziqi, da tsarin zamantakewa, irin waxanda duniya ba ta tava
gani ba. Haka kuma, ta kasance al’ummar da ta yi fice wajen dogaro da
kai, da kishin zuci, kamar yadda ta shahara wajen kawo amfani da ci
gaba ga duniya baki xaya.
Amma a yau, abubuwa da dama sun canza a cikin wannan al’umma.
Xaukakarta ta yi qasa, haskenta ya dushe, shahararta ta wuce,
jagorancinta ya kuvuce, darajarta ta ragu, kuma matsayinta ya faxi. A
fagen ilmi, sauran al’ummomi sun yi mata fintinkau. A vangaren
tattalin arziqi da ci gaban rayuwa, an bar ta a baya. Wannan yasa
talauci da jahilci suka addabe ta, kuma rashin sanin ciwon kai ya yaxu
a cikinta. Hakan, ya haifar da ci baya sosai a gare ta.
Rashin kishin kai da wadatar zuci sun sanya waxansu daga cikin
`ya`yan wannan al’umma sun xauki zaman kashe wando da xumama
benci a matsayin alamar wayewa; barace-barace da roqo da maula da
bambaxanci a matsayin sana’a; kuma zaman ludo da karta da tsegumi a
matsayin hanya mafi dacewa ta amfani da lokaci. Wannan xabi’a ta
jawo wa al’ummar Musulmi koma baya, da qorafi da tsana da kushe
daga sauran al’ummomi.
Daga cikin waxannan munanan xabi’u, yawon maula ya fi haifar da
illoli da sharri a cikin al’umma, kasancewar masu yin maula sun tattaro
aibobin da suka zarce saura. Galibin masu yawon maula na da’awar
wayewa da sanin inda duniya ta sa gaba. Suna yin kyakkyawar shiga, ta
hanyar sanya manyan rigunar da ke bayyana su a matsayin manyan
mutane. Xabi’arsu ita ce, bin gidajen masu kuxi, da ofisoshin manyan
ma’aikata, da wajen hirar manyan `yan siyasa, don samun abin cefane.
Sana’arsu ita ce neman abin hannun mutane ta hanyar da ba ta dace ba.
Maula ta qunshi neman abin hannun mutane, ba tare da haqqi ba, ta
hanyar qarya ko naci ko bambaxanci ko zamba. Manufar xan maula ita
ce samun biyan buqata daga waninsa ta kowace irin hanyar da za ta
jawo masa qasqanci, da wulaqanci, da mutuwar zuciya, da xabi’ar
samun na banza. Mutanen da ke yin maula, na xaukar wannan xabi’a, a
matsayin sana’a, kasancewar ba su da wata hanyar samun biyan
buqatar rayuwa da ta wuce ta. Don haka, su ke yin takakkiya zuwa gida
ko ofis ko wajen sana’ar wanda za su yi wa maular, ko dai da sunan
siyasa ko malanta ko kuma wani abin daban.
101
Haqiqa, Musulunci ya hana bin irin waxannan hanyoyi da `yan
maula ke amfani da su don samun biyan buqata a hannun jama’a. A
cikin hadisai da dama, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya tsawatar game da roqo (idan babu tsananin larura) ko
naci, don a raba wani da abin hannunsa, ko zaqewa cikin yabo, ko
zamba domin a karvi wani abu a hannun mutane. Haka kuma, Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi kyakkyawar
addu’a ga waxanda ke kamewa daga roqo ko bambaxanci.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce wa Hakīm bn Hizām (Allah Ya yarda da shi):
‚Ya Hakīm! Dukiya, na da daxi: to wanda ya karve ta (a hannun wani)
bisa daxin rai (daga wanda ya ba da), za a sanya masa albarka a cikinta.
Wanda kuwa ya karva ta hanyar naci (ko bambaxanci), ba za a sanya
masa albarka a ciki ba. Kuma zai zamanto kamar wanda ke cin abinci,
amma ba ya qoshi‛ [Bukhari].
Dangane da raba mutane da abin hannunsu ta hanyar naci, Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Wanda ya roqi mutane (abin hannunsu) alhali yana da abin da ya kai qimar Uqiyah, to haqiqa ya yi naci‛ [Abu Dawud da Nasā’i].
Dangane da amfani da hanyar zamba ko kushe don kai wa ga biyan
buqata, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
ce:
‚ Tir da bawan dinare da dirhami da bargo da riga: idan an ba shi (abin
da ya nema) sai ya gamsu (ya yi yabo). Amma idan bai samu ba, ya qi
gamsuwa (ya yi zamba)‛ [Bukhari].
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya bayyana irin haxari da halin qasqanci da mai maula ke ciki, da
kuma mummunar makomarsa idan bai tuba ba. Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Mutum ba zai gushe yana tambayar mutane dukiyarsu ba, har sai ya zo
a ranar Qiyama, ba tare da ko tsoka xaya a fuskarsa ba‛ [Bukhari].
Malamai sun ce hadisin zai iya xaukar cewa mai roqo zai zo a
qasqance, ba tare da mutunci ko qima ba a ranar lahira (saboda neman
102
abin hannun mutane da ya riqa yi), ko kuma hadisin na nufin za a yi
masa azaba a fuskarsa har sai naman ya zaganye gaba xaya.
Kuma Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ya ce:
‚Roqo magurji ne da mutum ke gurje fuskarsa da shi. Don haka, wanda
ya so, ya ci gaba da gurje fuskarsa ko ya bari, sai dai idan mutum zai
roqi sarki ne, ko (zai yi roqo) cikin abin da ba shi da makawa‛ [Abu Dawud, Tirmidhi da Nasā’i].
A cikin wani Hadisin, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce:
‚Wanda ya roqi mutane wani abu alhali ya wadata daga gare shi, zai zame masa wani abin qasqanci a fuskarsa‛ [Dārimi da Ahmad].
Dangane da mummunar makomar xan maula ko mai sana’ar roqo
idan bai tuba ba, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce:
.
‚Wanda ya yi roqo alhali yana da abin da zai wadace shi, to yana
yawaita (rabonsa ne) daga wutar Jahannama.‛ Suka ce: Ya Manzon
Allah, mene ne zai wadace shi? Ya ce: ‘Abin da zai ishe shi yin kalaci
ko abincin dare‛ [Ahmad]. A ruwayar Abu Dawud: ‚Ya kasance yana
da abincin yini da dare (kwana xaya).‛
A cikin wani Hadisin, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya ce:
‚Wanda ke roqon mutane dukiyarsu don yawaita abin da ya mallaka,
yana roqon garwashin wuta ne. Don haka (ya rage gare shi) ya roqi
kaxan ko mai yawa‛ [Muslim].
Bayan wannan, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya yi yabo ga waxanda ke kamewa daga roqo ko maula, kuma
ya lamunce masu shiga aljanna a ranar qiyama. Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
103
‚Ya samu babban rabo: wanda ya musulunta, kuma aka azurta shi da
(gwargwadon) abin da ya ke buqata, kuma Allah Ya sanya masa
wadatar zuci a cikin abin da Ya ba shi‛ [Muslim].
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce:
‚Wane ne zai lamunce mani cewa ba zai nemi komai a hannun mutane ba, ni kuwa in lamunce masa shiga aljanna? Sai Thaubān (Allah Ya
yarda da shi) ya ce: ‘Ni ne’. Don haka ya kasance ba ya neman komai a hannun wani‛ [Nasā’i da Baihaqi].
Babu shakka, maula na haifar da matsaloli ga wanda ke yinta, da
wanda a ke yi wa, da al’umma baki xaya. Daga cikin matsalolin da
maula ke haifarwa ga mai maular, akwai: jawo mutuwar zuciya; da
zama talasuru; da jawo qasqanci, da qyama, da zubewar mutunci a
cikin jama’a; da tauye tattalin arziqi; da mummunar makoma a lahira
idan ba a tuba ba.
Wanda a ke yi wa maula bai kuvuta daga sharri da aibobinta ba.
Daga cikin aibobinta ga wanda a ke yi wa, akwai: tauye tattalin arziqi,
domin yana vatar da kuxi ta hanyar abin da bai tanada ba; da haifar da
girman kai da riya; da yin xabi’ar xan hali don a cike gurbin abin da
aka rasa ta hanyar biyan buqatar masu maula.
Sharrin maula bai tsaya a kan xaixaikun mutane ba. Gaba xayan
al’umma ba su kuvuta daga musifarta ba, domin tana haifar da koma
baya gare su ta hanyar: rashin ba da gudummuwa wajen samar da
buqatun al’umma; da jawo tsana da kushe ga al’umma daga sauran
qasashen qetare; da yaxa aqidar zaman kashe wando; da jawo wa
gwabnati hasarar kuxin shiga; da jawo wa gwabnati qarin kashe kuxi
don samar da abubuwan more rayuwa, kamar magani a asibiti da ruwan
sha ga mutanen da za su iya tallafa wa kansu, ba domin suna yin maula
ba.
Ban da maula, xabi’ar barace-barace na daga cikin matsalolin da ke
addabar al’ummar Musulmi, musamman a arewacin Nijeriya. Mabarata
sun xaukar wa kansu xabi’ar roqon mutane abin hannunsu, ta hanyar
qasqanci da wulaqantar da kai, da jawo wa Musulunci da Musulmi
gori, musamman a idanun kafirai. Mutuwar zuci da rashin kishin kai
sun sanya waxansu mutane sun xauki bara a matsayin sana’a, duk da
cewa mafi yawansu suna da lafiyar jiki, da ikon yin aiki don dogaro da
kai, ba tare da sun zame wa al’umma matsala ba. Abin baqin ciki shi
ne, maimakon a qyamaci xabi’ar barace-barace a tsakanin Musulmi,
mafi yawan mutane ba su damu ba. Hasali ma, waxansu azzaluman
104
malamai na qarfafar wannan mummunar xabi’a, kuma suna goyon
bayan mabarata, har ma suna nuna cewa Musulunci bai hana xaukar
bara a matsayin sana’a ba. Bayan haka, wasu daga cikin irin waxannan
azzaluman malamai na da’awar cewa karatun Alqur’ani ba zai yiwu ba
sai an yi bara, duk da cewa su ba su tura `ya`yansu almajiranci.
Kasancewar maula da barace-barace alamomi ne waxanda ke nuna
ci baya, da rashin sanin ciwon kai a cikin al’umma, Musulunci ya
tanadar da hanyoyin magance su. Hanyoyin da Musulunci ya bi wajen
magance matsalar maula da bara sun kasu gida biyu. Kashi na farko ya
qunshi saitin tunani da zaburarwa game da dogaro da kai. Kashi na
biyu ya shafi matakan tattalin arziqi da havaka dukiya.
Musulunci ya xauki matakin yin saiti ga tunanin mabiyansa dangane
da haxarin maula da barace-barace da zaman kashe wando da
bambaxanci da rashin kishin zuci ko dogaro da kai, kuma ya zaburar da
su a kan tsare mutunci ta hanyar yin sana’a. Matakan da Musulunci ya
xauka a wannan vangare sun haxa da:
1. Tunatar da su yalwar qasa da abin da ke cikinta, da hore ta da aka
yi gare su, ta yadda za su yi fafutukar neman na kansu. Kuma aka
tabbatar masu da cewa neman arziqi da alhairan da ke cikin qasa, ibada ce ga Allah [A’arāf, 7:10; Mulk, 67:15].
2. Sanya fafutukar neman na kai ta hanyar halal a matsayin alama ta tawakkali ga Allah [Ahmad da Tirmidhī].
3. Kwaxaitarwa game da yin noma, da kasuwanci, da sana’o’in
hannu, da sauran ayyuka (na albashi ko lada) [Bukhari da
Muslim].
4. Xaukar yin aiki don samun abin biyan buqatar rayuwa a matsayin
sadaka, da kuma hanyar ba da sadaka [Bukhari da Muslim].
5. Rashin yarda da duk abin da aka samu ta hanyar da ba ta dace ba.
Wannan yasa Musulunci ya haramta qwace, da fashi, da sata, da
caca, da kuxin ruwa (riba), da duk wata harkar kuxi da ke da
alaqa da su. Kuma ya tanadi uquba dabam daban ga waxanda
suka aikata xayansu. Ta wannan hanyar, Musulunci ya kallafa wa
mabiyansa neman na kai da rashin zaman xumama benci [Mā’idah, 5:33; Mā’idah, 5:38; Baqarah, 2:275-276, 278-279;
Baqarah, 2:219; Mā’idah, 5:90].
105
Ilmin addini wajibi ne a kan kowane Musulmi. Da shi ne
a ke sanin Allah, kuma a ke sanin dokokinSa, da yadda
za a bauta maSa. Ilmi shi ne maganin cutar jahilci da
6. Tsawatarwa game da roqo, da maula, da barace-barace, da
yaudara [Bukhari da Muslim].
7. Hana ba da sadaka ga mawadata, da waxanda ke da lafiyar jiki da ikon yin aiki don dogaro da kai [Tirmidhī].
Bayanan da suka gabata na nuna wa kowane Musulmi wajibcin
dogaro da kai gwargwadon iko, don tsare mutunci, da nisantar zaman
kashe wando, da baxala, da aqidar cima zaune. Alqur’ani da Sunnar
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sun nuna
wa kowane mutum muhimmancin yin gwagwarmayar neman abin kai
ta hanyar kasuwanci da sana’o’in hannu ko aikin da za a biya lada.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Mutum bai ci abinci mafi alhairi ba fiye da wanda ya samu ta hanyar
aiki da hannunsa‛ [Bukhari]. Haka kuma, Alqur’ani da Sunnah sun
karantar da cewa Allah (Maxaukaki) Ya tarbiyyantar da fiyayyun
halittarSa, Annabawa, a kan yin aiki, domin su zama abin koyi.
Wannan yasa suka yi sana’o’i dabam daban, waxanda suka haxa da
kasuwanci, da kiwon dabbobi, da qira. Bayan wannan, an umurci
kowane Musulmi ya nemi ilmin bauta wa Allah da ilmin harkokin
rayuwa don samun damar amfanar da kansa, da sauran al’umma,
gwargwadon iko, kamar yadda aka hana shi zaman banza, da aqidar
maula da bara, da zame wa al’umma nauyi.
A taqaice, wajibi ne kowane Musulmi ya nemi abin yi, wanda zai
taimaka masa wajen dogaro da kansa, da nisantar neman abin hannun
mutane, ba tare da haqqi ba, ta hanyar naci ko roqo ko bambaxanci ko
qarya ko zamba. Kuma wajibi ne ya ji tsoron Allah a cikin dukkan
al’amuransa.
A vangaren al’umma kuma, Musulunci ya wajabta mata taimaka wa
mutanen da ke da kishin koyon sana’a don magance zaman kawai. Za a
yi hakan, ta hanyar koya masu sana’o’i, da samar da ayyukan yi ga
waxanda ke da ilmin yin ayyukan hukuma. Haka kuma, akwai buqatar
samar da tallafi ga waxanda suka qware a kan waxansu sana’o’in
hannu, amma ba su da kayan aiki. Manufar ita ce a ba su damar amfani
da qwarewarsu da hazaqarsu wajen dogaro da kansu, da tallafa wa
waxanda za su yi aiki a qarqashinsu.
106
cutar savanin da ke tsakanin al’umma. Shi kuma ilmin
zamani ko ilmin sana’a, gishirin zaman duniya ne.
Wanda ba shi da ilmi, ya rasa komai, ko da kuwa yana
da mulki ko dukiya. Kowane mutum yana buqatar ilmin
addini da na zamani/sana’a, kamar yadda ya ke buqatar
qosasshiyar lafiya, da abinci, da abin sha, da tufafi, da
wajen kwana. Domin kuwa babu yadda za a yi al’umma
ta samu ci gaba, matuqar mafi yawan jama’arta na cikin
jahilci. Wannan ya sa aka ce: ‚wanda ke neman lahira,
ya nemi ilmi; wanda ke neman duniya, ya nemi ilmi;
haka kuma, wanda ke neman duniya da lahira gaba xaya,
to ya nemi ilmi.‛178
Don haka, lallai ne iyaye su ji tsoron Allah game da
ilmin `ya`yansu. Su sani, Allah zai tambaye su a ranar
Qiyama, domin kuwa `ya`ya amana ce a gare su. Su yi
amfani da dukiyar da Allah Ya ba su (komai
qanqantarta) wajen ilmantar da `ya`yansu. Su fifita
neman ilmi ga kansu, da `ya`yansu, da sauran waxanda
ke qarqashinsu a kan komai. Babu hasara ko kaxan a
cikin dukiyar da aka ciyar wajen neman ilmin addini da
na zamani.
Sannan, wajibi ne a kan iyaye su zava wa kansu, da
`ya`yansu makarantun da suka dace, don koyon ilmin
addini da na zamani. Ilmin da babu tarbiyya a cikinsa
akwai matsala. Sanannen abu ne cewa akwai makarantun
islamiyya da dama a wannan lokaci waxanda ba su da
alqibla ko tsarin karantarwa mai kyau. A waxansu
makarantun ma, ba a karantar da yara sahihin addini,
kamar yadda ya ke qunshe cikin Alqur’ani da hadisai
ingantattu bisa fahimtar magabata na qwarai. Maimakon
178
Ana danganta wannan magana ga Imam Ash-Shāfi’ī (Allah Ya
jiqansa)
107
haka, za ka ga ana koyar da waqe-waqe, da hadisan
qarya, da sauran abubuwan da ba su da wani ingantaccen
dalili a cikin Shari’ah. Abin mamaki, waxansu iyayen
ma, suna kai `ya`yansu makarantun islamiyyar `yan
bidi’a ne, ko ma makarantun `yan shi’a, inda za su koyo
zagin Sahabbai, da cin mutuncin matan Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da aqidar
qiyayya ga Musulmi. Babu shakka, wanda duk ya yi
haka, haqiqa ya ha’inci amanar kulawa da `ya`ya, wadda
Allah (Mai girma) Ya xora masa.
A vangaren ilmin boko ko koyon sana’a ma, akwai
matsaloli dabam daban. Sau da yawa, iyayen da ba su
kishin addininsu na tura `ya`yansu makarantu ko
wuraren koyon sana’a da ke da haxari ga addini da
tarbiyya. Sau da yawa, mun ji labarin yaran da ke rufe
idanu don yin addu’ar coci wajen cin abinci, ko kuma su
riqa maimaita waqoqin kirista waxanda suka koya a
makaranta. Yaran da ke da hazaqa ma, har na xaya su ke
yi a darasin addinin kirista. A wajen koyon sana’a ma,
ana samun matsaloli, musamman idan abin ya haxa da
waxanda ba musulmi ba. Da yawa matasa na qorafi
game da yadda mutanen da ke koya masu aiki ke hana su
yin salla a kan lokaci, ko su tursasa su a kan munanan
al’adunsu, kamar durquso ko kwanciya wajen gaisuwa,
ko a umurce su da sayen giya a lokacin da za a yaye su.
Saboda haka, tilas ne iyaye su sanya ido a kan harkar
ilmin `ya`yansu. Su tabbata sun zavar masu makarantu
ko wuraren koyon sana’a da suka dace. Ta haka ne za a
samu ilmi mai kyau, kuma mai amfani, sannan a gina
al’umma ta qwarai.
13. Wajibi ne iyaye su koya wa `ya`yansu yin salla, da zarar
sun kai shekara bakwai. Kafin wannan lokaci, iyaye su
108
koya wa `ya`yansu ma’anar kalmar shahada, da
hukunce-hukuncen tsarki da alwalla, da sauran hukunce-
hukuncen da ya kamata yara qanana su sani. Idan `ya`ya
mata ne, za a sanar da su hukunce-hukuncen jinin al’ada
(jinin haila) da zarar sun kusa balaga.179
Haka kuma, an
179
Jinin al’ada shi ne jinin da ke fito wa da kansa daga al’aurar mace
wadda za ta iya xaukar ciki, kuma yana daga manya-manyan alamomin
balaga a haqqin mace. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya bayyana wa A’isha (Allah Ya yarda da ita) cewa jinin
al’ada wani abu ne da Allah (Maxaukaki) Ya hukunta shi a kan mata daga cikin `ya`yan Adam [Bukhari]; kuma Abdullah ibn Abbās (Allah
Ya yarda da shi) ya ce, ‘farkon wadda ta fara yin jinin al’ada ita ce Hauwa, bayan an saukar da su daga aljanna’ [Hākim da Ibnul Munzir].
Mafi yawan mata na fara jinin al’ada ne daga shekara goma sha biyu
(12) har zuwa shekara hamsin (50), ko da ya ke waxansu na farawa
kafin su kai shekara goma sha biyu, waxansu kuma na wuce shekara
hamsin kafin su daina. Maganganun da aka ruwaito cewa an iyakance
shekarun jinin al’ada zuwa 55 ko 70 ko 60 ko 50, duk ba su inganta ba, kamar yadda Ad-Dārimi da Ibn Taimiyyah suka bayyana. Amma a mafi
yawan lokaci, `yan mata na fara jinin al’ada ne daga shekara goma sha
biyu, idan suna zaune a cikin qasashe masu zafi, ko kuma shekara
goma sha huxu, idan suna zaune a cikin qasashe masu sanyi. Abdul-Muta’ālī Jabrī, a cikin littafinsa Fiqhul Ukhtil Muslimah fix Xahārah wal Haid, ya bayyana cewa duk macen da ta ga jini ya zubo mata kafin
ta kai shekara tara (9), to, wannan jinin cuta ne, ba jinin haila ba.
Jinin al’ada ba shi da qarancin kwanaki ko mafi yawan kwanaki. A
duk lokacin da mace ta ga jini ya zubo mata, a tsakanin lokacin da ta ke
sa ran jinin al’adarta zai zo, kuma ta fahimci cewa ba jinin cuta ba ne,
tana nan a matsayin mai haila, ko da ya xauki kwanaki da yawan gaske.
Babu wani hadisi ingantacce da ya iyakance kwanakin haila, kamar
yadda Ibnul Munzir da Ibn Taimiyyah da Ibnul Qayyim da Ash-Shaukāni da Sadīq Khān suka tabbatar. Hadisin da ke magana a kan
qarancin lokacin haila kwana uku, kuma mafi tsawancinsa kwana goma
sha biyar, hadisi ne na qarya, a bisa ittifaqin malamai. Haka kuma,
hadisin da ya yi magana a kan kwana shida ko bakwai, yana magana ne
a kan jinin istihadha (jinin cuta) ba jinin al’ada ba.
Jinin al’ada na da launi guda uku, matuqar babu wata illar da ta
cuxanye shi: (1) launin ja (2) launin fatse-fatse (kamar ruwan qwai) (3)
launin qasa-qasa (kamar gurvataccen ruwa). Jinin al’ada na yankewa
109
ne ta hanyoyi guda biyu: (1) bushewar kafar da jinin ke zubowa, wato,
mace ta sanya wani abu kamar farin qyalle ko audugar mata a cikin
al’aurarta, ta fito da shi ba tare da jini ba (2) fitowar farin ruwa daga
mahaifa.
Mafi yawan mata ba su yin jinin al’ada a lokacin da su ke da juna
biyu. Hasali ma, babbar alamar da ke nuna cewa mace ta xauki ciki, ita
ce, jinin al’adarta ya qi zuwa a lokacin da ya kamata. Idan mace mai
ciki ta ga jini ya zubo mata, ta garzaya asibiti, kasancewar wannan jinin
alama ce ta haxari. Amma kuma, an ce `yan kaxan daga matan da ke da
juna biyu na yin jinin al’ada, ko da ya ke binciken likitoci yana nuna
shakku a kan haka. Ke nan, idan mai ciki ta ga jini ya zubo mata, irin
wanda ta saba yi na al’ada, kuma ta je asibiti, aka tabbatar da cewa ba
vari ne za ta yi ba, sai ta xauke shi a matsayin jinin al’ada.
An haramta wa macen da ke al’ada: (1) sallar farilla da ta nafila (2)
azumin farilla da na nafila (3) saduwa, wato, kwanciyar aure da miji (4)
xawafi a xakin ka’aba, matuqar ba a kai ga larurar da dole sai ta yi
xawafin a haka ba. Idan an kai ga wannan larura, misali, kamar ya
zamanto za ta rasa aikin hajjin wannan shekara idan ba ta yi ba, Ibn
Taimiyyah da waxansu malamai na ganin za ta iya yin qunzugu, ta
gabatar da xawafinta, a cikin jinin al’ada (5) sakin aure, wato, haramun
ne mijinta ya sake ta a lokacin da ta ke cikin jinin al’ada.
An halatta wa matar da ke cikin jinin al’ada: (1) zikirin Allah da karatun Alqur’ani, a bisa fahimtar Abu Hanīfah da Shāfi’ī da Ahmad
ibn Hanbal da Ibn Hazm (2) sujudar tilawa a cikin karatun Alqur’ani,
kasancewar babu wani sahihin dalili da ya hana yin haka (3) xaukar
Alqur’ani, kasancewar babu wani nassi sahihi wanda qarara ya hana ta
xaukar Alqur’ani ko ya hana ta tava shi (4) miji ya kwanta a kan
cinyarta, ya karanta Alqur’ani (5) halartar filin sallar idi, ko da ya ke ba
za ta yi sallar ba (6) shiga masallaci (7) a ci abinci tare da ita (8) yin ma
mijinta hidima (9) kwanciya tare da ita, amma ban da saduwar aure
(10) rungumarta da sumbantarta.
Idan jinin al’ada ya qi tsayawa, har na tsawon lokacin da aka
fahimci ya zamanto na cuta, ko kuma mace ta zamanto tana yin jinin
al’ada fiye da sau biyu a cikin wata xaya, ko kuma jinin ba ya wuce
kwana xaya ko biyu a cikin kowane wata, wannan jini ya zamanto na
istihadha (jinin cuta). Idan tana da sanannen adadin kwanakin haila,
kafin ya fara mata gardama daga baya, za ta yi amfani da kwanakin da ta saba yi a can baya, kamar yadda hadisin Ummu Habībah ya tabbatar.
Idan ba ta tava samun iyakantaccen kwanaki ba tun da ta fara haila,
amma za ta iya bambancewa a tsakanin jinin la’ada, da jinin istihadha,
110
so iyaye su riqa zuwa da `ya`yansu masallaci, kuma su
koya masu azumi tun suna qanana, don su saba. Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Ku umurci `ya`yanku da yin salla idan sun kai shekara
bakwai; kuma ku buge su a kanta (idan suka qi yi) idan
sun kai shekara goma; kuma ku raba su a wajen
kwanciya (ta yadda kowanne daga cikinsu zai samu
gado/katifa ko kuma mayafi daban).‛180
Kuma Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi sallar jam’i a cikin masallaci yana riqe da Umāmah bint
Zainab181
, kamar yadda ya yi salla tare da al-Hasan ko
al-Husain a hannunsa.182
Bayan wannan, Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Na
kan fara salla da niyyar tsawaitawa a cikinta, amma idan
na ji kukan yaro (a cikin masallaci), sai in gajarta sallar
don (gudun) kada in takura mahaifiyarsa (da ke salla tare
da mu).‛183
Dangane da koya masu azumi, ar-Rabi’ bint Mu’awwidh
(Allah Ya yarda da ita) ta ba da labarin cewa sun kasance suna koya wa qananan yara azumin āshura a zamanin
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi). Har ma su kan tafi da su masallaci tare da kayan
wasa, ta yadda idan sun fara kuka saboda yunwa, sai su
ba su kayan wasa.184
Bugu da qari, hadisi ya tabbata
za ta yi amfani da launin baqi a matsayin haila, launin ja a matsayin
istihadha; ko kuma mara kauri a matsayin haila, shi kuma mai kauri a matsayin istihadha, kamar yadda hadisin Fāximah bint Abi Hubaish ya
nuna. Idan kuwa ba za ta iya bambancewa a tsakaninsu ba, sai ta xauki
kwana shida (6) ko kwana bakwai (7) a matsayin al’adarta, bisa la’akari
da kwanakin da tsararrakinta ke yi. 180
Abu Dāwud: Sahīh 181
Bukhari da Muslim 182
Ahmad da Nasā’i: Sahīh 183
Bukhari 184
Bukhari da Muslim
111
cewa wata mace ta ce wa Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi), bayan ta xaga wani
yaron da ke hannunta: ‚ya halatta wannan (yaron) ya yi
aikin hajji‛? Sai Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Na’am, kuma ladan (aikin
hajjin da ya yi) naki ne (tunda shi bai balaga ba).‛185
Waxannan hadisai na nuna yadda Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) da sahabbansa
(Allah Ya yarda da su) suka kasance suna ba da
muhimmanci ga tarbiyyar `ya`ya, da koya masu addini
tun suna qanana, ta yadda ba zai yi masu wuya ba idan
sun balaga. Haka kuma, hadisan na nuna halaccin zuwa
da yara masallaci, da shigar da su cikinsa. Ke nan,
maganar da ta shahara cewa ba a zuwa da yara masallaci,
ba ta da inganci. Haka nan ma, xabi’ar korar yara, ko
zaginsu idan sun shiga masallaci, ba ta da kyau. Hadisin
da ke cewa: ‚Ku nisantar da `ya`yanku daga masallaci‛, mai rauni (da’īf) ne.
186
14. Wajibi ne a koya wa `ya`ya kyawawan xabi’u, da
halayen girma da karamci, don su taso da cikakkiyar
tarbiya.187
A sanar da `ya`ya muhimmancin faxin
185
Muslim 186
Duba Da’īf al-Jāmi’ # 2636; da Da’īf Ibn Mājah #164 187
Kyawawan xabi’u ( ) su ne abu mafi nauyaya mizanin
mumini [Abu Dāwud da Tirmidhi]; xaya daga cikin abubuwan da suka
fi shigar da mutane aljanna [Tirmidhi]; kuma suna daga cikin abubuwa
guda huxu waxanda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce idan mutum na da su, kada ya yi baqin ciki a kan duk
wani abin duniya da ya rasa [Ahmad].
Waxanda ke da kyawawan xabi’u su ne mafi cikar imani [Tirmidhi];
mafi alhairi a cikin mutane, kuma daga cikin zavavvu [Bukhari da Muslim]; suna daga cikin mafi soyuwar bayi a wajen Allah [Hākim];
suna kai wa ga darajar mai azumi da rana, kuma ya raya dare [Abu Dāwud]; su ne mafi kusa da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
112
gaskiya da riqon amana; da cika alqawari; da girmama
manya, da tausayin qanana; da biyayya ga iyaye; da son
`yan’uwa da dangi; da kiyaye haqqin maqwabta, da
girmama baqi; da son `yan’uwa Musulmi, da kare
mutuncinsu; da sauransu. Haka kuma, a sanar da su
haxari, da kuma sakamakon munanan xabi’u.188
Lallai
tabbata a gare shi); kuma Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya lamunce masu wani gida a qololuwar aljanna [Abu Dāwud].
Daga cikin kyawawan xabi’u waxanda ya kamata iyaye su koya wa
`ya`yansu, akwai: taqawa (tsoron Allah, da kiyaye dokokinSa); da
dagewa a kan bauta wa Allah; da juriya; da dauriya; da yafewa da
haquri; da kyauta da ciyarwa; da sadaukantaka; da sauqin kai; da
kyakkyawar mu’amala; da tausayi; da rahama; da soyayya da qiyayya a
kan gaskiya; da adalci; da riqon amana; da faxin gaskiya; da cika
alqawari; da sadar da zumunta; da kyautatawa; da qanqan da kai; da
kunya da kawaici; da gudun duniya (zuhudu); da natsuwa; da tunani
game da halittun Allah (tafakkuri). 188
Munanan xabi’u na hana mutane kai wa ga nasara; suna haifar da
rashin walwala, da rashin aminci da yarda ga waxanda ke da su. Haka
kuma, waxanda ke nuna mummunan hali, na zama abin qyama a cikin
mutane. Munanan xabi’u na da hanyoyi guda uku: (i) zuciya (ii)
harshe; da (iii) gangar jiki.
Ta hanyar zuciya a ke yin munafinci; da hassada; da qiyayya; da
mugunta; da jiji da kai. Ta hanyar halshe a ke faxin magana ba tare da
ilmi ba; da cutar da musulmi ta hanyar cin naman mutane; da shaidar
zur; da qazafi; da qarya; da annamimanci; da vatanci; da izgili; da
tonon asiri; da gori; da batsa; da jayayya a kan varna; da yabon mutane
ba bisa qa’ida ba; da kururuwar mutuwa; da tsinuwa; da waqa. Ta
hanyar gangar jiki a ke taqama; da nuna raini ga mutane; da girman kai;
da nuna isa; da cutarwa ta zahiri; da algushu; da mummunar
zamantakewa.
Munafinci na daga mafi haxarin dukkan munanan xabi’u. Munafinci
ya qunshi bayyanar da savanin abin da aka voye. A shar’ance,
munafinci shi ne bayyanar da Musulunci da voye kafirci da sharri [Baqarah, 2:8-20; Mujādilah, 58:14-19; Nisā, 4:88, 72-73, 136, 142,
145; Aal Imrān, 3:168-169].
Munafinci nau’i biyu ne: munafinci na aqida ko quduri ( )
da munafinci na aiki ( ). Munafincin aqida ya qunshi (i) qaryata
113
ne iyaye su guji koya wa `ya`ya munanan xabi’u, kamar
zagi, da qarya, da sava alqawari, da yaudara, da ha’inci.
Abin mamaki, da yawa daga cikin iyaye na koya wa
`ya`yansu qarya, ba tare da sun sani ba. Misali, za a aiko
ana sallama da mahaifin yaro a qofar gida; amma sai
mahaifin ya ce wa xansa: ‘je ka ce babanka ba ya nan, ko
yana barci’. Ta haka, ya koya wa xansa qarya, ba tare da
ya sani ba. Ko kuma iyaye su kira `ya`yansu qanana da
sunan za su ba su wani abu, alhali kuwa ba komai a
hannunsu. Wannan ma, koyar da qarya da yaudara ce ga
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (ii) qaryata
wani abu daga cikin abubuwan da Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya zo da shi (iii) qin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (iv) qin wani sashe na abin da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya zo da shi (v) farin ciki game da qasqanci ko tawaya ko rashin ci gaban
addinin da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya zo da shi (vi) qin duk wata nasara da addinin Musulunci zai samu.
Wanda duk ya ke da xaya daga cikin waxannan siffofin munafinci,
ya fita daga cikin Musulunci kuma ya shiga cikin waxanda aka siffanta
su da mafi sharrin siffofi, kamar kafirci, da rashin imani, da izgilanci ga
addini, da karkata gaba xaya zuwa ga maqiyan addini. Nau’in munafinci na biyu ya qunshi (i) qarya a wajen bayar da
labari (ii) ha’inci bayan an amince wa mutum (iii) yaudara idan an yi
yarjejeniya (iv) wuce iyaka a wajen husuma (v) sava alqawari (vi)
kasala wajen bauta (vii) riya (viii) rashin ambaton Allah (ix) gaggawa a
cikin salla (x) zunxen waxanda ke yin ayyukan alhairi (xi) izgilanci ga
Allah da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) da Sunnah (xii) rantsuwa a kan qarya (xiii) rashin son ciyarwa saboda
Allah (xiv) watsi da Musulunci (xv) yaxa jita-jita da varna (xvi) aibanta
dokokin Allah (xvii) qasqantar da mutanen kirki (xviii) qin yin sallar
farilla a cikin jam’i (xix) kawo varna, wai da sunan gyara (xx) ba da
uzurin qarya (xxi) umurni da mummuna da yin hani ga kyakkyawa
(xxii) mantawa da Allah (xxiii) qaryata alqawarin Allah ko alqawarin
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) (xxiv) ba
da himma wajen gyara zahiri, amma kuma a yi watsi da baxini (xxv)
rashin fahimtar addini.
114
`ya`ya. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya ce: ‚Wanda ya ce wa yaro: zo ka karva,
sannan, ya qi ba shi komai, to za a rubuta masa
(zunubin) qarya.‛189
Haka kuma, ‘Abdullah ibn ‘Aamir
(Allah Ya yarda da shi) ya ce: ‚Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya zo gidanmu,
lokacin ina qarami. Sai na kama hanya zan fita don yin
wasa. Sai mahaifiyata ta ce: ‘Abdullah, zo ka karva. Sai
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Me ki ke son ki ba shi?‛ Sai ta ce: dabino.
Sai (Manzon Allah) ya ce: ‚Da ba ki ba shi komai ba, za
a rubuta maki (zunubin) qarya.‛190
Waxansu iyayen na koya wa `ya`yansu darussa dabam
daban na zagi da tsinuwa, ba tare da sun sani ba. Kuci-
kuci kaxan sai su zage su, ko su tsine masu. Wani
lokacin ma, iyayen da ba su da tarbiyya, kan sanya
`ya`yansu qanana su zagi yayyensu, ko su yi masu
daquwa (zagi da hannu). Irin wannan mummunar xabi’a
na da haxari ga yaro, domin kuwa zai qware da zagi fiye
da yadda zai qware da karatun fatiha. A vangaren iyaye
ma, akwai babbar illa, kasancewar duk lokacin da
`ya`yan suka yi zagi (a gida ko a waje), iyayen ne aka
zaga. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Lallai yana daga mafi girman zunubi,
mutum ya la’anci mahaifansa. Sai aka ce: Ya Manzon
Allah, ta yaya mutum zai la’anci mahaifansa? Ya ce:
Mutum ya zagi uban wani, shi ma (wancan) ya zagi
ubansa; kuma ya zagi uwar wani, shi ma a zagi tasa
uwar.‛191
189
Ibn Wahab: Sahīh al-Isnād [Duba littafin as-Sahīhah 2/385] 190
Ahmad da Abu Dāwud: Sahīh 191
Bukhari
115
Ban da wannan, waxansu iyayen na koya wa `ya`yansu
ha’inci da algushu a wajen sana’a. Za ka ga an koya wa
yaro/yarinya tauye mudu ko qara ruwa ko yin amaja a
cikin kayan sayarwa. Waxansu `ya`yan kuma, ana koya
masu husuma, da rashin qimanta juna, da yadda savani
ke aukuwa a tsakanin miji da mata, tun suna qanana.
Domin kuwa, waxansu iyayen su kan yi faxa a
tsakaninsu, wani lokaci ma har da dambe, ko murxe
wuyar riga, ko zage-zage da doke-doke a tsakaninsu, a
gaban `ya`yansu. Haka kuma, waxansu iyayen na koya
wa `ya`yansu nau’o’in savon Allah tun suna qanana.
Misali, sai ka ga mutumin da ke shan taba sigari192
ko
192
A zamanin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) da sahabbansa (Allah Ya yarda da su) da waxanda suka biyo bayansu daga cikin tabi’ai da tabi’ut-tābi’īn, babu taba sigari irin wadda
a ke gani a yau. Saboda haka, ba a samu wani bayani ko hukunci qarara
daga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ko
sahabbansa (Allah Ya yarda da su) da sauran malaman farko dangane
da ita ba. Wannan ya sa, a lokacin da taba sigari ta bayyana, malamai
sun yi qiyasin hukuncinta daga hukuncin albasa da tafarnuwa, waxanda
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya hana
duk wanda ya ci su, zuwa masallaci, saboda cutuwar da sauran mutane
da mala’iku (waxanda ke cikin masallacin) za su yi daga warin
bakinsu. Suka ba da fatawar cewa taba sigari makaruhi ne, wato, abin
qi, gwargwadon abin da suka fahimta game da ita, a wancan lokaci. Ke
nan, a wancan lokaci, malamai sun dubi hukuncin taba sigari ne daga
vangaren cutarwar da ta ke yi ga mutanen da ke kusa da mai shan
sigari, ba wai illarta ga wanda ke sha ba. Amma daga baya, binciken
likitanci ya tabbatar da cewa taba sigari na da illoli, da haxari ta fuskar
wanda ke sha, da dukiyarsa, da sauran jama’a. Nan take, malamai suka
tabbatar da haramcinta.
A taqaice, shan taba sigari haramun ne, ba makaruhi ba. Shan sigari
ya qunshi almubazzarancin dukiya, da sakarci wajen kashe kuxi, da
cutar da lafiya, da cutar da sauran mutane waxanda za su ji warinta a lokacin da a ke zuqa ko busa ta. Alqur’ani da Hadisi da Ijmā’i duk sun
nuna haramcin waxannan abubuwa gaba xaya. Haka nan ma, sayar da
taba ko sayo ta, duk haramun ne, domin kuwa yin hakan, ya qunshi
taimakawa a cikin savon Allah.
116
giya, ya tura xansa ya sayo masa, ko ya sanya shi ya
xauko masa daga wani wuri, don ya sha. Yaro zai taso a
haka, kuma ya riqa zaton cewa waxannan abubuwa babu
laifi a aikata su.
15. Lallai ne iyaye su koya wa `ya`yansu ladubban da suka
shafi cin abinci ko shan wani abu, da yin sallama, da
shiga cikin gida ko cikin xaki, da magana, da zama a
cikin jama’a, da atishawa, da hamma, da sanya takalmi,
da kwanciya da tashi daga barci, da shiga cikin
masallaci, da shiga ban xaki, da sauransu. Waxannan
ladubba na da matuqar muhimmanci. Ya kamata iyaye
su sansu, kuma su ilmantar da `ya`yansu. Su koya masu
wanke hannu, da faxin ‘Bismillah’, da amfani da hannun
dama a lokacin cin abinci ko shan wani abu. Idan sun
kammala kuma, su ce ‘Alhamdu Lillah’, daga nan su
wanke hannu. A umurce su da yin sallama kafin su shiga
gida ko xaki, da neman izni idan za su shiga xakin
iyayensu kafin sallar asuba, da tsakiyar rana da bayan
sallar isha’i. Su koya masu rufe baki da hannun dama
idan sun yi hamma, da rufe hanci da hannun hagu tare da
faxin ‘Alhamdu Lillah’ idan sun yi itishawa. A koya
masu shiga masallaci da qafar dama, da fita da qafar
Abin mamaki shi ne, har yanzu waxansu mutane ba su yin la’akari,
kuma ba su lura da haxarin taba sigari. Su kan yi biris da kiraye-
kirayen da malaman addini, da kuma likitoci ke masu, dangane da
illolin sigari. A nan qasar misali, duk lokacin da aka yi tallar taba a
rediyo ko talabijin, za a bayyana wa mutane cewa ‘ma’aikatar lafiya ta
tarayya na faxakar da mutane cewa shan taba sigari na da haxari ga
rayuwa, kuma yana gaggautar da mutuwar mutum.
Tare da wannan bayani, daga cikin ribar dimokaraxiya a Nijeriya,
akwai gayyato kamfanin tabar sigari mai suna British-AmericanTobacco Company (BATC) da gwabnati ta yi, don su ci
karensu ba babbaka. Abin da waxansu ba su sani ba, shi ne, kamfanin
BATC yana daga kamfanonin da aka koro daga Turai, saboda musiba
da bala’in da ya ke yaxawa a cikin jama’a.
117
hagu. Haka kuma, a koya masu shiga ban xaki da qafar
hagu, da fita da qafar dama. Sannan, a koya wa `ya`ya
addu’o’in da a ke yi idan za a shiga masallaci ko za a
fita, da addu’o’in kwanciya da tashi daga barci, da
waxanda a ke yi a lokacin shiga ban xaki ko fitowa, da
addu’ar fita gida, da wadda a ke yi idan za a shiga gida.
Bayan wannan, a umurci yara su gabatar da dama wajen
sanya takalmi da riga da wando. Kuma a hana su yin
tafiya da takalmi qafa xaya, kasancewar xabi’a ce ta
shaixan.193
Bugu da qari, a koya masu yanke qumba da
gyara gashin kai, da nisantar wuraren qazanta, da
qoqarin kawar da abubuwan da ke cutarwa a kan hanya.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya kasance yana koya wa qananan yara ladubban
addini. Misali, lokacin da Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ga hannun ‘Umar
ibn Abi Salamah (Allah Ya yarda da shi) yana kai-kawo
a cikin akushi, ya ce masa: ‚Ya kai yaro! Ambaci sunan
Allah (ka ce: ‘Bismillah’ idan za ka fara cin abinci),
kuma ka ci da (hannun) dama, kuma ka ci (abin da ke) gabanka.‛
194 Haka kuma, lokacin da ‘Abdur-Rahmān ibn
Sahl da Huwaisah da Muhaisah `ya`yan Mas’ūd (Allah
Ya yarda da su) suka zo wajen Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ‘Abdur-Rahmān
(wanda shi ne qaraminsu) ya yi nufin ya fara magana, sai
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Ka bar babba daga cikinku ya fara
magana.‛195
Kuma ya ce: ‚Na ganni a cikin barci
(mafarki) ina asuwaki, sai waxansu mutane biyu - xaya
daga cikinsu ya girmi xayan - suka zo wuri na. Sai na
miqa wa qaramin cikinsu asuwaki. Sai aka ce mani: ‘fara 193
Bukhari 194
Bukhari 195
Bukhari da Muslim
118
da babba’. Sai na miqa wa babban na su.‛196
Ke nan, ana
la’akari da fifikon shekaru idan falala da daraja cikin
ilmi da jagoranci suka zama iri xaya, kamar yadda Ibn Hajar ya tabbatar a cikin Fat-hul Bārī. Dangane da
sallama, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ya kasance yana yin sallama ga
qananan yara, kuma idan sun yi masa sallama, yana
amsawa, kamar yadda hadisai suka nuna.197
Yin haka,
zai sa yara su san muhimmancin sallama, da kuma
ladubban da ke tattare da ita.198
Dangane da neman izni
kafin shiga xaki a lokuta uku, waxanda Alqur’ani ya
bayyana199
, ‘Abdullah ibn ‘Umar da ‘Abdullah ibn
Suwaid (Allah Ya yarda da su) sun kasance suna hana
`ya`yansu shiga xakunansu a waxannan lokuta, ba tare
da izni ba.200
16. Iyaye su koya wa `ya`yansu ladubban amfani da dama da
hagu, da wuraren da a ke amfani da kowannensu, ko
kuma a ke gabatar da xaya kafin xayan. Bayani ya
gabata cewa ana amfani da hannun dama wajen cin
abinci ko shan wani abu. Haka kuma, ana fara amfani da
dama wajen shiga masallaci, da fita daga ban xaki, da
sanya takalmi, da sanya tufafi; kamar yadda a ke gabatar
196
Muslim 197
Bukhari da Muslim 198
Ba a yin sallama ga wanda ba musulmi ba, kamar yadda hadisai
ingantattu suka nuna. Idan kuwa su ne suka fara yin sallama ga
musulmi, shin zai amsa ko ba zai amsa ba? Idan zai amsa, wace siga zai
yi amfani da ita wajen amsawa? Magana mafi qarfi ita ce, zai amsa
sallamar yahudawa da kirista; kuma zai amsa masu da lafazin da ya
dace, matuqar sun yi amfani da sahihan kalmomi wajen yin sallamar,
kuma bisa yadda Shari’ah ta tabbatar da lafazin. Duba littafin Ibnul Qayyim, Ahkāmu Ahliz Zimmah, shafi na 149 don qarin bayani. 199
Nūr, 24:58 200
Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī, Sahīh al-Adabil Mufrad #803 da
808
119
da hagu wajen fita daga masallaci, da shiga ban xaki.
Bayan waxannan, an so a yi amfani da dama cikin duk
wani abu mai kyau da tsafta, kamar sanya zobe ko
agogo, da kwanciya, da miqa wani abu ko karvar wani
abu. A wajen abubuwan qazanta kuwa, kamar wanke
bayan gida (kashi) ko fitsari, an so a yi amfani da hannun
hagu. Idan za a yi aski ko yanke qumba ko gyara suma
(gashin kai) ko wankan tsarki, an so a fara da vangaren
dama kafin hagu.
Hadisi ya tabbata cewa Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) yana gabatar da dama wajen
cin abinci, da shan abin sha, da alwalla, da sanya tufafi,
da miqawa, da karva. Yana amfani da hagu cikin sauran
abubuwa.201
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Idan xayanku zai ci
abinci, to ya ci da (hannunsa na) dama, kuma ya sha da
dama, kuma ya karva da dama, kuma ya miqa da dama;
domin shaixan na ci ne da hagu, kuma yana sha da hagu,
kuma yana ba da wa da hagu.‛202
Dangane da tsarki,
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Idan xayanku zai yi fitsari, kada ya riqe
zakarin shi da (hannun) dama. Kuma idan ya shiga ban
xaki, kada ya yi amfani da (hannun) dama wajen
tsarki.‛203
A wata ruwayar: ‚Idan xayanku zai yi tsarki,
kada ya yi amfani da (hannun) dama; ya yi amfani da
(hannun) hagu wajen tsarkinsa.‛204
Dangane da sanya
201
Ahmad: Sahīh [Duba littafin Muhammad Jamīl Zainū, Quxūf min as-Shamā’il al-Muhammadiyyah, shafi na 88; da Sahīh al-Jāmi’ ,
#4912 na Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī] 202
Ibn Mājah da al-Hasan ibn Sufyān: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #384; da as-Sahīhah #1236] 203
Ahmad, Bukhari, Muslim, Abu Dāwud da Tirmidhi [Duba Sahīh al-Jāmi’ #410] 204
Baihaqī, Ahmad da Abu Dāwud: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #322]
120
takalmi, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) ya ce: ‚Idan xayanku zai sanya takalmi, ya
fara da (qafar) dama; kuma idan zai cire, to ya fara da
(qafar) hagu: qafar dama ta zamanto ita ce farko wajen
sanyawa, amma ta zamanto a qarshe wajen cirewa.‛205
A
cikin wani hadisin, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Ka cire (takalmanka)
gaba xaya, ko ka sanya su gaba xaya; kuma idan za ka
sanya, ka fara da dama; idan kuma za ka cire, ka fara da
hagu.‛206
Dangane da kwanciya, Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚… sannan ka
kwanta a tsagin jikinka na dama…‛207
Dangane da
wanka, da gyaran suma (gashin kai), hadisi ya tabbata
cewa Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) yana sha’awar farawa da (vangaren) dama
wajen sanya takalmi, da gyara sumarsa, da wanka.‛208
Dangane da alwala, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Idan za ku sanya
tufafi ko za ku yi alwala, ku fara da (vangaren) dama.‛209
Dangane da shan ruwa, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya hana shan ruwa a tsaye.210
17. Lallai ne iyaye su ilmantar da `ya`yansu game da
haqqoqin zamantakewa, musamman haqqoqin iyaye, da
`yan’uwa, da shugabanni, da maqwabta, da sauran
musulmi. Kafin wannan, wajibi ne iyaye su sanar da
`ya`yansu haqqoqin Allah (Mai girma da xaukaka) da
haqqoqin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
205
Ahmad, Muslim, Abu Dāwud da Tirmidhi 206
Ibn Hibbān: Sahīh 207
Bukhari da Muslim 208
Bukhari da Muslim 209
Abu Dāwud da Ibn Hibbān: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #787] 210
Bukhari
121
tabbata a gare shi), kasancewar su ne mafi girman
haqqoqi a kan kowane mutum.
Haqqoqin Allah (Mai tsarki da xaukaka) a kan bayinSa
guda bakwai (7) ne: (1) imani da Shi a vangaren
rububiyyah da uluhiyyah da sunayenSa mafi kyawu da
siffofinSa mafi xaukaka211
(2) tsarkake bauta gare Shi
(3) bin umurninSa da barin haninSa (4) girmama Shi da
tsarkake Shi daga dukkan aibobi da tawaya, da girmama
umurni da haninSa, da tsayuwa a inda Ya iyakance (5)
bauta Masa a bisa asasin soyayya da tsoron azabarSa da
kwaxayin rahamarSa (6) gode maSa bisa ni’imominSa,
ta hanyar yarda da qudurce cewa dukkan ni’ima daga
gare Shi ta ke, kuma da bayyanar da ni’imar a fili, tare
da yabonSa a kanta, da sarrafa ni’imar, tare da juyar da
ita zuwa ga abin da Ya ke so (7) sallama wa qaddararSa
da yarda da duk abin da Ya hukunta.
Haqqoqin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) a kan al’ummarsa guda bakwai (7) ne:
(1) gasgata shi a cikin abin da ya ba da labari, da bin
umurni da haninsa, da imanin cewa shiriyarsa da Shari’ar
da ya zo da ita su ne mafi cika da dacewa (2) gabatar da
shi da fifita shi a kan kowa (3) mai da shi abin koyi (4)
ladabi a gare shi, da ladabi ga Sunnarsa (5) kare
martabarsa, da kiyaye matsayi da mutuncin sahabbansa
da matansa da sauran iyalan gidansa (6) kare Sunnarsa
da yaxa ta (7) yawaita salati a gare shi.212
211
Karanta littafina, The Most Beautiful Names of Allāh from the Qur’ān and Authentic Sunnah, domin qarin bayani game da sunayen
Allah. 212
Allah (Maxaukaki) Ya bayyana cewa Shi da mala’ikunSa suna yin
salati ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), kuma Ya umurci muminai da yin salati a gare shi [Ahzāb, 33:56].
Sahabbai (Allah Ya yarda da su) sun tambayi Manzon Allah (tsira da
122
amincin Allah su tabbata a gare shi) game da yadda za su yi masa
salatin da Allah (Mai girma da xaukaka) Ya umurci muminai su yi.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce, ‘Ku
ce:
Wannan yana nuna cewa babu wani salatin Annabi (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) da ya kai inganci, da matsayi, da falala, da
darajar wannan nau’in da ya karantar da sahabbansa (Allah Ya yarda da
su). Hadisai ingantattu sun tabbatar da sigogi guda bakwai na wannan
salati. Ana iya karanta kowace siga daga cikinsu a sallar farilla ko ta
nafila. Sigogin da suka tabbata daga bakin Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) kai tsaye su ne:
Idan kuwa ba a cikin salla ba ne, waxansu malamai sun ba da
fatawar halaccin karanta kowane irin salati ga Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi), matuqar yana da lafazi mai daxi,
da ma’ana mai kyau, kuma ba a fifita shi, ko aka daidaita shi da
waxanda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ya karantar da kansa ba. Sun dogara da sigogin salati da aka ruwaito
123
cewa Ibn Mas’ud da Aliyyu ibn Abi Xālib da waxansu daga cikin
tabi’ai da atbā’ut tābi’īn suna yi, maimakon waxannan sigogi da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
karantar.
Salati ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) na da falala da fa’idodi masu yawan gaske. Ibnul Qayyim, a cikin Jilā’ul Afhām fis Salāti Wassalāmi ‘ala Khairil Anām, (Al-Maktabatut
Taufīqiyyah, Egypt), shafi na 284-291, ya bayyana fa’idodi da falalar
salati har guda arba’in (40). Daga cikinsu, akwai: (1) biyayya ga
umurnin Allah (2) yin muwafaqa da Allah a cikin salati, duk da cewa
salatin Allah yana da bambanci da salatin mutane (3) yin muwafaqa da
mala’iku a cikin salati (4) dacewa da lada guda goma (5) samun
xaukakar daraja sau goma (6) dacewa da saryarwar laifuffuka guda
goma (7) qaunar amsa addu’ar da aka fara gabatar da godiya da yabo
ga Allah, da salati ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi) (8) dalilin samun ceto a ranar qiyama (9) dalilin samun
kusanci ga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
a ranar qiyama (10) kuvuta daga kaucewa hanyar aljanna (11) dacewa
da mai da gaisuwa daga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) (12) kuvuta daga wari da xoyi (13) kuvuta daga
addu’ar turmuje hanci da nisantarwa daga rahama (14) kuvuta daga
hasara da nadama (15) dalili ne na korewar baqin ciki da damuwa da
tsanani (16) dalili ne na dawwamar soyayyar Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) (17) hanya ce ta sauke mafi
qaranci daga cikin haqqoqin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) a kan mabiyansa.
Akwai lokuta da wuraren da aka wajabta yin salati ga Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), kuma akwai wurare da
lokutan da yin salati mustahabbi ne. Wuraren da aka fi son a yi salati ga
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), a matsayin
wajibi ko mustahabbi sun haxa da: (1) bayan tahiyar qarshe a cikin
sallolin farilla ko sallar nafila (2) bayan tahiyar farko (3) a cikin sallar
jana’iza bayan kabbara ta biyu (4) a cikin huxubar Juma’a ko Idi ko
roqon ruwa (5) bayan kwaikwayon mai kiran salla (6) a wajen addu’a
(7) lokacin shiga masallaci da lokacin fitowa daga cikinsa (8) lokacin
da mutane suka zo tashi daga wani majalisin da suka zauna (9) a duk
lokacin da aka ambace shi (10) ranar Juma’a (11) lokacin baqin ciki da
damuwa da tsanani.
124
Haqqoqin iyaye a kan `ya`yansu guda shida (6) ne: (1)
kyautata masu, da yin masu xa’a a cikin abin da bai sava
wa Shari’ah ba (2) tausasa magana da yin tawali’u a gare
su, da saurarensu a lokacin da su ke yin magana, da
rashin qosawa ko nuna gajiya ga maganarsu, da rashin
xaukaka murya a kan ta su (3) yin addu’a a gare su,
musamman bayan mutuwarsu, da rashin jawo dalilin
tsinuwa a gare su (4) sadar da makusantarsu da
abokansu, musamman bayan rasuwarsu (5) rashin
kiransu da sunayensu, ko zaunawa a wuri kafin su zauna
ko yin tafiya a gabansu (6) ilmantar da su, da yin masu
nasiha, a bisa fuska mafi dacewa.
`Yan’uwa da maqwabta na da haqqoqin da Shari’a ta ba
su. Haqqoqin `yan’uwa makusanta da `yan’uwa na nesa
guda biyu (2) ne: (1) sadar da zumunci, da rashin yanke
zumuntarsu (2) fifita su a kan sauran mutane wajen
kyauta da sadaka da zakka da jawo amfani.
Maqwabci na da haqqoqi guda uku (3) a kan
maqwabcinsa: (1) rashin cutar da shi (ta hanyar magana
ko aiki), ko cin mutuncinsa, ko vata wani abu da ya
mallaka (2) girmama shi, gwargwadon yadda Shari’a ta
ce (3) kyautatawa a gare shi. Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya bayyana cewa
mutumin da maqwabcinsa bai amintu daga sharrinsa ba,
bai da cikakken imani.
Shugabanni na da haqqoqi a kan waxanda su ke yi wa
shugabanci, kamar yadda a ke da haqqoqi a kansu.
Haqqoqin shugabanni guda shida ne a kan jama’arsu: (1)
kyautata wakilci gare su a duk lokacin da suka sanya
wakili (2) yin addu’ar shiriya da kyakkyawar jagoranci
gare su (3) tausasawa gare su a cikin magana da
mu’amala (4) yin masu xa’a cikin abin da bai sava wa
125
Shari’a ba (5) taimakonsu wajen sauke nauyin da aka
xora masu (6) yin haquri a kan cutarwar da za ta zo ta
hanyarsu.
Waxanda a ke yi wa shugabanci na da haqqoqi guda
biyar: (1) kiyaye masu larurori guda biyar ( ),
wato, addini, da rayuwa, da dukiya, da mutunci, da
hankali (2) yin masu adalci (3) tausasawa gare su da
qoqarin jawo masu amfani da tunkuxe cuta gare su (4)
rashin ha’intarsu da yaudararsu da satar dukiyarsu ko yin
almubazzaranci da ita (5) rashin shamakancewa daga
gare su (6) neman shawara daga zavavvun cikinsu kafin
a zartar da hukunci a kan muhimman abubuwan da suka
shafe su
Kowane musulmi na da haqqoqi guda goma sha uku
(13) a kan xan’uwansa musulmi: (1) yin masa sallama
idan sun haxu (2) amsa gayyatarsa, matuqar babu larurar
da za ta hana, kuma babu savon Allah a wurin (3) yin
masa nasiha, da basa shawara mai kyau idan ya nema (4)
faxin yarhamukallah idan ya ce Alhamdu Lillah bayan
ya yi atishawa (5) gaishe shi idan ya yi rashin lafiya (6)
halartar jana’izarsa idan ya mutu (7) kuvutar da shi a kan
rantsuwar da ya yi (8) rashin yin hijira daga gare shi (9)
tsare harshe da idanu daga cutar da shi (10) mutunta shi
da rashin cutar da shi, ta hanyar magana ko aiki (11)
taimakonsa ta kowace hanyar da ta dace, gwargwadon
iko (12) yin masa da’awa.
Karantar da `ya`ya waxannan haqqoqi, da nuna masu
wajibcin kiyaye su yadda ya kamata, za su taimaka
wajen tarbiyyar da ta shafi zamantakewa. Idan `ya`ya
suka taso a kan wannan turba, babu shakka, za a samu
zaman lafiya, da walwala, da kwanciyar hankali, da
martaba juna a cikin al’umma. Haka kuma, ana sa ran
126
irin waxannan `ya`ya za su zamanto masu son
`yan’uwansu Musulmi, da nuna qauna da haxin kai, da
tabbatar da `yan’uwantakar Musulunci,213
da nisantar
213
`Yan’uwantaka ita ce mafi girma daga cikin ginshiqan da Musulunci
ya dogara kansu wajen gina al’umma. Lokacin da Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya samar da al’ummar farko a
Madina, ya mai da `yan’uwantaka a matsayin ginshiqi na biyu, bayan
tabbatar da kaxaituwar manufa ta hanyar gina masallacin Quba.
`Yan’uwantaka wata irin alaqa ce da ke tsaye a bisa asasin imani da
Allah (Maxaukaki), domin kuwa imani ne ya haxa tsakanin muminai.
Musulunci ya girmama `yan’uwantaka, kuma ya qarfafata, sannan ya
tabbatar da kyakkyawar sakamako a nan duniya da can lahira ga
waxanda suka tabbatar da ita.
Allah (Maxaukaki) Ya ba da labarin aukuwar `yan’uwantaka a tsakanin muminai [Hujurāt, 49:10]; Ya sanya `yan’uwantaka a
matsayin ni’imar da Ya ke yi wa bayinSa gori a kanta [Aal Imrān,
3:103]; Ya sanya ta a matsayin dalilin da zai sa Allah (Maxaukaki) Ya so bawansa [Muslim; Mālik da Ahmad]; Ya sanya ta a matsayin igiyar
imani mafi qarfi [Bazzār]; Ya sanya matsayin masoyi iri xaya da na
wanda a ke so [Muslim]; Ya tabbatar da lada mai yawan gaske ga
waxanda suka tabbatar da `yan’uwantakar Musulunci a tsakaninsu
[Muslim]; Ya sanya ta a matsayin dalilin samun lagwadar imani
[Bukhari da Muslim] da kai wa ga kammalallen imani [Abu Dawud]
wanda ke kai mutum ga shiga aljanna [Muslim da Abu Dawud da
Tirmidhi], da samun matsayin da ya fi wanda mutum ya cancanta
[Bukhari da Muslim].
`Yan’uwantaka na da sharuxxa guda huxu: (1) ta kasance saboda
Allah (2) gwama ta da imani da taqawa (3) lazimtar manhaji da tsarin
Musulunci wajen tabbatar da ita (4) gina ta a bisa asasin nasiha ga
Allah da bayinSa.
Musulmi za su iya tabbatar da `yan’uwantaka a tsakaninsu, kuma su
qarfafeta ta waxannan hanyoyi: (1) idan mutum yana son wani, ya
sanar da shi; (2) idan zai yi balaguro, a nemi ya yi wa `yan’uwansa
Musulmi addu’a, a kan hanya (3) idan ya haxu da xan’uwansa
Musulmi a wani wuri, ya sakar masa fuska; (4) idan ya haxu da
Musulmi, ya yi gaggawar yin masu sallama, da yin musafaha da su; (5)
yawaita ziyara lokaci zuwa lokaci; (6) taya murna a lokacin farin ciki,
da yin jaje a lokacin baqin ciki; (7) taimakekeniya, musamman a
lokacin tsananin buqata; (8) kiyaye wa juna haqqoqin `yan’uwantaka.
127
yawan savani.214
Haka kuma, ana fatan cewa `ya`yan da
suka taso a kan irin wannan tarbiyya za su zamanto masu 214
Savani shi ne rashin daidaituwa a kan al’amarin addini, da ya ke da alaqa da asalin addini (usūluddīn) ko reshe (furu’ah). Idan savanin yana
da alaqa da asalin addini ne, wato, kamar mas’alolin tauhidi da aqida,
ana kiransa , kuma shi ne mafi sharrin nau’o’in savani. Idan kuwa
yana da alaqa ce da furu’a, wato, kamar mas’alolin fiqihu, ana kiransa
ko ko .
Savani a tsakanin Musulmi wani abu ne da aka qaddara, kuma dole
ne ya auku. Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ce: ‚Kuma da
Ubangijinka Ya so, da Ya sanya mutane al’umma xaya. Kuma ba za su
gushe ba suna masu sava wa juna. Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa
rahama, kuma domin wannan ne Ya halicce su…‛ [Hud, 11:118-119].
Kuma Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
bayyana cewa ya roqi Allah (Maxaukaki) kada Ya sanya savani a
tsakanin al’ummarsa, amma Allah bai amsa ba [Muslim]. Haka kuma,
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya tabbatar
da cewa al’ummarsa za ta kasu gida saba’in da uku (73), kashi saba’in
da biyu (72) daga cikinsu `yan wuta ne [Abu Dawud da Ahmad].
Duk da cewa aukuwar savani dole ne a cikin wannan al’umma, an
nemi musulmi da yin riqo da sabubban da za su kawo qarshen duk
wani irin savani a tsakaninsu, domin su zamanto al’umma guda xaya,
wadda za ta yi gwagwarmayar tabbatar da dokokin Allah da tsare-tsarenSa a doron qasa [Anbiyā, 21:92]. Wannan ya sa Allah
(Maxaukaki) Ya umurce mu da haxin kai, da yin riqo da igiyarSa, kuma Ya hana mu rarraba, wadda savani ke haifarwa [Aal Imrān,
3:103]. Ya bayyana mana cewa jayayya da savani na haifar da rauni da rashin qarfi a gare mu [Anfāl, 8:46]. Ya tsawatar da mu daga bin
hanyar waxanda suka rarraba, suka yi savani a tsakaninsu [Aal Imrān,
3:105], kasancewar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ba shi a kan irin wannan hanya [An’ām, 6:159], domin kuwa
son rarraba, da kuma son yin savani na daga cikin xabi’un mushrikai [Rūm, 30:31-32]. Haka kuma, Allah (Mai girma da xaukaka) Ya
shar’anta mana bin addini sahihi, wanda aka yi wa Annabawa da Manzanni wasiyya da shi [Shūrā, 42:13].
Savani ya kasu gida biyu: abin zargi ( ) da wanda babu zargi (
). Savanin da a ke yin zargi a kansa na da fuskoki guda huxu:
1. Savani a cikin mas’alolin aqida waxanda aka yi ittifaqi a kansu a
tsakanin ahlus-sunnah wal jamā’ah ( ). Idan kuwa
128
mas’alolin da ba a yi ittifaqi a kansu ba ne, saboda rashin hujjoji
qaxa’i, babu zargi a kansu, matuqar ba an karkata ga son zuciya ba.
Irin wannan nau’in, kamar yadda Ibn Taimiyyah ya bayyana a cikin littafin Majmū’ul Fatāwā, ya haxa da (i) zai yiwu mamaci ya ji
muryar waxanda ke raye? (ii) shin ana azabtar da mamaci a cikin
qabarinsa saboda kuka ko kururuwar iyalansa a dalilin mutuwarsa?
(iii) shin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ga Ubangijinsa kafin ya bar duniya? Kasancewar babu
ittifaqin magabata a kan waxannan mas’aloli, savani a cikinsu ba
ya jawo zargi ko inkari a tsakanin Musulmi, matuqar ba a gina
savanin a kan son zuciya ba. Amma babu laifi mutum ya yi qoqarin
gamsar da abokin savaninsa game da fahimtar da ta fi qarfi, da
fatawar da ta fi rinjaye a tsakanin malamai, gwargwadon binciken
da ya yi, da kuma hujjojin da ya dogara da su. Yin bayanin hujjoji,
da kuma rinjayar da fahimtar da ta fi qarfi, ba xaya ya ke da yin
inkari ba.
2. Savani a cikin mas’alolin da suka tabbata bisa dalilan da babu
kace-nace a kansu, kamar rukunan musulunci, da haddin sata, da
wajibcin sanya hijabi ga mata, da haramcin shan giya.
3. Duk wani savani da ke aukuwa a dalilin alfahari da qabila ko
qungiya ko mazhaba, da son zuciya.
4. Sava wa abin da al’umma ta yi ijma’i a kan shi.
Savanin da babu zargi a kan shi yana da alaqa ce da mas’alolin
furu’a, kuma ya kasu gida biyu:
1. Savanin da ke zuwa a dalilin nassosin da ba su yi karo da juna ba,
amma sun qunshi siffofi ko adadi ko lokaci dabam daban. Irin
wannan savanin a cikin nassosi ana kiran shi savanin nau’o’i (
). Misalinsa ya haxa da: siffar yadda a ke kiran salla da iqama;
da sigogin tahiyya da sallamewa daga salla da salatin Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi); da sigogin
addu’ar da a ke yi kafin a fara karatun salla bayan an yi kabbarar
harma; da nau’o’in azkarun da a ke yi a cikin ruku’u da sujuda; da
adadin tasbihi da a ke yi bayan sallar farilla; da siffofin sallar tsoro;
da adadin kabbarbarin da a ke yi a sallar jana’iza; da siffar yadda a
ke yin ishara da yatsa a wajen tahiya.
2. Savanin da ke zuwa a cikin nassosin da suka yi karo da juna, kuma
babu yadda za a yi a haxa su gaba xaya. Irin wannan savanin ana
kiran shi savanin da ke kishiyantar juna ( ). Misalinsa ya
129
haxa da: wajen da a ke yin ibadar i’itikafi; da hukuncin yin azumin
nafila a ranar Asabar; da hukuncin yin azumin arfa ko azumin
ashura idan ya kasance ranar Juma’a ko Asabar.
Savani irin wannan ba a yin zargi a kansa, matuqar ba a gina shi a
kan son zuciya ko yin yadda aka so ba. Hasali ma, irin wannan savani,
yana nuna yalwar addini ne idan ya shafi , ko kuma rashin
dalilin da a ke kira , domin kuwa sahabban Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sun yi savani a kan irin
waxannan mas’aloli na furu’a, saboda bambancin fahimta, da rashin
yiwuwar kiyaye dukkan maganganu da ayyukan Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) a xaixaikunsu, ko kuma saboda
bambancin ijtihadi a wajen da babu nassi qarara. Duk da cewa ba a yin
zargi a cikin irin wannan savani, hakan ba ya nuna cewa ba za a yi wa
juna nasiha a kan abin da ya fi dacewa ba. Ya kamata a yi nasiha, tare
da faxakarwa ga juna a kan fahimtar da ta fi qarfi, da kuma fatawar da
ta fi rinjaye. Haka kuma, za a iya xaukar hujjojin wanda aka yi savani
da shi a kan mas’alar, don a bayyana rauninsu, ko rashin dacewarsu.
Abin da Shari’a ta hana shi ne aibanta juna ko cin mutuncin juna a
dalilin irin wannan savani.
Dalilan da ke kawo savanin da ba a yarda da shi ba, wato, ,
musamman a cikin mas’alolin aqida, sun haxa da:
1. Makircin abokan gaba, kamar yadda Yahudawa irinsu
Abdullah ibn Saba’in suka haifar da qiyayya da gaba a tsakanin
musulmi, tun daga lokacin da aka samu savani a tsakanin Aliyyu ibn Abi Xālib da Mu’āwiyyah (Allah Ya yarda da su).
2. Jahiltar addinin musulunci, da qa’idodinsa, da usūl xin da a ke
bi wajen tabbatar da hukunce-hukunce.
3. Varaka a cikin hanyar da a ke bi wajen fahimtar addini (
), musamman idan aka nemi fahimtar Alqur’ani ko Sunnah
a bisa savanin yadda sahabbai da tabi’ai da sauran magabata na
qwarai suka fahimta.
4. Tsanantawa, da zurfafawa, da son wuce gona da iri a cikin
addini.
5. Bidi’a, da qage a cikin sahihiyar aqida, kamar yadda aka samu khawārij da murji’ah da mu’utazilah sun qago sababbin
abubuwa, kuma sun sava wa fahimtar sahabban Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).
130
6. Tasirantuwar da waxansu musulmi suka yi ga tunani da kuma
falsafar da ke gangarowa daga qasashen kafirai, da kuma
mummunar farfagandar maqiyan Musulunci.
7. Barin da’awa, da kuma yin sakaci a kan neman ilmin addini.
Shi kuwa , wato, savanin furu’ah, dalilan da ke kawo shi sun
haxa da: kasancewar xan Adam mai kuskure ne tun asali, don haka
babu mamaki idan ya sava wa waninsa bisa kuskure; da zalunci, da
qiyayya, da qin gaskiyar da ke kai mutane ga yin jayayya da qin karvar
gaskiya; da hassada, da girman kai; da ta’assubanci ga waxansu mutane
ko qungiya; da vacin tunani, da raunin tasawwuri; da lazimta wa
mutane abin da ba ya lazimtuwa, domin a cinma wata manufa; da son
yin savani domin a samu shahara; da bin son rai, da qoqarin biye wa
zuciya; da qarancin bincike a cikin littafan magabata; da qarancin
fahimtar , wato, hukunce-hukuncen savani, da yadda a ke yin
mu’amala da abokin savani; da kuma bidi’a a cikin addini, da nacewa
wajen qoqarin kare ta, da tallata ta, tare da qoqarin ciyar da ita gaba.
Alqur’ani da Sunnah sun karantar da ladubban da suka dace a
kiyaye a kan waxanda suka yi savani. Ladubban sun haxa da:
1. Ikhlasi, da koyi da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) da sahabbansa wajen mu’amala da wanda
aka yi savani da shi ( ).
2. Fatar shiriya, da dawo wa hanyar qwarai ga wanda ya sava wa
gaskiya.
3. Sauraron hujjar wanda aka yi savani da shi, da kuma ba shi
damar kawo fahimtarsa a kan mas’alar.
4. Ba da dalili da hujja a kan mas’alar da aka yi savani game da
ita, ba wai amfani da ra’ayi ko ta’assubanci ba.
5. Tausasawa wajen tattaunawa, da kuma mai da martani a cikin
natsuwa. 6. Tawāli’u, da qanqan da kai wajen raddi, matuqar yin hakan ba
zai haifar da qasqanci ba.
7. Mai da hukunci zuwa ga Alqur’ani da Sunnah a bisa fahimtar
magabata na qwarai, musamman sahabbai da tabi’ai da tabi’ut-tābi’in.
8. Zuwa ga na gaba wajen ilmi da fahimta domin ya warware
mas’alar, idan ba a samu fahimta ba a tsakanin masu savani.
131
kulawa da haqqoqin Musulmi, kuma masu son zaman
lafiya da jawo amfani ga al’umma.
18. Wajibi ne iyaye su riqa tausasawa ga `ya`yansu, tare da
nuna masu qauna da rashin gajiya ko qosawa da su,
musamman idan sun yi tambaya a kan abin da ba su sani
ba. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya ce: ‚Mafi alhairin mata a cikin larabawa, su
ne matan quraishawa: (kasancewar) su ne mafi
tausasawa (da nuna qauna) ga `ya`ya a lokacin da su ke
9. Tantance nau’in savani, ta yadda za a bambance a tsakanin
wanda ke da alaqa da aqida, da kuma wanda ya shafi furu’a, ko
kuma wanda a ke da hujja qarara a cikin nassi, da kuma wanda
babu hujja qarara, kasancewar kowannensu na da yanayinsa
daban.
10. Adalci ga abokin savani, ko da kuwa maqiyi ne mabayyani.
11. Kyautata zato ga abokin savani a tashin farko, kasancewar
akwai yiwuwar ya yi kuskure ne, amma bisa kyakkywar niyya
ko kuma qoqarin fahimtar gaskiya.
12. Yin mu’amala da abokin savani irin yadda a ke son shi ma ya
yi mu’amalar.
Domin rage yawan savani a tsakanin Musulmi, musamman a cikin
mas’alolin aqida, dole ne a bi hanyoyin da Shari’a ta tanadar, waxanda
suka haxa da:
1. Yin kowane abu domin Allah, ba tare da yarfiya ko qazafi ko
qage ba ga abokan savani, ko kuma yin abu don kawai a vata
masu rai.
2. Riqo da Alqur’ani da Sunnah bisa fahimtar magabata na
qwarai, da kuma xabbaqa hukunce-hukuncensu a cikin adini da
rayuwa gaba xaya.
3. Bin hanyar magabata na qwarai da qoqarin fahimtar addini irin
yadda suka fahimta.
4. Koyon karatu daga waxanda suka dace, da kuma nisantar
girman kai ga dukkan musulmi.
5. Kwaxayi da kuma fatan shiriya da samun dacewa ga kowane
musulmi.
132
qanana.‛215
An so iyaye su riqa sumbantar `ya`yansu, da
yin masu wasa, da shafa kansu, da xora su a kan cinya
ko qirji, da yawaita yin masu addu’a. Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance
yana sumbantar yara,216
yana rungume su,217
yana yin
masu wasa,218
yana xaukarsu ya xora a kan cinya219
ko
qirji,220
yana shafa kan yara,221
musamman marayu,222
kuma yana yi wa yara addu’ar Allah Ya sanya masu
albarka.223
Haka kuma, ya kasance ya kan xora hannunsa
a kan kafaxar yara, idan zai yi masu magana.224
Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
kasance yana yin waxannan abubuwa ne ga yara saboda
tausayawa da tausasawa da girmamawa da nuna qauna
gare su. Hasali ma, Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ya nuna cewa rashin
sumbantar `ya`ya, alama ce ta rashin tausayi da jin qai
gare su.225
Amma waxannan abubuwan da aka bayyana, ba su nuna
cewa iyaye su qyale `ya`yansu haka nan sakaka, ba tare
da yin masu tarbiyya ba. Dole ne iyaye su ladabtar da
`ya`yansu, kuma su riqa kwavonsu a duk lokacin da suka
ga sun karkace hanya. Ba shi daga qauna ko tausasawa
ko soyayya, a bar `ya`ya ba tare da ladabi, da sanin ya
kamata ba. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
215
Muslim 216
Bukhari da Muslim 217
Bukhari a cikin al-Adabul Mufrad: Sahīh 218
Bukhari da Muslim 219
Bukhari da Muslim 220
Bukhari da Muslim 221
Bukhari 222
Ahmad: Hasan 223
Ahmad, Bukhari da Muslim 224
Bukhari 225
Bukhari
133
tabbata a gare shi) bai tava ganin yaro ya yi wani abin da
ba dai dai ba, face ya shiryar da shi zuwa ga dai dai, ko
ya kwave shi. Wannan ya sa, a lokacin da aka kawo
zakkar dabino wajen Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), al-Hasan ibn Ali (Allah Ya
yarda da shi) ya xauki xaya ya sanya a bakinsa don ya ci.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) yana ganinsa, sai ya ce masa: ‚Kikh, kikh,226
don ya
fito da shi (daga bakinsa)‛. Sannan ya ce: Ba ka san (mu banu Hāshim da banu Abdil-Muxxalib) ba mu cin
sadaka ba?‛227
Haka kuma, a lokacin da Zainab bint Abi Salamah
(Allah Ya yarda da ita)228
ta shiga wajen Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) alhali yana
wanka, ya xebi ruwa a hannunsa ya watsa mata a fuska,
kuma ya ce: ‚Tafi ki bani wuri, sakaryar yarinya!‛229
Bayan wannan, hadisi ya tabbata cewa, lokacin da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ga hannun ‘Umar ibn Abi Salamah (Allah Ya
yarda da shi) – a lokacin yana yaro – na yawo a cikin
akushin abinci, sai ya ce masa: ‚Kai yaro! Ka ce:
Bismillah, ka ci da (hannun) dama, kuma ka ci
gabanka.‛230
Bugu da qari, lokacin da Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ga al-Fadl ibnul Abbās (Allah Ya yarda da shi) na kallon wata
mace, ita ma tana kallonsa (a lokacin aikin hajji), sai ya
226
Kalmar farisanci wadda ke nuna tsawatawa da neman a bar abin da a
ke aikatawa 227
Bukhari da Muslim 228
A lokacin tana qarama 229
Xabarāni: Hasan 230
Bukhari
134
riqa juyar da fuskarsa, don gudun kada ya ci gaba da
kallonta.231
A taqaice, soyayya da qaunar da ya kamata iyaye su
nuna wa `ya`yansu ba su nufin a bar `ya`ya ba tare da
jawo hankali da kwavo ba, a duk lokacin da buqatar
haka ta taso. Wajibi ne iyaye su tabbatar da cewa
`ya`yansu sun samu kyakkyawar tarbiyya, ta hanyar
kwavo, da jawo hankali, da nasiha, da tsawatarwa, da
nuna fushi, da tsoratarwa, da kau da fuska, wani lokaci
ma, har da duka, gwargwadon yadda ya dace. Illa iyaka,
dole ne a lura da abin da ya fi dacewa a duk lokacin da
buqatar yin wani abu ta taso. Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance idan ya ji
wani daga cikin mutanen gidansa (babba ko yaro) ya faxi
qarya, yana kau da fuskarsa daga gare shi (don nuna
masa vacin rai) har sai (wanda ya yi qaryar) ya tuba.‛232
Haka kuma, ya yi umurni da dūkan yara idan suka qi yin
sallar farilla, daga shekara goma.233
Don haka, lallai ne iyaye su sanya ido sosai game da
al’amuran `ya`yansu. Yana daga abin takaici, ka ga
waxansu iyayen sun yi biris da `ya`yansu, a lokacin da
su ke abubuwan da bai dace ba. Misali, uwa ko uba na
kallon yara suna cin abinci da hannun hagu, ko a ji suna
zage-zage, amma ba za a kwava masu ba, wai da hujjar
cewa qananan yara ne; ko kuma a ji suna yawaita
rantsuwa, ko suna rantsuwa da sunan wanin Allah, kamar kwarankwatsa, ko tarnatsa, ko yāsin, ko qabarin
tsoho, ko rawanin tsoho, amma a qyale su, saboda wai
yara ne. To wannan dai ba qauna ba ce a ma’aunin
231
Bukhari da Muslim 232
Ahmad da Hākim: Sahīh [Duba Sahīh al-Jāmi’ #4675 da as-Sahīhah
#2051] 233
Abu Dāwud da al-Bazzār: Sahīh
135
Shari’a. Bayani ya gabata cewa Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance mai
tausasawa, da nuna qauna, da soyayya, da jin qai ga
qananan yara. Amma duk da haka, ba ya barinsu, ba tare
da ladabtarwa ko faxakarwa ba, idan ya ji/ga sun yi abin
da ba daidai ba. Wannan ne ma ya sa Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ‚Ku
rataye bulala a wajen da iyalinku za su riqa gani, domin
kuwa (yin haka) ladabi ne a gare su.‛234
19. Wajibi ne iyaye su nisantar da `ya`yansu daga abokan
banza don gudun kada su koyi munanan xabi’u daga
gare su. Babu shakka, Musulunci ya ba abota da
qawance muhimmanci sosai, saboda irin tasirin da su ke
da shi a cikin rayuwar mutane.
Allah (Maxaukaki) Ya yi umurni da a lazimci masu
gaskiya;235
Ya zaburar da muminai a kan yin abota da
mutanen da ke yawaita ibada;236
Ya kwaxaitar da bin
hanyar waxanda ke komawa gare Shi;237
Ya hana yin
abota da azzalumai, saboda yin hakan, na haifar da
nadama, da hasara a lahira;238
Ya sanya sakamakon
abotar da ba a gina ta a kan asasin taqawa ba, shi ne,
samun qiyayya a tsakanin abokai;239
kuma Ya tsawatar
game da yin abota tare da wanda ya bar hanyarSa.240
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Mutum yana kan addinin (halaye da xabi’un)
234
Xabarāni, da Khaxīb da Ibn Asākir: Hasan [Duba as-Sahīhah #1447;
da Sahīh al-Jāmi’ #4022] 235
Taubah, 9:116 236
Kahf, 18:28 237
Luqmān, 31:15 238
Furqān, 25:28 239
Zukhruf, 43:67 240
Najm, 53:29
136
abokinsa, don haka, kowannenku ya duba wanda ya dace
ya yi abota da shi.‛241
Don haka, lallai ne kada iyaye su bar `ya`yansu su riqa
yin mu’amala da yaran da ba su da tarbiyya, a wajen
wasa ko wajen zuwa makaranta. Haka kuma, ya kamata
iyaye su tabbatar da cewa, waxanda ke yin abota da
`ya`yansu, masu hankali ne, da sahihin addini, da
kyawawan xabi’u. Wajibi ne su nisantar da `ya`yansu
daga jahilai ko fasiqai, da wawaye ko masu xabi’un
banza.
20. Wajibin iyaye ne su kula da irin tufafi da kayan adon da
za su sayo wa `ya`yansu don su sanya. Rashin sanya ido
a kan nau’o’in tufafin da yara ke amfani da su a yau da
kullum, na da haxari a kan tarbiyya. Abin mamaki,
waxansu iyayen na yin sakaci game da wannan al’amari,
ta yadda `ya`yansu za su riqa sanya tufafin da ba su dace
ba, wani lokaci ma, su sanya tufafin da Shari’a ta hana
sanyawa, amma ba su kula ba. Misali, waxansu iyayen
su kan sayo wa `ya`yansu kayayyakin da ke xauke da
hotunan manya-manyan kafirai, ko mawaqa, ko `yan
qwallo, ko gumaka, ko karuwai, da sauran manya-
manyan ashararan duniya, ko kuma tufafin da aka yi
rubutun batsa, ko surkulle, ko rashin tarbiyya, a jikinsu.
Haka kuma, waxansu kan sayo wa `ya`yansu mata
nau’o’in tufafin da ke nuna tsiraici da rashin mutunci,
tun suna qanana. A ganin irin waxannan iyayen, abin da
su ke yi daidai ne, kuma wai nuna qauna ce ga `ya`ya.
Ta haka, sai `ya`yan su taso da tsananin son kafirai, irin
su Lenin, Bob Marley, Michael Jackson, Ronaldo,
Okocha, da Kanu, fiye da yadda su ke son Allah (Mai
241
Abu Dāwud da Tirmidhi: Hasan li ghairih [Duba as-Sahīhah #927]
137
girma da xaukaka) da ManzonSa (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi), da sahabban Manzon Allah (Allah
Ya yarda da su) da sauran bayin Allah na qwarai. Sau da
yawa an ji yara na cewa suna son zama Bob Marley ko
Micheal Jackson ko Ronaldo da sauransu. Wannan, babu
shakka, bala’i ne mai girma, a cikin al’umma.
Wajibi ne iyaye su tabbatar cewa `ya`yansu na sanya
tufafin da bai sava wa Shari’a ba. Kuma ya kamata su
saba wa qananan yara maza sanya dogon wando a
lokacin da za su yi salla. Domin kuwa salla ba ta inganta
ga wanda ya buxe cinyarsa da gangan (alhali yana da
ikon rufewa), kamar yadda Ibn Taimiyyah ya tabbatar. A
qarqashin wannan magana ta Ibn Taimiyyah, Shaykh Muhammad Nāsiruddīn Al-Albānī ya ce: ‚Ya kamata a
koya wa yara maza sanya dogon wando. Bai halatta
iyaye su riqa sanya masu gajeren wando (a lokacin da za
su yi salla), kuma su riqa tafiya da su masallaci a haka
ba, saboda hadisin: ‘Ku umurci `ya`yanku da yin salla
idan sun kai shekara bakwai…’ Babu shakka umurnin da
za a yi masu ya haxa da sharuxxanta, da rukunanta
(kasancewar sallar ba ta inganta sai da su).‛242
Sai dai kuma, lallai ne iyaye su nisantar da `ya`yansu
daga sanya dogon wandon da tsawonsa ya wuce idon
sawu; wanda sai an take shi a qasa, saboda tsawo. Irin
wannan wando, bai dace da Musulmi ba. Hadisai sahihai
sun iyakance tsawon gyauto (kamar wando) zuwa wurare
uku: (i) tsakiyar qwauri;243
(ii) tsakanin saman qwauri
zuwa qasar gwiwa;244
(iii) daga tsakiyar qwauri zuwa
242
Ibn Taimiyyah, Hijābul Mar’ah wa libāsuha fis-Salah, Ta’alīq
Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī, (al-Maktabul Islāmī, Beirut, 1985),
shafi na 28 243
Ahmad, Muslim da Xabarāni 244
Ahmad, Tirmidhi, Nasā’i da Ibn Mājah
138
idon sawu.245
Idan doguwar riga ce, Sunnah ta iyakance
tsawonta zuwa idon sawu.246
Tufafin da ya wuce
wannnan haddi, bai dace da karantarwar Sunnar Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ba,
Allahumma, sai dai idan akwai mantuwa, ko kuma wata
larura, kamar rauni ko mikin da a ke da buqatar
rufewa.247
Malamai sun bayyana aibobin da ke tattare da sakin
tufafi, har ya ja qasa, a haqqin maza. Waxannan aibobi
sun haxa da: sava wa Sunnar Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi); da faxawa cikin
abin da Shari’ah ta hana; da almubazzaranci; da taqama,
da alfahari da girman kai; da kamanceceniya da mata; da
yiwuwar aukuwar najasa; da haxari ga ibada; da aukawa
cikin haxarin rashin samun kallo da rahama daga Allah;
da faxawa cikin uqubar Allah.248
Don haka, wajibi ne
kowane musulmi ya nisanci sakin tufafi, har ya ja qasa,
ko da kuwa ba da niyyar girman kai ba.249
245
Ahmad, Abu Dāwud da Ibn Mājah 246
Bakar Abdullah Abu Zaid, Hadduth-Thaub wal Uzrah wa Tahrīmul Isbāl wa Libāsish-Shuhrah, (Maktabah as-Sunnah, Egypt, 2001), shafi
na 7-14 247
Bakar Abdullah Abu Zaid, Hadduth-Thaub wal Uzrah wa Tahrīmul Isbāl wa Libāsish-Shuhrah, shafi na 23-24 248
Bakar Abdullah Abu Zaid, Hadduth-Thaub wal Uzrah wa Tahrīmul Isbāl wa Libāsish-Shuhrah, shafi na 19-21 249
Akwai mutanen da ke da’awar cewa, hadisan da suka tsawatar game
da sakin tufafi ya wuce idon sawu, duk suna magana ne a haqqin
wanda ya yi haka da nufin girman kai ko taqama. Hujjarsu mafi qarfi,
ita ce, bayan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya bayyana wa sahabbansa (Allah Ya yarda da su) irin uqubar da
aka tanada ga wanda ya saki tufafinsa, ya ja qasa, saboda girman kai,
Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ya ce, ‘tufafina yana jan qasa, duk da
cewa ina qoqarin xaga shi’. Sai Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) ya ce: ‘ba ka daga cikin masu sakin tufafi saboda
girman kai’. Haka kuma, Abu Hurairah (Allah Ya yarda da shi) ya
139
ruwaito daga Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Allah ba zai dubi wanda ya ja tufafinsa a qasa, saboda
taqama ba, a ranar qiyama.‛ Waxanda ke ganin halaccin sakin tufafi ya
ja qasa, sun bayyana cewa, duk wanda ya saki tufafi ya ja qasa ba da
nufin girman kai ba, bai shiga cikin narkon da aka bayyana a hadisan
ba.
Sai dai kuma, wannan fahimtar kuskure ne. Hadisan Abubakar, da
Abu Hurairah, da wata ruwaya daga Ibn Umar (Allah Ya yarda da su)
na nuna irin haxarin da ke cikin sakin tufafi, saboda girman kai ko taqama; amma hadisan Ibn Abbās, da Abu Sa’īd al-Khudrī, da
Huzaifah (Allah Ya yarda da su) sun tabbatar da azaba ga wanda ya
saki tufafinsa, ba tare da qayyade wani dalili ba, ko la’akari da
niyyarsa. Ke nan, ayyuka ne guda biyu mabambanta, waxanda ke
qunshe da sakamako dabam daban: wanda ya saki tufafi, da niyyar
taqama da girman kai, Allah ba zai kalle shi ba, a ranar qiyama, ba zai
tsarkake shi ba, kuma yana da azaba mai raxaxi, kamar yadda hadisan
Abubakar da Abu Hurairah da Ibn Umar (Allah Ya yarda da su) suka
nuna. Idan kuwa ya saki tufafin har ya wuce idon sawu, ba tare da
niyyar girman kai ko taqama ba, Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) ya bayyana cewa za a qona qasan idon sawunsa, saboda mujarradin wannan mummunar aiki, kamar yadda Ibn Abbās,
da Abu Sa’īd al-Khudrī, da Huzaifah (Allah Ya yarda da su) suka
ruwaito.
Kuma idan ma an qaddara cewa duk hadisan na magana ne a kan
wanda ya saki tufafi, saboda girman kai ko taqama, shi Abubakar
(Allah Ya yarda da shi) ya bayyana wa Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), cewa hakan na faruwa a gare shi, duk da
qoqarin da ya ke yi wajen tattare shi, da xaga shi sama. Waxanda ke
sakin tufafinsu a yanzu, suna yin haka? Ban da wannan, Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya tabbatar da cewa,
Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ba shi daga cikin waxanda ke sakin
tufafi, saboda girman kai. Idan mutum ya saki tufafinsa a yanzu, wane
ne zai ba shi tazkiyya ko lasisin cewa, ba don girman kai ya ke yi ba?
Haka kuma, idan Abubakar (Allah Ya yarda da shi) ya saki tufafinsa a
qasa, kasancewar ya sayo shi ne a haka, me za a ce game da waxanda
ke sayen yadi, su ba tela, ya auna su, sannan, su ce masa ga yadda su ke
son tsawon tufafin? Bayan wannan, hadisai sun tabbata daga Ibn Umar da Jābir ibn Salīm (Allah Ya yarda da su) cewa mujarradin sakin tufafi
a qasa, girman kai ne da taqama [Ahmad da Ibn Mani’]. Wace hujja ta
rage wa waxanda ke sakin tufafinsu har ya ja qasa?
140
Haka kuma, ya kamata a nisantar da qananan yara maza
daga amfani da zinare ko sanya tufafin alhariri. Idan ma
aka ga sun sanya, a umurce su da cirewa, tare da yin
masu bayanin matsayinsa, a haqqin maza. Abdullah ibn
‘Amr (Allah Ya yarda da shi) ya ce: ‘Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ga tufafi
(mai launin) fatse-fatse a jikina, sai ya ce: ‚Mahaifiyarka ce ta umurceka ka sanya!?‛
250 Kuma Jābir ibn Abdullah
(Allah Ya yarda da shi) ya ce: ‚Mun kasance muna fisge
shi (zinare ko tufafin alhariri) daga (jikin) yara maza,
amma muna barinsa ga mata.‛251
Bayan wannan, wajibi
ne iyaye su hana `ya`yansu maza sanya abin wuya
(sarqa) da abin hannu (warwaro) da xan kunne, kamar
yadda waxansu matasan da ba su da tarbiyya ke yi, a
matsayin koyi da arna. Haka nan ma, wajibi ne a hana su
yin irin askin nan na banza, wanda ke kamanta musulmi
da kafirai, ko kuma a aske wani vangaren gashin kai, a
bar saura, wai saboda gayu.
Don haka, duk da cewa mafi yawan malaman mazhabobi guda
huxu, na ganin cewa makaruhi ne sakin tufafi ya ja qasa, ba haram ba,
fahimtar da ta fi qarfi, da rinjaye, bisa tabbatattun dalilai, ita ce
haramci. Kuma idan ma an xauka cewa makaruhi ne, mene ne amfanin
aikata makaruhi, musamman idan za a iya kauce masa? Ballantana ma,
waxansu malamai na ganin cewa hadisan da suka yi magana a kan haramcin sakin tufafi, sun kai matsayin mutawātir ma’anawi, domin an
ruwaito daga Ibn Abbās, da Ibn Umar, da Ibn Mas’ud, da Abu
Hurairah, da Anas, da Abu Zar, da A’ishah, da Hubaib ibn Mugaffal, da Abu Sa’īd al-Khudri, da Huzaifah, da Mughīrah, da Samurah ibn
Jundub, da Sufyān ibn Sahl, da Abu Umāmah, da Ubaid ibn Khālid, da
Jābir ibn Salīm, da Ibnul Hanzaliyyah, da Amr ibn ash-Sharīd, da Amr
ibn Zurārah, da Amr ibn Fulān, da Kharīm ibn Fātik (Allah Ya yarda da
su). Duba littafin Bakar Abdullah Abu Zaid, Hadduth-Thaub wal Uzrah wa Tahrīmul Isbāl wa Libāsish-Shuhrah, shafi na 18-19 250
Muslim 251
Abu Dāwud: Hasan
141
Su kuma `ya`ya mata, lallai ne a saba masu da sanya
hijabi (ko mayafi) cikakke idan za su fita gida zuwa
makaranta ko kasuwa ko gidan biki ko asibiti ko ziyara
ko wani wuri daban. Kuskure ne a qyale `yan mata su
riqa sanya tufafi shara-shara ko kuma su fita ba tare da
hijabi cikakke ba, da zarar sun balaga, wato, sun fara
jinin al’ada. Maganar cewa hijabi wajibi ne kawai a kan
matar aure, ba ta da asali a cikin Alqur’ani da Sunnah.
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya ce: ‚Kuma ka ce wa
muminai mata su runtse daga gannansu, kuma su tsare
farjojinsu, kuma kada su bayyana qawarsu face abin da
ta bayyana daga gare ta, kuma su doka da mayafansu a
kan wuyan rigunansu, kuma kada su nuna qawarsu face
ga mazansu, ko ubanninsu…‛252
Kuma Ya ce: ‚Ya kai
Annabi! Ka ce wa matanka na aure da `ya`yanka da
matan muminai su kusantar da manyan tufafin da ke
kansu qasa.‛253
Hadisi ya tabbata cewa Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Daga qarshen al’ummata, za a samu waxansu mata (na
yawo) sanye da tufafi (amma kuma saboda shara-
shararsa), tsirara (su ke a zahiri)… Ku la’ance su, domin
kuwa la’anannu ne.‛254
A cikin wani hadisin, Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce:
‚Ba za su shiga aljanna ba, kuma ba za su ji qamshinta
ba.‛255
Ke nan, da zarar yarinya ta balaga (ko da ba ta yi
aure ba), wajibi ne ta sanya hijabi irin na Musulunci,
idan za ta fita.256
252
Nūr, 24:31 253
Ahzāb, 33:59 254
Xabarāni: Sahīh 255
Muslim 256
Nazari a cikin Alqur’ani da Sunnah na tabbatar da cewa akwai
sharuxxa guda takwas da a ke buqatar lulluvi ko mayafin da mace za ta
sanya (a lokacin da za ta fita) ya cika, kafin a kira shi hijabi. Sharuxxan
su ne: (1) ya zamanto ya rufe jikinta gaba xaya (2) kada ya kasance shi
142
Haramun ne ga mace ta yi wa iyayenta ko mijinta xa’a,
idan suka hana ta sanya hijabi cikakke, a lokacin da za ta
fita ko kuma suka taqaita mata sanya hijabi ga lokacin da
za ta yi salla kawai, kamar yadda waxansu ke yi.
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya ce: ‚Babu xa’a ga wata halitta a cikin savon
Mahalicci‛.257
Kuma ya ce: ‚Ana yin xa’a ne a cikin
abin da aka sani a Shar’ance.‛258
Tun da sanya hijabi
umurni ne daga Allah da Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi), ba daidai ba ne ga wata
mace ta qi sanyawa saboda mijinta ko iyayenta ba su so.
Idan ta qi sanyawa, ta yi laifi; idan kuwa ta sanya, ba ta
da laifi a wajen Allah (Maxaukaki), ko da iyayenta ko
mijinta sun yi fushi. Haqiqa, xa’a ga Allah (Mai girma
da xaukaka) da ManzonSa (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) na gaba da xa’a ga miji ko iyaye. 259
A
kansa tufafi ne na ado (3) kada ya riqa nuna wani vangare ko wata gava
na jikinta, saboda shara-shara da shafa-shafarsa (4) kada ya zamanto
matsattse ta yadda zai siffanta jiki (5) kada a sanya turare a lokacin da
za a fita ko kuma tun kafin lokacin fitan bayan an san za a fita daga
baya (6) kada ya yi kama da tufafin maza (7) kada ya yi kama da
tufafin mata kafirai (8) kada ya kasance tufafi ne na shahara (saboda tsada ko arharsa, sai dai ya kasance matsakaici). [Duba littafin Jilbāb al-Mar’ah al-Muslimah na Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī]. 257
Muslim 258
Muslim 259
Akwai savani mai tsanani, a tsakanin malamai, a wannan zamani,
dangane da hukuncin rufe fuska da tafin hannu. Misali, a yayin da Shaykh Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī da al-Qaradāwi ke ganin
halaccin bayyanar da fuska da tafin hannu, ko da ya ke rufewar mustahabbi ne; Shaykh Muhammad ibn Sālih al-‘Uthaymīn da At-
Tuwaijiri da mafi yawan malaman Saudia da malaman Yemen da
malaman Sunnah na qasar Masar na ganin wajibcin rufe fuska da tafin hannu. [Duba littafin Jilbābul Mar’atil Muslimah fil Kitāb was Sunnah da Ar-Raddul Mufhim na Al-Albānī; Risālatul Hijāb na Al-‘Uthaymīn;
Risālatul Hijāb na At-Tuwaijiri; Hirāsatul Fadīlah na Bakar Abdullah
143
Abu Zaid; da Al-Hijāb na Musxafa Al-Adawi don ganin maganganun
malamai, da savanin da suka yi].
Abin lura shi ne, duk malaman sun tabbatar da Shar’ancin sanya
niqabi da safar hannu, domin rufe fuska da tafin hannu. Hasali ma,
savanin da suka yi, ba wai a kan halacci ba ne. Sun yi savani ne
dangane da wajibci ko mustahabbancin niqabi. Kuma wannan savani
ba yanzu aka fara ba; tun daga lokacin sahabban Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) da tabi’ai da sauran magabata
aka samu bambancin fahimta. Bambancin lokacin magabata (salaf) da abin da ke faruwa a yanzu shi ne: magabata ba su qulla al-walā wal barā, wato, qiyayya da soyayya, a kan mas’alar ba; amma waxansu
xaliban ilmi a yanzu, suna neman kafirta juna saboda niqabi. Duk da irin zafafa wa juna da aka yi a tsakanin Al-Albānī, musamman a cikin
Ar-Raddul Mufhim, da At-Tuwaijiri da magoya bayansa, ba su qulla
soyayya da qiyayya a kan wannan mas’ala ba. Abin mamaki, waxansu
`yan zafi a Nijeriya, sun mai da mas’alar niqabi, kamar xaya daga cikin
rukunan Musulunci, ta yadda su ke qulla qiyayya da soyayya ( )
a kanta. Irin waxannan xaliban ilmi, ba su da wani magabaci a kan
haka, daga cikin malaman da suka gabata, da malaman wannan zamani.
Lallai ne xaliban ilmi da masu da’awa su ji tsoron Allah.
Kwatsam, sai ga waxansu `yan bidi’a na da’awar cewa niqabi bidi’a
ne, kuma wai ba a fara sanya shi ba, sai bayan shekara hamsin (50) da
barin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
duniya. Wannan qarya ce tsantsa, wadda ba ta buqatar a yi kace-nace a
kanta. Waxannan mutane, galibinsu `yan boko ne waxanda suka
tasirantu da shubuhohin , waxanda ke raddin hadisan Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ingantattu saboda
wai sun sava wa abin da kimiyyar zamani ta tabbatar. Bayan waxannan
`yan boko aqida, an samu waxansu daga cikin shehunnan xariqa na
sukar hijabi da niqabi, kuma suna umurtar matan Musulmi da sanya
gyale ko xigilgilallen mayafi, maimakon hijabi, wai don kada su yi
kamanceceniya da matan `yan izala.
Daga baya-bayan nan, sai ga wani malami a jami’ar Ahmadu Bello,
Zaria, Issa Hasan Tikuma, ya rubuta wani littafi, yana sukar xalibai
mata waxanda ke sanya niqabi, kuma yana kira ga malaman jami’a da
su hana irin waxannan xalibai zama a cikin aji, a lokacin karatu. Bai
tsaya nan ba, Tikuma ya jahiltar da malamai, kuma ya zarge su da
jumudi, wato, daskarewar fahimta, da sakarci da kuma rashin faxin
gaskiya. Hujjarsa a cikin wannan littafi mai suna The Abuse of Islam and the Dormancy of Islamic Scholars: Evidence from the Misuse of
144
vangaren miji kuma, haramun ne a gare shi ya bar
matarsa ta fita, ba tare da hijabi cikakke ba. Idan ba za ta
sanya tufafin da ya dace ba, a lokacin da za ta fita, kada
ya yi mata iznin fita.260
Niqab (Face Veil) in the Nigerian Society ita ce wai waxansu mata na
yin amfani da niqabi a matsayin kariya wajen satar jarabawa ko sace-
sace a kasuwa, da sauran nau’o’in varna.
Tir da wannan mummunar famita, da kuma qarfin halin rashin
kunya (jara’a) a kan malamai. A ina aka tava aibanta wani tabbataccen
abu a cikin Shari’ah saboda waxansu `yan tsirarun mutane da ke sakaci
da shi? Wane tabbaci Tikuma ya ke da shi cewa xalibai mata suna
fakewa da niqabi wajen yin varna? Shin, Tikuma ba ya jin cewa yana
qoqarin jawo wani bala’i ne ga kansa da hukumar jami’ar Ahmadu
Bello, a dalilin kiraye-kirayen da ya yi cewa a xauki qwaqqwarar
mataki a kan masu sanya niqabi? Ba ya tunanin cewa varna ya ke yi wa
Musulunci da musulmi, maimakon gyara? Allah Ya shiryar da mu.
Kwanan nan aka ce Issa Hasan Tikuma ya sake rubuta wani littafi a
kan niqabi. Ko da ya ke ba a buga littafin ba, waxanda suka tattauna da
shi, sun ce littafin ya qunshi bayanan da ke nuna cewa wai niqabi
wajibi ne kawai a kan matan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi). Duk da cewa babu wani xalibin ilmi da ya ruxu da
shirmensa, da yawa daga mutanen da ke mu’amala da shi, suna zaton
cewa wai shi Ahlus-Sunnah ne! Bincike ya nuna cewa Issa Hasan
Tikuma na fama da karkatacciyar aqida, da kuma ra’ayin xariqar
sufaye, duk da cewa ba ya son a gane hakan. Allah Ya kyauta. 260
Waxansu mata na da’awar cewa ba su sanya hijabi saboda ba shi ne
ya ke tabbatar da tsoron Allah ba, kuma wai ai zuciya a ke dubawa ba
tufafi ba. Haka kuma, su kan yi da’awar cewa akwai matan da ke sanya
hijabi, wataqila ma har da niqabi, amma ayyukansu munana ne.
Wannan shubuhar na nuna jahilci da son zuciyar irin waxannan mata,
duk da cewa suna samun goyon bayan waxansu malaman da ke da
karkatacciyar fahimtar Musulunci. Sanannen abu shi ne, kamar yadda
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya yi umurni da yin salla, da azumi, da
zakka, da hajji, da biyayya ga iyaye, da kyautata wa maqwabta da `yan’uwa, haka kuma, Ya umurci mata da sanya hijabi [Nūr 24:31;
Ahzāb 33:59]. Ke nan, biyayya ce ga Allah, mace ta sanya hijabi, ko da
sanya hijabin bai hana ta yin waxansu munanan abubuwa ba. Shin
akwai musulmin da zai ce ba a buqatar yin aure a yanzu, tun da dai bai
hana waxansu ma’aurata yin zina ba!? Ko kuwa, za a ce ba dole ne
145
Haka kuma, kasancewar itace ana tanqwara shi ne tun
yana xanye, ya kamata iyaye su himmatu wajen koya wa
`ya`yansu sanya hijabi, da saba masu amfani da shi, tun
suna qanana, musamman a lokacin da za su fita,
maimakon gyale ko abin tatan qullun koko.261
Shaykh Muhammad Sālih ibn al-‘Uthaimīn ya ce: ‚Ya ku
`yan’uwa, iyayen `ya`ya mata! Sanya wa `ya`ya mata
gajejjerun tufafi ko matsattsun tufafin da ke siffanta jiki
ko tufafin da ke bayyana launin jiki saboda shara-
shararsa, abu ne da ya yaxu a tsakanin mutane kuma aka
xauke shi da sauqi. (Ku sani cewa) wanda duk ya sanya
wa `ya`yansa mata irin waxannan tufafi ko kuma ya
qyale su idan sun sanya da kansu, to yana sanya masu
tufafin `yan wuta ne, kamar yadda ya tabbata daga
Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).262
Ya kai uba musulmi! Yanzu za ka so wa `yarka, kuma
masoyiyarka, shiga wuta? Ka yarda ka riqa sanya wa
`yarka tufafin da zai nuna rashin kunyarta, bayan kuwa
kunya na daga imani? Ka yarda `yarka ta mai da kanta
kamar wata hajar (kayan) sayarwa…?‛263
Wajibi ne iyaye su sanya ido a kan `ya`yansu mata don
tabbatar da cewa ba su yin amfani da kayan ado na
haram. Sanannen abu ne cewa qarin gashi, da tsaga wani
mutane su yi salla ba, tun da dai sallar ba ta hana waxansu musulmi
aikata alfasha ba? 261
Sanya hijabi na da fa’idodi masu yawa: (1) tsare mutunci; (2)
tsarkake zuciya; (3) samun kyawawan xabi’u; (4) alama ce ta kamewa;
(5) hanya ce ta karya kwaxayi da tunanin shaixan; (6) yana taimakawa
wajen tsare kunya da kishi; (7) yana hana tabarruj. [Duba littafin Hirāsatul Fadīlah na Bakar Abdullah Abu Zaid]. 262
Imām Muslim da Xabarāni suka ruwaito hadisin, kuma ya gabata. 263
Samīr Abdul-‘Azīz, Manhaj al-Islām fi Tarbiyyatil Aulād, shafi na
247-248
146
vangare na jiki don ado,264
da aske gashin gira, da
amfani da duk wani sanadarin da ke canza fatar jiki
(bleaching), haramun ne a musulunci. Hasali ma,
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya roqi Allah (Mai girma da xaukaka) Ya la’anci
waxanda ke yin haka, kamar yadda hadisai suka
tabbatar.265
Amma abin mamaki, waxansu iyayen ne ke
umurtar `ya`yansu su tsaga jikinsu, su yi zane-zane ko
hotunan abubuwa masu rai (bayan an tsattsaga jikin), da
sunan ado. Wani lokaci ma, iyayen ne ke yin haka da
kansu. Idan iyaye suka tsaga fuska ko wani vangare na
jikin `ya`yansu, laifin yana kansu, tun da dai `ya`yan ba
su da ikon hanawa a wannan lokaci.266
Wannan shi ne abin da Imām Nawawī da mafi yawan malamai suka
tabbatar.267
21. Haqqin `ya`ya ne a kan iyayensu a sanar da su
muhimmancin lokaci da yadda za su yi amfani da shi, da
fahimtar da su cewa an halicce su ne don bauta, da
tunatar da su wajibcin tattali don zama sojojin
Musulunci, da faxakar da su qalubalen da ke gabansu, a
matsayinsu na yara manyan gobe, da karantar da su irin
264
Wannan ya haxa da tsagar al’ada da a ke yi wa yara a fuska, kamar
bille, fashin goshi, kwale, tsagen kananci, mallanci, gobiranci, nufanci,
yarbanci da sauransu. Dukkansu laifi ne, kuma canza halittar Allah ce,
da cutar da jiki ba tare da larura ba. Waxanda aka yi wa irin wannan
tsaga tun suna qanana, ba su da laifi, domin kuwa ba su da ikon hanawa
a wancan lokaci. Sai dai kuma wajibi ne su nisantar da nasu `ya`yan
daga irin wannan aiki mara kyau nan gaba. 265
Bukhari da Muslim 266
Wannan hukuncin bai haxa da huda kunne don sanya wa yara mata
xan kunne, da sauran kayayyakin ado ba. Shi kam babu laifi, tun da dai
larura ce, kamar yadda malamai, irin su Ibn al-Qayyim, suka tabbatar. Duba littafin Tuhfah al-Maudūd, shafi na 143-144 267
Samīr Abdul-‘Azīz, Manhaj al-Islām fi Tarbiyyatil Aulād, shafi na
245
147
gudummuwar da a ke sa ran su ba da wajen kawo ci gaba
da xaukaka ga al’umma. Waxannan abubuwa za su
tabbata ne kawai idan `ya`ya sun taso da kishin zuci, da
son karatu da aiki da shi, da son dogaro da kai, da
kyakkyawar mu’amala, da son taimakon jama’a, da sanin
muhimmancin lokaci, bayan sun samu kyakkyawar
tarbiya.268
268
‘Lokaci’ yana daga abubuwa mafi tsada waxanda Allah (Mai girma
da xaukaka) Ya yi wa bayinSa kyautarsu. Babu wata kasuwa da a ke
sayar da ‘lokaci’; shi ne farkon abin da a ke nema daga kowane
musulmi, kasancewar jihadi, da da’awah, da karatun Alqur’ani, da tsai
da salla, da yin ziyara, da koyon karatu da karantarwa duk suna buqatar
lokaci. Wannan ya sa a ke xaukar ‘lokaci’ a matsayin rayuwa. Saboda
matsayin ‘lokaci’, Allah (Mai girma da xaukaka) Ya goranta wa bayinSa ni’imar ‘lokaci’ [An’ām, 6:13; Ibrāhīm, 14:32-34; Nahl, 16:12;
Isrā, 17:12; Fussilāt, 41:37], kuma Ya rantse da ‘lokaci’ gaba xayansa
ko sashensa [‘Asr, 103:1; Lail, 92:1-2; Fajr, 89:1-4; Duha, 93:1-2; Inshiqāq, 84:16-17; Takwir, 81:17-18].
‘Lokaci’ na da matuqar muhimmanci a rayuwar musulmi: shi ne
rayuwa gaba xaya, kamar yadda Al-Hasan Al-Basari ya ce, ‘Ya kai xan
Adam, rayuwarka gaba xaya ta qunshi kwanaki ne, idan wata rana ta
wuce, sashenka ne ya wuce.’ ‘Lokaci’ na daga asalin ni’imomin da
Allah Ya yi wa bayinSa; yana daga cikin abubuwan da za a yi hisabi a
kansu a ranar qiyama; kuma shi ne uwar dukiya da jarin kowane
mutum.
Wajibi ne musulmi ya yi amfani da lokacinsa, yadda ya dace. Haka
kuma, laifi ne a tozarta ‘lokaci’, domin yin hakan, na jawo nadama,
kuma butulci ne ga Allah. A wannan zamani, rashin amfani da ‘lokaci’
yadda ya dace, alama ce ta ci baya ga al’umma.
Amfani da ‘lokaci’ yadda ya dace na buqatar: (i) tsattsara abubuwan
da za a gabatar (ii) samar da manufa, da abin da a ke son a cimma, tun
gabanin a gudanar da abu (iii) shirya abubuwa a bisa tsarin cancanta, da gwargwadon muhimmanci (iv) shirya jadawalin ayyukan da za a yi a
cikin yini (v) amfani da lokacin da ya fi daxi, da kuma karsashi ga
mutum (vi) sabawa da qin xaukar nauyin abubuwan da ba su zama dole
ba (vii) watsi da aqidar sai komai ya yi daidai, xari bisa xari, domin
kuwa kyautatawa da ingantawa kawai a ke buqata, ba wai kamala ba.
Malamai sun bayyana cewa kowane mai hankali yana buqatar raba
‘lokacinsa’ gida huxu: (1) ambaton Allah ta hanyar nau’o’in ibada na
148
Wajibi ne iyaye su tsawata wa `ya`yansu, a duk lokacin
da suka ga suna amfani da lokaci wajen aikata abubuwan
da ba za su amfane su ba, duniya da lahira. Zaman
xumama benci, da zaman kashe wando, ko zaman kalle-
kallen finafinan wasan kwaikwayo269
da wasannin `yan
farilla da nafila (2) yi wa kai hisabi (3) tunani a cikin halittar Allah (4)
biyan buqatar duniya, kamar neman abinci. 269
Bincike ya tabbatar da cewa kallon finafinai na da illoli ta fuskar
aqida, da al’ada, da tarbiyya, da tarihi, da tunani, da lafiya, da tattalin
arziki. Ta vangaren aqida, finafinai na da illolin da suka shafi nuna
muhimman alamomin kafirai da vataccen addininsu; da nuna cewa
waxansu mutane, musamman matsafa, da shugabannin kiristoci,
waxanda ke yin amfani da karama ta qarya ko gicciye (cross), suna iya
yin tarayya da Allah wajen yin halitta da kashewa da rayawa; da haifar
da shakku a cikin zukatan waxansu, game da ikon Allah da qarfinSa;
da koyar da sihiri da bokanci; da koyar da yin wasa da sunan Allah. A
vangaren yanayin zamantakewa, waxanda ke kallon finafinai, su kan yi
sha’awar gwanayen `yan fim, ko mawaqa daga cikin kafirai da karuwai
da kangararru, da irin xabi’un da su ke nunawa a lokacin wasan fim, da
son koyi da su; da yaxa halayen banza; da koyar da zinace-zinace, da
fyaxe, da kisan kai; da nau’o’in rashin gaskiya, kamar qarya, da zamba
da karvar rashawa. A vangaren tarbiyya kuma, kallon finafinai na
vavvako wa samari sha’awar mata, da son yin jima’i; da raye-raye; da
maganganun batsa; da bayyana tsiraici; da rashin son sanya tufafin da
ya dace; da sauransu. A vangaren ibada, kallon finafinai na haifar da
sakaci da jinkiri wajen ibada; da jawo tauye lada; da wulaqanta hijabi.
A tarihance, finafinan da a ke shiryawa, musamman daga qasashen
Turai, na kawo tarihi a hagungunce domin a gurvuta sahihin tarihin
Musulunci; da nuna azzalumai a matsayin masu gaskiya; da rashin
qimanta baraden Musulunci; da tsoratar da musulmi game da qarfin
kafirai. A fagen lafiya, kallon finafinai na jawo matsala ga idanuwa; da
haifar da rashin barci.
Abin baqin ciki da takaici shi ne, duk waxannan matsaloli da
aibobin da ke tattare da finafinan Turanci (Nigerian Films), da finafinan
India, da waxanda a ke shigo da su daga qasashen Turai, ana samunsu a
cikin finafinan Hausa. Hasali ma, varnar da `yan fim xin Hausa ke yi
wa Musulmin Nijeriya da Musulunci ta fi wadda waxancan ke yi,
saboda mutane na fahimtar halshen da `yan fim xin Hausa ke amfani da
149
aljannu (cartoon), ba su da amfani a cikin rayuwar
musulmi (yaro da babba, mace da namiji), Allahumma,
sai dai idan cartoon xin da aka shirya bisa tsarin
Musulunci. Ibn al-Qayyim ya ce: ‚Kuma ya kamata
waliyyin yaro (iyaye ko waninsu) ya nisantar da shi daga
karvar abin hannun mutane, domin kuwa da zarar ya
saba karva, hakan zai zame masa xabi’a; sai ya zamanto
maimakon ya riqa ba da wa, sai dai ya karva. Kuma ya
kamata (uba) ya koya wa yaronsa yin kyauta da
taimakon jama’a (gwargwadon hali). Idan zai ba da
kyautar wani abu, an so ya ba da ta hannun yaron, don ya
saba masa da ayyukan alhairi. Haka kuma, ya kamata ya
nisantar da shi daga kasala, da zaman kashe wando da
xumama benci, domin kuwa abubuwa ne waxanda ke
haifar da tawaya ga wanda ke yinsu.‛270
22. Lallai ne iyaye su riqa karantar da `ya`yansu sahihin
tarihin Musulunci, da irin gwagwarmayar da sahabban
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) suka yi wajen tsare martabar addinin Musulunci, da
yaxa shi a duniya. Haka kuma, lallai ne a karantar da su
martabar sahabbai da tabi’ai da tabi’ut tabi’in da sauran
malaman Sunnah, da irin abubuwan koyi da suka yi a
cikin rayuwarsu. Idan yara suka ilmantu a kan matsayin
sahabban Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi); suka fahimci daraja da matsayin
matan Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) da `ya`yan Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) da jikokin Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi); da
shi. Haka kuma, ana ganin irin fitsara, da ballagazanci, da sakarci, da
shashanci, da kwaikwayon al’adu da addinin kafirai, da rashin kamun
kai, da munanan xabi’un da mafi yawan `yan fim ke koyarwa ta
fuskoki dabam daban. Allah Ya kiyaye mu. 270
Tuhfah al-Maudūd, shafi na 162
150
matsayin tabi’ai da manyan malaman Sunnah, ana sa ran
su girmama su, irin girmamawar da ta dace da su, kuma
su yi tsayuwar daka wajen tsare martabarsu da bayyana
falalarsu, tare da tona asirin wanda ke adawa da su. Haka
kuma, ana sa ran su xauki waxannan manyan mutane a
matsayin abin koyi gare su, maimakon `yan qwallo da
`yan rawa ko kangararrun matasan da ke yin finafinai.
23. Ya kamata iyaye su tarbiyyantar da `ya`yansu a kan yin
da’awa, da umurni da kyakkyawa da hani da mummuna,
domin su san muhimmancin qoqarin tabbatar da gyara a
cikin al’umma.271
Haka kuma, ya kamata iyaye su nemi
271
Da’awah ta qunshi yin kira zuwa ga imani da Allah, da abin da
ManzanninSa suka zo da shi, ta hanyar gaskata abin da suka ba da
labari, da yin masu xa’a cikin umurninsu. Kira zuwa ga addinin Allah
farilla ce da Allah (Maxaukaki) Ya xora a kan al’ummar Musulmi baki xaya [Aal Imrān, 3:110]; sai dai kuma tana zama farillar dole a kan
shugaba [Hajj, 22:41], sannan sai malamai, kasancewar sun xauki
alqawari ga Allah (Maxaukaki) cewa za su bayyana littafinSa, ba tare da voyewa ba [Aal Imrān, 3:187].
Ayoyin Alqur’ani da ingantattun hadisai sun zo da umurni game da yin da’awah [Aal Imrān, 3:104; Nahl, 16:125; Taubah, 9:71; Bukhari
da Muslim;]. Haka kuma, hadisan Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) sun yi umurni da yin da’awa, da umurni da
kyakkyawa da hani da mummuna [Bukhari da Muslim]. Malamai da
yawa sun tafi a kan cewa yin kira zuwa ga hanyar Allah, da umurni da
kyakkyawa da hani da mummuna wajibi ne a kan kowane Musulmi gwargwadon iko. Misali, Ibn Kathīr, a cikin tafsirinsa, a qarqashin Aal
Imrān, 3:104, ya bayyana cewa yin da’awa wajibi ne a kan kowane
mutum, gwargwadon ikonsa. Haka kuma, Ash-Shaukāni, a cikin
tafsirinsa, a qarqashin Yusuf, 12:108, ya bayyana cewa ayar na nuna
wajibcin koyi da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) a cikin da’awah.
Ahlus Sunnah na yin da’awah saboda dalilai guda tara:
1. Lada mai girma wanda Allah (Maxaukaki) Ya tanadar wa
mai yin da’awah, kasancewar wanda ke yin da’awah: yana
daga cikin mafi kyautata magana [Fussilat, 41:33]; shi ne mafi alhairin mutane [Aal Imrān, 3:110]; yana daga cikin
151
masu babban rabo a duniya da lahira [Aal Imrān, 3:104];
yana da ladan kwatankwacin mutanen da suka bi shi
[Muslim]; yana samun lada wanda ba ya yankewa bayan
mutuwarsa [Muslim]; yana samun addu’ar neman gafarar
Allah (Maxaukaki) daga waxanda ke sama da qasa, har da
tururuwar da ke cikin rami, da kifin da ke cikin teku [Xabarāni]; yana samun matsayin da alhairinsa ya fi duniya
da abin da ke cikinta [Bukhari].
2. Yin biyayya da xa’a ga umurnin Manzon Allah [Ahmad da
Bukhari] da yin koyi da Annabawa [Yusuf, 12:108].
3. Samun uzuri wajen Allah (Maxaukaki) a ranar qiyama [A’arāf, 7:164].
4. Neman tsira da kuvuta daga fitinar duniya da lahira [Anfāl,
8:25].
5. Al’umma ta gyaru kuma al’amarinta ya kyautatu.
6. Qalubalantar varnar `yan bidi’a, da bayyana wa al’umma gaskiya, da kare martabar sahihin addini [Nisā, 4:104].
7. Mutane su fahimci gaskiya, kuma su iya bambancewa a
tsakanin gaskiya da qarya [Nur, 24:54].
8. Samar da aminci a cikin al’umma [Hud, 11:117].
9. Tabbatar da manufar da’awar Sunnah, da yaxa ta, da kare
muradunta.
Ana kiran mutane ne zuwa ga sanin Allah (Mai girma da xaukaka)
da sunayenSa da siffofinSa, da sanin Shari’arSa da ke kai mutane zuwa
ga aljanna, da sanin sakamakon yin maSa xa’a ko kangarewa, kamar
yadda Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
koyar da Mu’azu ibn Jabal (Allah Ya yarda da shi) a lokacin da ya tura
shi zuwa Yemen [Bukhari da Muslim]. Za a yi wa mutane da’awah a
kowane lokaci, gwargwadon yanayi da iko: dare da rana, kamar yadda
Annabi Nuhu (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi [Nuh,
71:5]; a cikin halin tsanani da qunci ko yalwa, kamar yadda Annabi
Yusuf (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi a cikin
kurkuku [Yusuf, 12:39-40]; hatta a cikin ciwon ajali, kamar yadda
Annabi Ya’aqub (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi ga
`ya`yansa [Baqarah, 2:133]; da lokacin gargarar mutuwa, kamar yadda
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya yi
wasiyya game da kiyaye salla da haqqoqin bayi [Ahmad, Abu Dawud, Nasā’i, Baihaqi, Ibn Hibbān da Xabarāni].
Ana gina da’awa ce a bisa asasin ilmi, da fahimtar hali, da yanayi da
matakin ilmin wanda za a yi wa da’awar, da fahimtar halin da a ke ciki,
152
taimakon dattawan qwarai, da sauran mutanen kirki
wajen ganin `ya`yansu sun samu tarbiyya. Babu laifi su
haxa `ya`yansu abota da `ya`yan da aka san suna da
tarbiyya, ko kuma su tura su gidajen mutanen da suka
shahara da xabi’un qwarai domin su koyi tarbiyya. Idan
an yi baqon malamin Sunnah, iyaye su tafi da `ya`yansu
wajensa domin ya yi masu nasiha tare da jawo hankali,
kuma ya kwaxaitar da su a kan shiga cikin harkokin
da’awa. Idan an samu hali, iyaye su tafi da `ya`yansu
ziyarar malaman Sunnah a wasu garuruwan domin a
saba wa yara lazimtar mutanen kirki da son jin alhairi.
QALUBALEN DA KE FUSKANTAR TARBIYYA
A yau, tarbiyya a cikin al’ummar musulmi na fuskantar
matsaloli, da qalubale iri-iri. Waxannan matsaloli sun shafi
cikin gida da waje, kuma suna yin karen-tsaye ga tarbiyyar
`ya`yan musulmi.
da fahimtar hanyoyin isar da da’awar, waxanda suka haxa da rediyo da
talbijin da yanar gizo da wayar hannu da jarida da mujalla da allon
masallaci. Za a iya gudanar da da’awa ta hanyoyin shirya darussan ilmi,
da muhadarori, da buxe makarantun islamiyya ko boko, da makarantun
hardar Alqur’ani, da ziyarar asibiti ko gidan yari, da ziyarar gidan
marayu, da filin idi, da sauran wuraren da a ke taruwa.
Ya kamata mai da’awah ya fara gyara kansa saboda tasirin yin haka a cikin da’awah [Hud, 11:88; An’ām, 6:14]; daga nan sai makusantan
shi, kamar ma’aura da `ya`ya da `yan’uwa da dangi [Shu’arā, 26:214];
daga nan sai maqwabta na kusa da na nesa [An’ām, 6:92]; sannan
sauran mutanen duniya gwargwadon iko da halin da a ke ciki [Ibrahim,
14:1].
Lallai ne mai da’awa ya mallaki siffofi guda takwas: taqawa; da
ikhlasi; da gwargwadon ilmin da ya ke buqata don yin da’awar; da
zamantowa kyakkyawar abin koyi; da qanqan da kai; da juriya; da
la’akari da halin wanda za a yi wa da’awar.
153
Daga cikin manyan qalubalen da ke fuskantar tarbiyya,
akwai:
1. Talauci272
272
Talauci ya qunshi yanayin rashin mallakar abin da a ke buqata a
cikin rayuwa, da ya haxa da abinci, da abin sha, da muhalli. Masana
ilmin tattalin arziki sun kasa talauci gida biyu: (1) mai dama-dama, da
ke haifar da yanayin da mutane za su rasa abincin da ke gina jiki, da
abubuwan more rayuwa (2) mai tsanani, da ke haifar da yanayin da
mutane da qyar za su rayu, yanayin daga shi sai mutuwa, saboda rashin
abinci, da ruwan sha tsaftatacce, da wajen kwana, da ilmi, da abubuwan
da za su kyautata tsaftar muhalli.
A yau, matsalar talauci na xaya daga cikin matsalolin da suka fi
addabar mutane. A qididdigar da cibiyar ICPD ta yi a shekarar 2002, an
qiyasta cewa fiye da mutane biliyan xaya ne ke rayuwa a cikin
matsanancin talauci. A Nijeriya, binciken da aka gudanar a tsakanin 2006 zuwa 2007 ya gano cewa kusan kashi biyu bisa uku (⅔) na ‘yan
Nijeriya na fama da matsanancin talauci, kuma suna rayuwa a kan qasa
da dalar Amurka guda xaya ($1) a kowace rana, duk da cewa Nijeriya
ta samu fiye da dala biliyan xari uku ($300 billion) daga man fetur da
iskar gas, tun daga 1960 zuwa yau.
Ba da daxewa ba, a cikin shekarar 2008, tsohon gwabnan babban
bankin Nijeriya (CBN), Farfesa Soludo, ya bayyana cewa kimanin
kashi saba’in bisa xari (70%) na mutanen da ke zaune a arewacin
Nijeriya, na rayuwa a kan qasa da naira dubu huxu (N4000) a kowane
wata. A qiyasin da aka yi wa mutanen da ke rayuwa a cikin jihohin
arewa, an bayyana cewa kashi 95% a jihar Jigawa, kashi 89.7% a jihar
Kebbi, kashi 88.6% a jihar Kogi, kashi 86.3% a jihar Bauchi, kashi
85.2% a jihar Kwara, kashi 83.3% a jihar Yobe, kashi 80.9% a jihar
Zamfara, kashi 77% a jihar Gombe, kashi 76.8% a jihar Sokoto, da
kashi 71.7% a jihar Adamawa na rayuwa a kan qasa da naira xari da
talatin (N130) a kowace rana, ko kuma naira dubu huxu (N4000) a
kowane wata.
Bayan wannan, duk da irin rawar da ilmin boko ke takawa a wajen
kawar da talauci da kawo ci gaba ga al’umma, musamman a wannan
zamani, mutanen arewa, waxanda galibinsu Musulmi ne, an bar su a
can baya. Misali, tsohon gwabnan CBN xin, ya bayyana cewa a cikin
fiye da xalibai miliyan xaya (1,000,000) waxanda suka zauna wa
jarabawar share fagen shiga jami’a a shekarar 2008, xalibai dubu
saba’in da uku (73,000) ne kawai daga dukkan jihohin arewa in ban da
jihohin Kogi da Kwara da Benue, a yayin da a jihar Imo kawai, an
154
2. Saxaxowar munanan aqidu da hanyoyin vata273
samu fiye da xalibai dubu xari (100,000). Wannan na nuna cewa babu
mamaki idan talauci ya yi wa Musulmin Nijeriya kaka-gida,
musamman waxanda ke zaune a arewa.
Musulunci na kallon talauci a matsayin musiba, wadda ke auka wa
mutane, kuma ya kamata a nemi tsarin Allah (Mai girma da xaukaka)
daga gare ta, kuma a yaqe ta, saboda mummunar tasirinta a kan aqidar
mutane, da mu’amalarsu. Talauci ba abin so ba ne, kuma ba a yin tutiya
ko qafafa da shi, ballantana ya zamanto abin alfahari. Talauci na da
haxari mai yawan gaske a kan aqida, da xabi’a, da mu’amala, da
tunanin mutane. Talauci na xaya daga cikin manya-manyan dalilan
yaxuwar munanan xabi’u da ayyukan alfasha, kamar sata da zina da
kisan rai.
Talauci na xaya daga cikin abubuwan da ke yin karen-tsaye ga
tarbiyya. Da yawa daga `yan matan da ke yin talla a cikin kasuwa ko a
tashar mota ko a gidajen mai, suna yi ne saboda talaucin iyayensu. Ba
wani abu ne voyayye ba cewa irin wannan tallace-tallace na daga cikin
abubuwan da ke gurvata tarbiyyar `ya`ya. Haka kuma, wani lokaci,
waxansu iyayen ba su iya kwava wa `ya`yansu, musamman `yan mata,
a lokacin da su ke yin abubuwan da ba su dace ba, kasancewar sun kasa
xauke wa `ya`yan nasu larurorin rayuwa.
Musulunci ya xauki matakan yin faxa da talauci, da magance
matsalolinsa ta hanyoyin da suka haxa da: (1) ilmantar da mutane
sahihiyar aqidar cewa arziqi daga Allah (Maxaukaki) ya ke; abin da
Allah Ya raba wa bawa, shi ne nasa, kuma wajibin kowane musulmi shi
ne ya yi haquri da musibar talauci, sannan ya xauki matakan kawar da
shi (2) neman tsari daga talauci ta hanyar addu’o’i (3) zaburar da
mutane a kan yin aiki, da neman na kai, da dogaro da kai, da kai-kawo
wajen neman abin rayuwa (4) haramta zaman banza, da barace-barace,
da maula, da sana’ar roqo (5) tabbatar da taimakekeniya a cikin
al’umma, ta hanyar tallafi daga iyali da `yan’uwa da dangi, da tallafi
daga mutanen gari, da kuma tallafi daga hukuma. 273
Daga cikin munanan aqidun da ke yin karan-tsaye, da barazana ga
tarbiyyar Musulunci a wannan zamani, akwai:
1. Aqidar Shi’a, wadda ke karantar da zagin sahabban Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), da kafirta su, musamman Abubakar da Umar da Uthmān da Mu’āwiyah da Amr
ibnul ‘Āss da Mughīrah ibn Shu’ubah da Xalha da Zubair da
Abdur-Rahmān ibn ‘Auf da A’isha da Hafsah (Allah Ya yarda da
155
su). Haka kuma, `yan shi’a na da aqidar cewa sahabban Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) gaba xayansu
sun yi ridda bayan rasuwar Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) in ban da waxansu `yan tsirarun da ba su
wuce guda ashirin da biyar ba.
Waxanda ke bin aqidar shi’a na ganin cewa A’isha (Allah Ya
yarda da ita), matar Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi) ta yi zina, kuma ta cancanci zagi da la’ana, duk
da cewa Allah (Maxaukaki) Ya tsarkake ta; Ya wanke ta daga
zargin da munafukai suka yi mata; Ya yi kashedi ga waxanda ke
yaxa labarin; Ya qarya ta su; kuma Ya tabbatar da cewa waxanda
ke faxin haka ba mutanen kirki ba ne [Nur, 24:11-25]. `Yan shi’a na da aqidar cewa Abubakar da Umar da Uthmān
(Allah Ya yarda da su) ba halifofin Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi) ba ne, domin wai sun ha’inci Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), kuma wai sun qi zartar da wasiyyar da ya yi masu cewa wai Aliyyu ibn Abi Xālib
(Allah Ya yarda da shi) shi ne zai zamanto halifa a bayansa. Bayan
wannan, `yan shi’a sun soki Abu Hurairah (Allah Ya yarda da shi),
kuma sun zarge shi da cewa wai yana qirqiro hadisan qarya. Amma
a nasu vangaren, `yan shi’a sun qirqiro hadisan qarya valo-valo
domin su kare munanan aqidunsu, da kaidinsu game da Musulunci
da musulmi; kuma suna da xabi’ar watsi da duk wani hadisin da ya
sava wa ra’ayoyin da suka gina addininsu a kai.
`Yan shi’a na ganin halaccin auren wacin gadi (auren mutu’a), da al’adar ba da aron farjin mace (i’āratul furūj), da halaccin jin
daxi da jaririyar da ke shan nono, da halaccin saduwa da mace a
duburarta, da ganin rashin wajibcin sallar Juma’a, har sai
Mahadinsu ya bayyana, da sauransu. Haka kuma, suna ganin
halaccin voye wa mutane gaskiyar abin da ke cikin zukatansu, tare
da bayyanar da savanin haka a fili, wai da sunan tuqiyyah. Bayan
wannan, `yan shi’a sun sava wa musulmin duniya a cikin
mas’alolin Alqur’ani, da rukunan Musulunci, da shugabanci. Suna
da aqidar cewa Alqur’anin da ke hannun Musulmi bai cika ba, wai saboda Abubakar da Umar da Uthmān da waxansu sahabbai (Allah
Ya yarda da su) sun yi qari da ragi a cikinsa. A wajen `yan shi’a,
Alqur’anin gaskiya yana hannun Mahadinsu, wanda ya shige rami
tun yana rarrafe, yau fiye da shekara dubu xaya, bai fito ba. A
da’awarsu, idan Mahadinsu ya fito, zai bayyanar da Alqur’anin
gaskiya. Amma a babin tuqiyya, `yan shi’a na karanta Alqur’anin
156
da ke hannun sauran Musulmin duniya a halin yanzu, kuma suna
bayyana shi a cikin jama’a, sannan suna qaryar cewa ba su da wani
Alqur’ani savanin wanda ke hannun sauran Musulmi.
A vangaren rukunan Musulunci, `yan shi’a sun qara rukunin yarda da limanci, da kuma shugabancin Aliyyu ibn Abi Xālib da
Al-Hasan da Al-Husain (Allah Ya yarda da su) da sauran mutane
guda tara, waxanda suka ga damar zave daga zuriyyar Al-Husain, a
matsayin xaya daga cikin rukunan Musulunci/imani. Dangane da
shugabanci, `yan shi’a ba su yarda da halifancin Abubakar da Umar da Uthmān (Allah Ya yarda da su) ba. Hasali ma, suna xaukarsu
kafirai, kuma maciya amanar Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi). A wajen `yan shi’a, waxancan limaman nasu
guda goma sha biyu, su ne halifofin Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi). Kuma suna da aqidar cewa
limamansu guda goma sha biyu, suna da matsayin da ya fi na
kowane mala’ika ko Annabi a wajen Allah; kuma wai sun san
gaibu; kuma ba su yin kuskure, ba su rafkannuwa; ba su mantuwa;
sannan kuma, ba su mutuwa sai lokacin da suka so.
Bugu da qari, `yan shi’a na da xabi’ar fakewa a qarqashin
da’awar son mutanen gidan Manzon Allah (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi) domin ganin sun yaudari mutanen da ba su da
ilmin sharrin addinin shi’a, ta yadda ba za a yi saurin fahimtar
bala’in da ke tattare da su ba. Yana daga hanyoyin da su ke bi
wajen yaudarar mutane, xabi’ar bayyana cewa wai an zalunci Nana Fāximah (Allah Ya yarda da ita), aka hana ta gadon dukiyar
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi); da kuma xabi’ar bayyana baqin ciki a ranar āshura, wato goma ga
watan Muharram, wai don tunawa da ranar da aka yi wa sayyidina Husain ibn Abi Xālib (Allah Ya yarda da su) kisan gilla, duk da
cewa su ne suka yi masa alqawarin qarya, kuma suka gayyace shi zuwa Kūfa, sannan, suka bar shi a hannun maqiyansa. Abin
mamaki shi ne, `yan shi’a na kururuta maganar gadon Fāximah ce
kawai, amma ba su yin maganar gadon matan Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi), da kuma sauran
`yan’uwansa daga vangaren mahaifinsa, tun da dai suna da gado a cikin dukiyar, kamar yadda Fāximah ta ke da shi. Mene ne dalilin
da ya sa `yan shi’a ba su yin magana a kan gadon waxannan, sai dai na Fāximah kawai?
Bala’i da fitinar `yan Shi’a ba su qyale kowane Musulmi ba,
domin kuwa har Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
157
gare shi) ma bai tsira ba. Littafansu na cike da maganganun rashin
kunya da rashin mutuntawa ga Manzon tsira (tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi). Misali, ya zo a cikin littafin
na As-Sayyid Husain Al-Musawiy, wanda `yan Shi’a
suka kashe daga baya, kamar yadda suka kashe Musa Al-Musawiy da Ahmad Al-Kātib saboda sun tona masu asiri, cewa: (i) Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kalli Zainab
bint Jahash (Allah Ya yarda da ita) tana wanka tsirara, har ta ba shi sha’awa, kafin Zaid ibn Hārithah (Allah Ya yarda da shi) ya sake
ta; (ii) Aliyyu (Allah Ya yarda da shi) ya zauna a kan cinyar Nana
A’isha (Allah Ya yarda da ita), kuma da ta yi masa magana, sai
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce
mata kada ta cutar masa da xan’uwa; (iii) Aliyyu (Allah Ya yarda
da shi) ya kwanta a tsakanin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) da Nana A’isha (Allah Ya yarda da ita); (iv)
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) na
sumbantar Nana Faxima (Allah Ya yarda da ita), kuma ya sanya fuskarsa a tsakanin nononta; (v) za a qona al’aurar Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) saboda ya yi kwanciyar aure da Nana A’isha (Allah Ya yarda da ita); (vi)
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya
voye wasiyya game da shugabancin Aliyyu (Allah Ya yarda da shi)
saboda tsoron Abubakar da Umar (Allah Ya yarda da su). Domin
qarin bayani, a karanta na As-Sayyid
Husain Al-Musawiy, da na Abu Khalīfah
Aliyyu ibn Muhammad Al-Qudaibiy, waxanda dukkansu malaman
shi’a ne a lokacin da suka rubuta littafan.
Babu shakka, waxannan miyagun aqidun shi’a na karan-tsaye
ga tarbiyyar al’ummar musulmi, domin kuwa ta wace hanya
kyakkyawar tarbiyya za ta samu ga `ya`yan da suka taso a kan
aqidar cin mutuncin Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi), ko watsi da hadisan Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi), ko zagin sahabbai da qudurce
cewa sun yi ridda, ko zagin A’isha (Allah Ya yarda da ita) da
qudurce ta yi zina, ko auren mutu’a, ko ba da aron mace domin a
kwana da ita?
Saboda munin aqidar shi’a da haxarinta ga Musulmi, malamai
sun ba da fatawoyi iri-iri a kansu. A cikin littafin
, Dokta Ibrahim ibn `Aamir Ar-Ruhailiy, ya ciro
158
fatawoyin malamai fiye da ashirin dangane da `yan shi’a. Daga
ciki: (a) An tambayi Imām Mālik ibn Anas (Allah Ya jiqan shi)
dangane da waxanda ke zagin sahabban Annabi (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi), sai ya ce:
.
[Ba su da rabo a cikin Musulunci]
Kuma an ruwaito ya ce:
[Kada ku yi masu magana, kuma kada ku yi ruwayar (Hadisi)
daga gare su, domin suna yin qarya (a matsayin addini)]
(b) Imām Shā’fi’i (Allah Ya jiqan shi ) ya ce:
[Daga cikin waxanda ke bin son zuciyarsu, ban ga waxanda suka kai Rāfidah (masu zagin sahabbai) qarya da shaidar zur a
cikin da’awarsu ba]
(c) Al-Qāsim ibn Salām (Allah Ya jiqan shi) ya ce:
[Na zauna da mutane (dabam daban), kuma na tattauna da `yan
falsafa, amma ban ga qazamai, kucakai, masu raunin hujja, kuma wawaye ba, kamar Rāfidah (masu zagin sahabbai)]
(d) An tambayi Imām Ahmad ibn Hanbal (Allah Ya jiqan
shi) game da wanda ya zagi Abubakar da Umar (Allah
Ya yarda da su), sai ya ce:
[Ina ganin ya fita Musulunci]
(e) Ibn Taimiyyah (Allah Ya jiqan shi) ya ce:
[Babu waxanda suka kai `yan shi’a sharri da jahilci da zalunci da
kusanci ga kafirci da fasiqanci da savon Allah, daga cikin dukkan
qungiyoyin bidi’a da vata waxanda ke dangantuwa zuwa
Musulunci]
159
Duk da irin munin aqidun shi’a, da fatawoyin da malaman farko
suka ba da a kansu, sai ga wani matashin xariqar tijjaniyya daga
Kaduna yana bayyana cewa wai `yan shi’a ba su zagin sahabbai,
kuma ma wai idan ma sun zagi sahabbai, ba a ga suna yin maulidi
ba, saboda son Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi)? Ya faxi wannan maganar a cikin lakcar da ya gabatar wa
`yan shi’a a garin Zaria, a lokacin taronsu na makon haxin kai,
kuma ya maimaita irin wannan mummunar magana a xakin taron
musabaqar Alqur’ani wanda ke Kinkinau, Kaduna, a wajen taron
qara wa juna ilmi dangane da ganin wata da haxin kai, a ranar Asabar, Rabi’uth-Thāni 2, 1430 (March 28, 2009). A nan take,
kusan dukkan mahalarta taron, waxanda suka haxa da shaihunnan
Tijjaniya, suka yi Allah wadai saboda qaryar da ya sharara. Bayan
shi, a cikin tafsirin Ramadan na shekarar Hijira 1429, da a ke sanya
wa a NTA, Zaria, daga wata zawiyyar Tijjaniyya, a Tudun Wada,
Zaria, wani matashin da a ke yi wa zaton wayayye ne, ya bayyana
cewa aqidodin shi’a wai sahihai ne, kuma wai ba su da matsala.
Abin da ya xaure wa mutane kai shi ne: shin waxannan matasan
tijjaniyya sun fi shehunnansu ilmi ne? Ashe babban Shehi bai yi
kaca-kaca da `yan shi’a ba, a cikin tafsirin Ramadan na shekarar
1428 da 1429? Ashe `yan shi’a ba su yi barazanar kashe wani
Shehin da ke yin tafsiri a Chikaji, Sabon Gari, Zaria ba, saboda ya
bayyana sharrinsu, da bala’in da ke cikin aqidunsu? Ko kuma sun fi
shehunnansu bincike ne game da aqidar shi’a? Ko kuwa sun raina
shehunnansu ne? Anya, babu wata alaqar sirri da ke tsakanin
waxannan matasan tijjaniya da `yan shi’a? Ko kuwa dai duk a
babin haxa qarfi da qarfe ne domin a yaqi Ahlus-Sunnah (`yan
Izala, Salafiyyah)? Shi dai matashin tijjaniyyar da ke Kaduna an
fahimci cewa an turo shi ne domin ya qalubalanci babban Shehi,
kuma ya share fagen zama halifan tijjaniya idan ya rayu bayan
rasuwar babban Shehi, tun da dama waxanda ke xaukar nauyin
yaxa karatunsa abokan hamayyar babban Shehin ne. Shi yasa ya ke
ta yin vavatu da qarerayi dabam daban, da tavargaza iri-iri, a
rediyo, don ya ci kasuwar muridai, kuma ya bayyanar da
matsayinsa a cikin tijjaniyyar.
Shi kuwa matashin Zaria, muna zargin cewa son zuciya ne
kawai ya ke damunsa, da baqar qiyayya ga Sunnah, da mummunar
hassada ga Ahlus-Sunnah, domin kuwa ya daxe yana faxin cewa
kalmar ko isxilahin (aqida) ba a san ta ba a zamanin
160
magabata. A cewarsa, Wahabiyawa ne, wato, `yan Izala, suka fara
amfani da kalmar aqida. Ba domin hassadar da ya ke yi wa Ahlus-
Sunnah ba, mene ne yasa zai ce: `yan shi’a na da
(sahihiyar aqida), bayan kuwa ya ce kalmar sabon isxilahi ne
da Wahabiyawa suka qirqiro? Kuma shin da gaske aqidar `yan
shi’a sahihiya ce a wajensa? Dangane da isxilahin , shin
gaskiya ne cewa magabata ba su yi amfani da shi ba? Mene ne zai
ce game da waxannan littafai: na Abu Yālā; da
na Al-Lālakā’iy; da na Ibn Hanbal; da
na Abu Uthmān As-Sābūniy; da
na Abu Bakr Al-Ismā’īliy; da na Ax-Xahhāwiy; da
na Ibn Qudāmah; da na As-Safārīniy?
Marubutan waxannan littafai ba su yi amfani da isxilahin aqida ba?
Ko kuwa ba su a cikin magabata? Ashe ba shi ne ya ke da’awar
cewa yana karanta littafan Ibn Taimiyyah, da littafan Ibnul Qayyim, kuma ya mallaki kaset-kaset xin Nāsiruddīn Albāni da
rubuce-rubucensa domin ya bayyana kurakuransu ba? Mene ne ya
sa bai karanta littafan shi’a domin ya fahimci munin aqidunsu ko
kuma sahihancinsu ba? Allah Ya shiryar da mu.
2. Aqidar Khawārij, waxanda suka yi tawaye ga Aliyyu ibn Abi Xālib
(Allah Ya yarda da shi) saboda yarda da sulhun da ya yi a tsakaninsa da Mu’awiyah ibn Abi Sufyān (Allah Ya yarda da su).
Khawārij sun kafirta waxanda suka yarda da wannan sulhu; sun
zarge su da yin ridda; suka yi da’awar cewa Aliyyu ibn Abi Xālib
da A’isha da Xalha da Zubair da Amr da Abu Musa sun yi ridda;
kuma suka xaura yaqi da sayyidina Aliyyu (Allah Ya yarda da shi);
sannan suka halatta wa kansu zubar da jinin wanda duk ya sava wa
da’awarsu. Aqidar khawārij ta ginu ne a kan kafirta musulmi a dalilin
manyan zunubai, da yin tawaye ga shugabannin musulmi, da
janyewa daga cikin jama’a. Ana gane khawarijawa ta hanyoyi guda
uku: (1) kafirta musulmi saboda sun aikata manyan zunubai
waxanda ba su kai matsayin shirka ba (2) yin tawaye ga
shugabanni, da yin fito-na-fito da su (3) kare aqidunsu ta kowace
hanya, da ganin halaccin zubar da jinin musulmi, wai da sunan
jihadi ko gusar da abin qi.
161
Daga cikin siffofin khawārij a wannan zamani, akwai: yin
tawaye ga shugabanni, da yin fito-na-fito da su; da tsanani a cikin
addini; da zurfafawa a cikin ibada; da raina manyan malamai, da
wulaqanta su, da zarginsu da munafunci, da kuma ganin halaccin
kashe su; da qarancin karatun addini da rashin aiki da fahimtar
magabata na qwarai; da kafirta musulmi saboda zunubin da bai kai
matsayin shirka ba; da yin kira zuwa ga jahilci; da kushe karatun
boko ko kuma ganin kafircin karatun boko, da kira zuwa ga
janyewa daga aikin gwabnati; da ganin halaccin qwace dukiyar
musulmi; da ganin halaccin kashe duk wanda bai yarda da aqidarsu
ba; da kuma ganin wajibcin yin hijira zuwa gare su.
Babu shakka, idan yaro ya taso a kan wannan mummunar aqida,
zai zamanto barazana ga tarbiyyar `ya`yan musulmi. Haka kuma,
waxanda ke da aqidar khawarijanci a yau, na jawo wa musulmi
gori, da ci baya, da kuma qauyanci.
3. Aqidar Istishrāqiyyah, wato, masu bin Orientalism, waxanda
galibinsu ba musulmi ba ne, amma suka karanta addinin musulunci,
bisa mummunar manufar haifar da shubuhohi game da fahimtar
addini; da sanya shakku game da aikin Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) na isar da Alqur’ani da
Sunnah; da jefa tunanin cewa tanade-tanaden musulunci ba za su
iya wadatar da mutanen wannan zamani ba saboda ci gaba da
wayewar da aka samu a duniya; da jefa wa musulmi shakku
dangane da sahihancin hadisan Manzon Allah (tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi); da qoqarin amfani da tsukakken tunani
da taqaitacciyar qwaqwalwa wajen tabbatar da inganci ko rashin
ingancin hadisai; da zargin manyan malaman hadisi, irin su Imam
Az-Zuhri, da cewa sun qirqiro hadisan qarya; da zargin sarakuna
da halifofin musulmi cewa sun sanya malamai sun qirqiro hadisan
da za su goyi bayan zaluncinsu; da sauransu.
Waxanda ke da irin wannan mummunar kaidi game da
karantarwar musulunci sun samu nasarar gurvata tunanin irin su Xāha Husain (a qasar Masar), da Abdullah Chakralawi da Ghulām
Ahmad Pervaiz (a India) da Zia Gogelup (a Turkiyyah). A dalilin
haka, sai aqidar istishrāqiyya ta shigo cikin qasashen musulmi, ta
hanyar rubuce-rubucen da irin waxancan malamai suka yi bayan
sun tasirantu da ra’ayoyin mustashriqai irin su Sprenger, da
Edward, da Salisbury, da Houdas, da Goldziher, da Wensinck, da
Watt, da Schacht, da Robson.
162
Aqidar istishraqiya na da mummunar tasiri a kan tarbiyyar
`ya`yan musulmi, musamman a vangaren aqidarsu da tunaninsu
game da Shari’ar Musulunci, kamar yadda mu ke gani a wannan
zamani. Haka kuma, mummunar tasirin aqidar istishraqiya ya
sanya waxansu `yan bokon zamani na yin dakon aqidar , wato,
aqidar amfani da sakamakon binciken kimiyyar zamani a matsayin
ma’aunin inganci ko raunin Hadisi, zuwa cikin Musulmi.
4. Aqidar Qala-qato, wadda ta qunshi da’awar amfani da Alqur’ani
kaxai, a cikin dukkan wani abin addini, tare da watsi da hadisi, da
kuma sukar littafan fiqihu. `Yan qala-qato na da’awar cewa Allah
(Maxaukaki) Ya umurci musulmi da yin riqo da Alqur’ani kawai,
kuma babu inda aka ce a yi amfani da hadisi ko kuma ra’ayin
waxansu mutane. Wannan ya sa a ke kiransu da suna `yan qala-qato, ko kuma qur’aniyyun, wato, waxanda ke da’awar riqo da
Alqur’ani zalla, kuma su ke xaukar hadisai da littafan fiqihu a
matsayin maganar wani qato.
`Yan qala-qato ba su amfani da wani hadisin Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sai idan ya yi dai-dai
da zahirin ayar Alqur’ani; kuma sun sava wa dukkan musulmin
duniya a wajen tauhidi, da sallolin farilla da na nafila, da zakka, da
azumin farilla da na taxawwu’i, da aikin hajji, da aure, da saki, da
idda, da hukunce-hukuncen tsarki, da jana’iza, da sallar idi, da
sallar juma’a, da sauransu.
`Yan qala-qato na ganin cewa haramun ne a ci kifi idan ba a
yanka ba; kuma suna ganin cewa wajibi ne macen da ke yin haila ta
yi salla da azumi. Waxansu daga cikin `yan qala-qato ba su yarda
cewa Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) yana da
sahabbai (Allah Ya yarda da su) ba, in ban da Zaid (Allah Ya yarda
da shi), kasancewar shi kaxai ne Allah (Maxaukaki) Ya ambaci
sunansa valo-valo a cikin Alqur’ani.
Wannan mummunar aqida, ta ci karo da aqidar Musulunci,
kuma ta sava wa abin da musulmin duniya suka fahimta. Malamai
da yawa sun kafirta waxanda ke da irin wannan bamagujiyar aqida.
Misali, Muhammad ibn Nasr Al-Marwazi, a cikin As-Sunnah, ya ce
waxanda ke raddin sahihan hadisan Manzon Allah (tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi) sun fita daga cikin jama’ar musulmi; Al-Ājurri, a cikin Ash-Sharī’ah, ya ce kasancewar ba za a
iya fahimtar Alqur’ani ba sai ta hanyar Sunnah, waxanda ke qin yarda da Sunnah, sun yi ridda; Ibn Hazm, a cikin Al-Ihkām fi
163
Usulil Ahkām, ya kafirta su; Ibn Taimiyyah, a cikin Al-Wasiyyatul Kubrah da Ibn Daqīqil ‘Eid, a cikin Sharhul Ilmām, sun kafirta su;
As-Suyuxī, a cikin Miftāhul Jannah fil Ihtijāj bis Sunnah, ya ce
waxanda ke inkarin ingantattun hadisai, kafirai ne, kuma Allah (Maxaukaki) zai tayar da su tare da Fir’auna da Hāmān a ranar
qiyama.
Babu shakka, aqidar `yan qala-qato na yin barazana ga tarbiyyar
`ya`yan musulmi, musamman a Nijeriya, da qasar Nijer, kuma tana
dankwafe qwaqwalwar waxanda ba su san inda aka sa gaba ba,
sannan, tana nisantar da mutane daga Musulunci gaba xaya, ba tare
da sun sani ba.
5. Aqidar , wato, aqidar kore bambanci a tsakanin Musulunci
da kiristanci ko yahudanci (interfaith) bisa hujjar cewa mabiyansu
sun yarda da Allah Ubangiji a matsayin abin bauta, kuma suna
iqirarin bin littafin da aka saukar daga sama. Wannan mummunar
aqida ta shigo Nijeriya ta hanyar waxansu matasa masu kishin
addini, amma ba tare da ilmi ba. Da yawansu ba su yi karatun
addini ba sai ta hanyar jaridu da mujallu da littafan da aka fassara
addinin Musulunci bisa fahimtar abokan gaban Musulmi.
Mabiya wannan aqida na bi lungu-lungu don tallata
bamagujiyar aqidarsu, wai da sunan qoqarin wanzar da zaman
lafiya, ko sasantawa a tsakanin Musulmi da mabiya addinin kirista.
Domin abin na su ya yi masu armashi, qungiyoyin da ke tallata
wannan varna suna zaven shugabanni guda biyu: Imam, domin ya
wakilci Musulmi, da Pastor, da ke wakiltar kirista. A galibi, wanda
a ke kiransa Imam xin, bai yi karatun a zo a gani ba game da
addinin Musulunci, kuma bai san makircin maqiyan Musulunci ba.
Malaman Musulunci sun ba da fatawar haramcin wannan
yunquri, da haxarin shiga cikin wannan baqar harka, sai dai idan za
ta samar da damar tattaunawar ilmi a tsakanin Musulmi da kirista
domin a nuna masa varnar da kiristanci ya qunsa. Abin mamaki, a
cikin `yan dakon wannan bamagujiyar aqida a Nijeriya, akwai
wanda a ke yi wa zaton ilmi da wayewa a nan Kaduna, shi kuwa
shugaban nasu, dama can bai da ilmin a zo a gani.
Aqidar daidaituwar mabiya addinai dabam daban na da
mummunan tasiri a kan tarbiyyar al’umma. Idan yaro ya taso a
kanta, ko kuma ya yi karo da waxanda ke yaxa ta, za a cire masa aqidar Al-wala’u wal barā daga zuciyarsa, duk da cewa tana daga
cikin abubuwan da tauhidi ke lazimta wa Musulmi.
164
3. Savani a tsakanin iyaye ko kuma rabuwar aure 274
274
Aure aya ce daga cikin ayoyin Allah, kuma ni’ima ce daga cikin
ni’imominSa. An shar’anta aure a Musulunci, aka qarfafe shi, aka
kwaxaitar da yin shi, aka hana yin tabattul (aqidar rashin yin aure
saboda a samu damar bauta wa Allah sosai), kuma aka bayyana cewa
barin yin aure domin a samu damar yin ibada ya sava wa Sunnar
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).
Aure na da manufofi da fa’idodin da suka haxa da: (1) biyayya ga
Allah (Maxaukaki) da nisantar savo (2) samun ladan ciyar da iyali (3)
kamewa daga zina, da tsare mutunci (4) samar da iyali da taimakawa
wajen yawaita al’umma (5) xorewar jinsin xan Adam (6) samun xa na
qwarai da zai yi wa iyayensa addu’a bayan mutuwarsu (7) samun
natsuwa da sukuni da kwanciyar hankali (8) biyan buqatar sha’awa ta
xabi’a (9) samun ladan yin tarbiyya da xaukar xawainiyar `ya`ya (10)
kai wa ga matsayin kamala a cikin mutane (11) dacewa da abin da
Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ke so (12)
raya Sunnar Annabawa (13) dacewa da samun taimakon Allah idan aka
yi aure saboda kange kai daga zina.
Abubuwan lura a wajen zaven abokiyar zama su ne: (1) riqo da
addini [Baqarah, 2:221] (2) sahihiyar aqida [Tirmidhi] (3) kyawawan
xabi’u [Tirmidhi] (4) iya soyayya da kuma haihuwa [Ahmad da Abu
Dawud] (5) budurci, matuqar babu wata maslahar da za ta sa a fifita bazawara [Bukhari] (6) kyau [Nasā’i da Ahmad; Muwaxxa Mālik;
Ahmad]. A wajen zaven abokin zama, mace ta yi tarayya da namiji a
cikin mafi yawan waxannan xabi’u. Don haka, wajibin iyaye ne su
zava wa xiyarsu miji na qwarai bisa lura da waxannan siffofi.
Yana daga abubuwan da aka hana a cikin neman aure: (1) kaxaita da
wadda za a aura, ko yin tafiya tare da ita, ko fita yawon shaqatawa ba
tare da wani muharrami ba, ko da kuwa an biya sadaki [Bukhari da
Muslim; Ahmad da Tirmidhi] (2) tava jikin wadda za a aura, ko rungumarta, ko sumbantarta, ko da an biya sadaki [Xabarāni] (3)
maganganun batsa a wajen hira, ko aikawa da saqon da ke xauke da
maganganun batsa ko hotunan tsiraici ko sakarci ko motsar da sha’awa
ta cikin wayar tafi da gidanka (4) kwanciya (jima’i) da wadda za a aura
tun kafin a xaura auren, ko da an biya sadaki.
Fatawar da ke nuna cewa idan aka amince za a aurar da yarinya ga
mutum, kuma iyayenta ko wakilansu suka karvi sadaki, wannan
saurayin wai zai ci gaba da sha’aninsa da ita, har ma da yin jima’i,
fatawa ce da aka ginata a kan kuskure, da rashin la’akari da tasirin urf,
165
wato, al’adun da ba su yi karo da nassosin addini ba, a cikin
mu’amaloli. Duk mutanen da urfinsu ya nuna cewa ba a xaukar aure ya
tabbata a tsakanin mace da namiji har sai an tara jama’a don xaura
auren, dole ne a jinkirta zuwa wannan lokaci. Maganar cewa tun da an
kammala dukkan sharuxxan aure, ta hanyar biyan sadaki, bayan
waliyyai sun yarda za su ba da `yarsu kuma saurayi da budurwa sun
daidaita kansu, sannan an karvi sadaki a gaban a qalla mutane biyu
zuwa uku, aure wai ya tabbata a tsakaninsu, kasancewar taron xaurin
aure al’ada ce kawai, magana ce mai tsananin rauni. Daga cikin
abubuwan da ke nuna rauninta shi ne, su kansu mutane ba su yarda
cewa abubuwan da aure ke lazimtawa a tsakanin ma’aura sun tabbata a
cikin irin wannan shiri ba. Misali, idan saurayin ya mutu kafin ranar
xaura aure, ko kuma ita budurwar ta mutu, ba za a yarda wanda ke da
rai a cikinsu ya ci gadon xayan ba. Haka kuma, idan aka samu canjin
ra’ayi a tsakaninsu, saurayin ba zai ce ya fasa auren ba ta hanyar rubuta
takardar saki ko furtawa, ko kuma ita budurwar ta yanke alaqarta da shi
ta hanyar khul’i, domin za a danganta hauka ga duk wanda ya yi hakan
a cikinsu, kasancewar mutane ba su xaukar cewa sun zama ma’aurata.
Don haka, waxanda ke ba da irin wannan fatawar su ji tsoro.
Saboda muhimmancin aure, da kuma babban tasirinsa a kan
tarbiyyar `ya`ya, Musulunci ya xauki matakai na dawwamar da aure, a
tsakanin miji da mata, matuqar babu wata larurar da ta bijiro. Daga
cikin hanyoyin da Musulunci ya bi domin dawwamar da aure, akwai:
(1) fifita addini da kyakkyawar xabi’a a wajen zaven miji/mata (2)
halatta kallon wadda a ke son a aura domin kada a yi kitso da
qwarqwata (3) sharxanta yardar wadda za a aura, matuqar ta balaga (4)
hana wa miji neman kamala daga wajen matarsa, da bayyanar da
muhimmancin yin haquri da juna (5) halatta wa mutane shiga cikin
al’amarin ma’aura domin yin gyara da sulhu a tsakaninsu, idan akwai
buqatar haka (6) halatta qarya (ba yaudara ba) a tsakanin ma’aura
domin zamantakewa ta qara danqo (7) wajabta wa ma’aurata
zamantakewa kyakkyawa a tsakaninsu, ta hanyar bayyana wa
kowannensu haqqoqinsa, da kuma haqqoqin da ke kansa.
Haqqoqin ma’aurata sun kasu gida uku: waxanda suka yi tarayya a
ciki; da waxanda miji ke da su a kan matarsa; da waxanda mace ta ke
da su a kan mijinta. Haqqoqin da suka yi tarayya a kai guda uku ne: (1) haqqin jima’i da jin daxin juna [Nisā, 4:20-21; Baqarah, 2:223;
Bukhari] (2) haqqin gadon dukiyar wanda ya riga mutuwa [Nisā, 4:11-
12] (3) haqqin dangantuwar `ya`ya [Bukhari da Muslim].
166
Haqqoqin mace a kan mijinta sun haxa da: biyan sadaki [Nisā, 4:4];
xaukar nauyi da xawainiya, da ciyarwa da tufatarwa, da kula da lafiya, da wajen zama [Baqarah, 2:223; Nisā, 34]; kyakkyawar mu’amala
[Nisā, 4:19]; jima’i, gwargwadon ikonsa da yanayinsa [Bukhari da
Muslim]; rashin duka, sai in ya zama dole [Nisā, 4:34; Bukhari]; kiyaye
sirrin jima’i [Abu Dawud]; adalci a tsakaninta da kishiyarta [Nisā,
4:129; Abu Dawud]; karantar da ita addini [Tahrīm, 66:6; Bukhari];
tsare mutunci da rashin cin mutunci [Bukhari da Muslim]; rashin
watsarwa ko wofintarwa [Ahmad da Muslim].
Haqqoqin miji a kan matarsa sun haxa da: samar masa da sukuni da natsuwa a cikin gida [A’arāf, 7:189; Rum, 30:21]; yarda da
shugabancinsa ga gida [Nisā, 4:34]; biyayya cikin duk abin da ba savon
Allah ba [Hākim]; biya masa buqatar jima’i, matuqar babu larurar da
za ta hana [Tirmidhi]; rashin barin wani ya shiga gidan idan mijin ya
hana [Bukhari da Muslim]; rashin fita daga gida ba tare da izini ba [Ahzāb, 33:33]; yin masa abinci, da gyara shimfixarsa, da yin masa
dukkan nau’o’in hidama, gwargwadon iko, kuma gwargwadon urf [Ahmad; Bukhari da Muslim]; taimaka masa da nuna masa goyon baya
da qarfafa gwiwa a cikin dukkan abubuwan da Shari’ah ba ta hana ba [Nasā’i]; gode wa qoqarinsa, da rashin matsawa a kan buqatun da babu
larura [Bukhari da Muslim; Nasā’i; Hākim]; rashin yin azumin nafila
ba tare da izininsa ba, matuqar bai yi tafiya ba [Bukhari da Muslim].
Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya albarkaci wannan al’umma ta
hanyar ba ta cikakkiyar Shari’ah, da dokoki, da tsare-tsare waxanda ke
yin mata jagoranci a cikin dukkan al’amura, kuma su ke ba ta mafita
daga kowace irin matsala. Kasancewar savani a tsakanin ma’aura wani
abu ne na xabi’a, kuma dole ya auku, a lokaci zuwa lokaci, Shari’ar
Musulunci ta tanadar wa Musulmi hanyoyin warware matsalolin aure,
ko kuma savani a tsakanin ma’aura: idan matsalar daga gefen matar ce,
an tsara wa miji irin matakan da zai bi domin ganin ta dawo kan hanya kuma ta yi masa xa’a [Nisā, 4:34]; idan bijirewar ko tawayen daga
vangaren miji ne, an tsara wa mace hanyar da za ta bi wajen samar da gyara a tsakaninsu [Nisā, 4:128]; idan kuwa kowannensu na da hannu a
cikin bijirewar, ko kuma yin tawayen ga juna, kuma warware matsalar
a tsakaninsu ya ci tura, Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya ba da
umurnin a samu wakilai daga vangarorin ma’aura don zaman sulhu [Nisā, 4:35].
Bijirewa ko tawaye daga mace na xaukar fuskoki mabambanta: (1)
qin yin ado ga miji a lokacin da ya ke buqata; (2) qin zuwa shimfixarsa
ko yarda da shi a lokacin da ya ke buqatar jima’i; (3) fita gida ba tare
167
da izininsa ba; (4) qin yin masa hidima a gida; (5) qin kula da
`ya`yansa; (6) sakaci wajen bautar Allah (Mai tsarki da xaukaka) da
kiyaye dokokin Musulunci. A vangaren miji, tawaye na xaukar: (1)
girman kai a gare ta, da qin kiyaye haqqoqin da Allah (Mai tsarki da
xaukaka) ya xora masa, dangane da ita; (2) zaluntarta ta hanyar duka
ko zagi ko cin mutunci ko qin jima’i ko hana ta abinci da sauran
buqatun larura; (3) kau da kai daga gare ta; (4) qin magana da ita, da
sauransu.
Duk da waxannan matakai, akwai yiwuwar a samu savani a tsakanin
ma’aura, kuma akwai yiwuwar wannan savani ya haddasa rabuwar
aure. Savani a tsakanin iyaye, da kuma rabuwar aure, suna da
mummunar tasiri a kan tarbiyyar `ya`ya. Lallai ne iyaye su yi qoqarin
ganin sun magance savanin da ke tsakaninsu, ba tare da `ya`yansu sun
sani ba. Haka kuma, ya kamata su xauki dukkan matakan da suka dace
domin ganin rabuwar auren ba ta auku a tsakaninsu ba. Rabuwar aure a
tsakanin miji da mata na daga cikin abubuwan da ke kawo matsala ga
`ya`yan da aka haifa.
Galibi, savanin da ke aukuwa a tsakanin ma’aura na da dalilai guda
biyar: (1) yanayi da xabi’ar zuciya, ta yadda wani lokaci mutum zai
samu canjin tunani game da abokin zama; soyayya ta koma qiyayya,
qauna ta koma rashin qauna (2) rashin ikhlasi, da rashin tsarkake
zuciya game da alaqar aure, da rashin xaukar aure a matsayin ibada (3)
sakacin mace a vangaren tattalin miji da haquri da qana’a da karvar
gyara (4) matsala daga miji, a dalilin rashin adalci a tsakanin mata, da
rashin kishi, da rashin kulawa da tarbiyyar `ya`ya, da rashin zama a
gida (5) tsadar rayuwa, da rashin cikakken abin yi.
Idan savani ya auku a tsakanin iyaye, kuma iyayen suka bari
`ya`yansu suka fahimci akwai wannan savani, musamman idan
al’amarin ya kai su ga cacar baki ko zage-zage ko cin mutuncin juna ko
dambe ko cin kwalar riga ko dukar mace a gaban `ya`yan, wannan zai
sanya `ya`yan su rasa kwanciyar hankali ko kuma su xauka cewa haka
ya kamata a gina rayuwar aure. Ke nan, lallai iyaye su nisanci yin
savani a gaban `ya`yansu ko kuma tattauna matsalolin da suka shafi
zamantakewarsu a gaban `ya`yan. Yawan yin savani a tsakanin
ma’aura yana hana iyaye samun natsuwa da kwanciyar hankalin da za
su yi tarbiyyar `ya`yansu yadda ya kamata.
Mutuwar aure musiba ce ga `ya`ya, domin kuwa za su iya shiga
mummunan hali, kasancewar mahaifiyarsu ba ta a cikin gidan, kuma ba
lallai ne a dace da wadda za ta kula da su, ta xauki amanar yin masu
tarbiyya ba yadda ya dace. Haka kuma, idan ma `ya`yan na hannun
168
4. Da’awar kare `yancin mata, da kururuta haqqoqin
yara275
uwarsu ce, ko suna hannun dangin uwa, akwai yiwuwar su rasa
cikakkiyar tarbiyya, kasancewar ubansu na nesa da su; ballantana kuma
idan rashin mutunci ya shiga a tsakanin ma’aura, a lokacin rabuwa, ta
yadda uban zai yi watsi da al’amarin `ya`yansa gaba xaya.
Dalilan da ke kawo mutuwar aure sun haxa da: (1) rashin fahimtar
manufar aure a Musulunci ko yadda a ke zamantakewar aure (2) auren
dole (3) rashin tattaunawa a tsakanin ma’aura (4) talauci da sauran
matsalolin rayuwa (5) rashin ba da muhimmanci ga rayuwar aure (6)
canjin tunani game da abokin zama ko rashin samun yadda a ke zato
daga abokin zama (7) rashin kula da haqqoqin aure (8) ha’intar abokin
zama, da rashin kamun kai (9) shaye-shayen barasa ko abubuwan da ke
gusar da hankali (10) cin mutuncin abokin zama, ko wulaqanta surukai
(11) yawan duka ko zagi (12) rashin sanya ido daga iyaye ko kuma
rashin tarbiyya tun daga gida, kafin aure (13) rashin sanin hanyoyin
warware matsala idan ta auku (14) rashin agaji daga al’umma (15) son
kai, ko bin son zuciya a tsakanin ma’aura.
Ya kamata iyaye su ji tsoron Allah (Maxaukaki) game da tarbiyyar
`ya`yansu, kuma su danne zukatansu, su yi haquri da juna, su kyautata
wa juna, su kiyaye haqqoqin juna, kuma su riqa tuna makomar
tarbiyyar `ya`yansu. 275
Allah (Mai girma da xaukaka) Ya halicci namiji da mace a matsayin
vangare guda biyu na nau’in mutum, domin su yi tarayya wajen raya
duniya, kowannensu a bisa abin da ya kevanta da shi, kuma su yi
tarayya a cikin bauta wa Allah (Mai girma da xaukaka), ba tare da
bambanci a tsakaninsu ba a cikin tauhidi, da aqida, da haqiqanin imani
da miqa wuya, tare da sallamawa ga Allah; da ayyukan lada ko uquba;
da ayyukan kwaxaitarwa ko tsawatarwa; da ayyukan falala; da sauran
ayyukan wajibi. Haka kuma, an kevance wa kowannensu ayyukan da
suka dace da yanayinsa, domin a samu zaman lafiya da walwala da
kwanciyar hankali.
Ana cikin wannan hali, sai shaixan ya qawata wa mutane yin shirka
da Allah (Mai girma da xaukaka), da canza tsarin Allah, da yin zalunci
da varna a cikin qasa. Wannan ya sanya mace ta shiga cikin
mummunan hali, kuma ta fuskanci yanayi mai tsanani da mu’amala
mara kyau daga maza. Mace ba ta fita daga wannan halin qaqanikayin
ba, har sai bayan an aiko Manzon Allah (tsira da amincin Allah su
169
tabbata a gare shi). Misali, kafin zuwan Musulunci: (1) Girkawa (Greek) na xaukar mace a matsayin bishiya mai guba; qazantar
shaixan; dalilin tashe-tashen hankula da rikice-rikicen duniya; kuma
hajar sayarwa (2) Romawa (Romans) na xaukar mace a matsayin
wadda ba ta da ruhi, kuma za a iya kashe ta bisa duk wata tuhumar da
aka yi mata; ana ladabtar da ita ta hanyar zuba mata tafasasshen mai a jikinta (3) Mutanen qasar Sīn (China) na ganin cewa mace ruwan zafi
ne mai wanke nasara da walwala, kuma ruwan najasa ce da ke tafiyar
da farin ciki da dukiya; ana gadon mace, kamar yanda a ke gadon
dabbobi; kuma za a iya rufe ta da ranta (4) Yahudawa (Jews) sun ce
mace tsinanniya ce kuma ita ce dalilin vacewa da halakar namiji, kuma
ubanta na da damar ya sayar da ita, sannan, yahudawa na xaukar duk
wadda ke cikin jinin al’ada a matsayin najasa (5) Hindu (mutanen qasar
India) na xaukar cewa munin mace da haxarinta sun fi mutuwa, da
guba, da wuta, da maciji, kuma suna ganin wajibcin qonata tare da
mijinta idan ya riga ta mutuwa (6) Farisawa (mutanen Iran) na ganin
halaccin auren muharramai, da yanke wa mace hukuncin kisa, ba tare
da wani dalili qwaqqwara ba; kuma da nisantar da ita daga mutane a
lokacin da ta ke yin jinin al’ada (7) Nasara (Kirista) na xaukar mace a
matsayin mutum wanda ba shi da ruhi, kuma an halicce ta ne don kawai
ta yi wa maza hidima; ita ce qofar da shaixan ya ke bi domin ya vata
mutane; kuma tana rusa dokokin Allah, ta sanya maza su fanxare wa
mahaliccinsu (8) Larabawa a lokacin jahiliyya suna wulaqanta `ya`ya
mata ta hanyar bizne su da ransu ko kuma su bar su da rai, amma a
cikin wulaqanci da qasqanci, kuma suna auren matan da iyayensu suka
bari, sannan ba su ba mace gadon komai daga cikin abin da iyayenta ko
mijinta ya bari.
Musulunci na zuwa, sai ya ruguje waxannan tsare-tsare na
maguzanci, kuma ya tabbatar da adalci ga `ya mace, ta hanyar dawo
mata da mutuncinta da martabar da aka halicce ta a kansu. Allah
(Maxaukaki) Ya tabbatar da cewa mace cikakken mutum ne, wadda ta
cancanci bauta wa Allah, da yabo da zargi, da lada da zunubi, da
aljanna da wuta, gwargwadon imaninta da ayyukanta na qwarai ko
munana. Haka kuma, an ba ta damar mallakar dukiya, da yin
kasuwanci, da cin gado, da `yancin yin kyauta ko barin wasiyya. Aka
wajabta mata neman ilmi, kamar yadda aka wajabta a kan namiji, aka
ba ta damar yin musharaka da maza a wajen sallar idi da halartar jam’i.
Musulunci ya wajabta biyan sadaki a gare ta kafin a aure ta, ya tabbatar
mata da haqqoqi a matsayinta ta uwa ko matar aure ko `ya. Bayan
wannan, Musulunci ya bayyana mata cewa a vangarorin shugabancin
170
aure ko shugabancin al’umma, da annabta ko manzanci, da haila ko
jinin biqi, da xaukar ciki ko shayarwa, da rabon gado, da karvar shaida
a kotu, da sanya hijabi, tana da bambanci da namiji, bisa la’akari da
yanayin kowannensu, domin gudun kada ta xauka cewa sun yi
musharaka da tarayya a cikin kowane abu, ba tare da togaciya ba.
Musulunci ya nuna wa mace irin rawar da za ta taka, da
gudummuwar da za ta ba da wajen gina qaqqarfar al’umma.
Gudummuwar mace wajen gina al’umma na da fuskoki guda uku: (1)
haihuwa da tarbiyya domin samar da nagartattun tubalan gida al’ummar
da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) zai yi
alfahari da ita a ranar qiyama (2) samar da natsuwa da sukuni ga
mazajensu, da qarfafa wa mazajensu gwiwa a kan gwagwarmayar
rayuwa wadda ba ta sava wa manufar halitta ba (3) taimakon al’umma
a vangaren kare martaba da matsayin mata, ta hanyar ilmartarwa da
wakilci kyakkyawa, da shiga cikin ayyukan da suka dace da yanayinsu,
kamar likitanci, da jinya, da unguwar zoma, da karantarwa, da fannin
harhaxa magani.
Ganin irin matsayin da `ya mace ke da shi a Musulunci, da kuma
irin gudummuwar da mace za ta ba al’ummar musulmi, sai abokan
gaban Musulunci, musamman yahudawa da munafukai da sauran masu
mugun qulli da hassada da karkacewar tunani da fanxewar jima’i suka
fara xaukar matakin kawo varna a cikin al’amarin mace, domin su keta
suturar da Allah (Maxaukaki) Ya yi wa mace, kuma su tozarta ta, tare
da jawo mata hasarar duniya da lahira. Kuma suka kururuta `yancin
mata, wai da sunan kuvutar da su daga bautar da su ke yi a gidan aure.
Manufarsu ita ce:
1. `Yantar da mace daga ladubban Musulunci, da xaukar matakan
ganin ta yi tawaye ga dokokin Allah.
2. Watsar da hijabi, kamar yadda ya kasance a qasar Masar, a inda
mata suka jefar da hijabinsu a ranar 20/03/1919, kuma daga baya abin ya yaxu zuwa qasashen Turkiyya da Shām da Irāq, sannan, a
shekarar 1995, mata suka yi taron gangami na duniya a Peking,
domin su yi Allah wadai ga danniyar da a ke yin masu, da sunan
addini. Irin wannan farfaganda, da kiraye-kirayen shaixan, sun
sanya wa mata, musamman `yan boko, qyamar hijabi, kuma suna
xaukar sanya shi a matsayin alamar rashin wayewa.
3. Cuxanya a tsakanin maza da mata, da rashin kunya, da rashin
kamun kai, da qin yin auren wuri, duk da cewa ana yin zinace-
zinacen wuri.
171
5. Hulxa da mutanen banza da kangararrun yara da
mutanen da suka shahara da sharri, da lazimtar wuraren
da ke vata tarbiyya, kamar gidajen sinima ko wuraren
kallon finafinai da qwallon qafa.276
4. Tawaye ga mazan aure, ta hanyar fita ba tare da iznin miji ba, da
yin yadda aka so, ba tare da kiyaye haqqoqin aure da matsayin miji
ba.
5. Qirqiro kundin mata, da neman kafa dokokin da ke wa Musulunci
karen-tsaye, wai da sunan kare haqqoqin mata. Irin waxannan
kundaye da qudurorin da munafukai da sauran abokan gaban
Musulunci ke qoqarin tabbatarwa sun haxa da: tabbatar wa mace
haqqin sakin mijinta, kamar yadda maza ke da ikon sakin matansu;
da tabbatar wa mace damar yarda ko qin yarda da duk matar da za
a auro a matsayin kishiya; da taqaita adadin iyalin kowane mutum
zuwa ga matarsa ta farko da `ya`ya guda huxu; da kuma samar da
rijistar ma’aurata wadda za ta ba da damar a bibiyi halin da
ma’aura ke ciki don tabbatar da cewa ba a sava wa kundin ma’aura
ba.
Bayan wannan, kasancewar addinin Musulunci ya lulluve `ya`ya da
goma ta arziqi, ya samar da tanade-tanaden da za su kyautata
al’amarinsu, kuma ya tabbatar masu da haqqoqi a kan iyayensu,
maqiya Musulunci da sauran `yan barandarsu, sun kai gwauro da mari,
don ganin sun vata tsarin zamantakewar iyali a Musulunci. Suna bin
hanyoyi dabam daban don ganin sun jefa ruxani a cikin zukatan
Musulmi game da dacewar tsare-tsaren Musulunci, da sahihancin
karantarwarsa, da kyawun tsari, da tattalin da Musulunci ya yi wa yara.
Daga cikin hanyoyin da suka xauka, akwai nuna kamar Musulunci wai
bai kare wa yara haqqoqinsu ba, yadda ya kamata. Wannan ya sa suka
qirqiro dokar haqqoqin yara, suka yi qoqarin qaqaba wa qasashen
musulmi [duba littafi na Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin ‘Yaya a Musulunci domin samun cikakken bayani].
Ba sai an faxa ba, irin waxannan kururuwar shaixan da kiraye-
kirayen banza waxanda maqiyan Musulunci ke yi, suna da mummunar
illa, da haxari mai girma a kan makomar al’umma da kuma tarbiyyar
`ya`yanta. 276
Bayani ya gabata dangane da haxarin abokan banza, da mummunar
tasirinsu a kan tarbiyyar `ya`ya.
172
6. Mummunar mu’amalar da iyaye ke nuna wa `ya`ya.277
277
Mummunar mu’amalar da waxansu iyaye ke yi tare da `ya`yansu na
taimakawa wajen rashin tarbiyya. Idan mahaifi ya zamanto ba ya jawo
`ya`yansa kusa da shi, akwai yiwuwar ya kasa fahimtar halayensu da
qoqarinsu ko gazawarsu. Haka kuma, mummunar mu’amala da `ya`ya
na janyo wa `ya`ya dakushewar qwaqwalwa da rashin saitin tunani, da
kuma yin hulxa da mutanen banza.
Ya kamata iyaye su jawo `ya`yansu a jiki domin su saba da juna; su
riqa yin hira da su domin su ba su shawarwari ko su yi masu gyara a
wuraren da suka dace; su yi qoqarin fahimtar matsalolinsu domin su
san hanyoyin magance su; su riqa sauraron abubuwan da yara ke faxi a
cikin maganganunsu domin su yi masu saiti; su riqa yin kawaici ga
waxansu kura-kuran da `ya`yansu za su yi a gabansu a wani lokacin
domin su samu damar faxakar da su daga baya. Muhammad ibn Abdillah Al-Habdān, a cikin littafin Al-Usrah Baynal Islām wal Garb, shafi na 54-60, ya bayyana matakai guda goma
sha biyu (12) waxanda ya kamata iyaye su bi domin kyautata
mu’amalarsu da `ya`yansu. Matakan su ne:
1. Samar wa yara wajen ajiye littafan karatu (maktabah) na
musamman, wanda zai qunshi littafai masu ma’ana, tare da yin
tarayya da su wajen karatu, lokaci zuwa lokaci.
2. Keve wa yara lokacin wasa, da nuna masu wajibcin kammala
ayyukan da ke gabansu kafin su tafi wajen wasa. 3. Fita da yara domin shaqatawa, kamar yadda Aliyyu ibn Abi Xālib
(Allah Ya yarda da shi) ya kasance yana yi da Al-Hasan da Al-
Husain (Allah Ya yarda da su).
4. Tarayya da yara a cikin wasanninsu domin a samu damar yin masu
gyara. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
ya guntsa ruwa a bakinsa, sannan, ya fesa wa Al-Husain (Allah Ya
yarda da shi), shi kuma Al-Husain na gudu yana dariya. Bayan
wannan, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya kasance yana xora yara a kan bayansa domin ya yi masu
wasa. Haka nan, ya tabbata cewa yana fitar da halshensa ga Al-
Husain, shi kuma Al-Husain sai ya yi ta yin dariya.
5. Samar da darasin Alqur’ani a cikin gida ko masallaci domin a riqa
karanta Alqur’ani kuma ana qoqarin hardace shi.
6. Qarfafa masu gwiwar halartar daurah ko kevantattun tarurrukan da a ke shiryawa a waxansu lokutan musamman (kamar irin su IVC da
qungiyar xalibai musulmi ta qasa, MSS, ke shiryawa).
173
7. Kallon finafinan banza, waxanda ke vata tarbiyya.278
8. Zaman banza da rashin aikin yi.
9. Sakaci da al’amarin tarbiyya.279
10. Mutuwar iyaye.280
7. Shigar da su cikin ayyukan kasuwanci ko sana’ar da mahaifi ke yi
domin su saba tun suna qanana.
8. Kwaxaitar da su yin bincike a cikin harkar ilmi, da tafiya da su
wajen da’awa da sauraren ilmi, da tafiya da su masallaci.
9. Ba su labarai game da musulmi da Musulunci a duniya da irin
wayewa da ci gaban Musulunci.
10. Ziyartar asibiti da maqabarta tare da su.
11. Sanya masu kaset xin karatun Alqur’ani ko wa’azi, sannan, a yi
masu tambayoyi a kan kaset xin daga baya.
12. Kawar da kai daga kurakuransu a wani lokacin, domin a samu
damar yin masu gyara cikin hikima daga baya. 278
Bayani ya gabata dangane da haxarin kallon finafinai, da yadda
finafinai ke qalubalantar tarbiyyar al’ummar musulmi. 279
Bayani ya gabata dangane da yadda waxansu iyaye ke yin sakaci
game da al’amarin tarbiyya, da alamomin sakaci, da kuma haxarin irin
wannan sakaci a kan `ya`ya da iyaye da al’umma baki xaya. 280
Mutuwar iyaye na daga matsalolin tarbiyya, musamman idan iyaye
suka mutu a lokacin da `ya`yansu ke qanana, kuma ya zamanto ba a
dace da `yan’uwa ko dangi waxanda za su ji tsoron Allah game da
waxannan marayu ba.
Maraici abu ne da ke samun yara, a dalilin mutuwar iyayensu,
musamman mahaifi, a lokacin da yaran ba su kai matsayin da za su
kula da kansu ba. Idan Allah (Maxaukaki) Ya xauki ran mahaifi, kuma
aka dace da `yan’uwa na qwarai waxanda za su ci gaba da xaukar
nauyi da xawainiyar marayun, ana sa ran waxannan marayu ba za su
tozarta ba. Idan kuwa waxanda za su ci gaba da kulawa da marayun,
azzalumai ne ko kuma waxanda ba su ba al’amarin tarbiyya
muhimmanci ba, akwai yiwuwar waxannan marayu su tozarta a
vangaren addininsu da rayuwarsu.
Al’amarin maraici na da girma a cikin Musulunci. Akwai ayoyin
Alqur’ani fiye da guda ashirin da kuma ingantattun hadisai masu tarin
174
yawa waxanda suka yi magana a kan marayu, da irin haqqoqin da su
ke da shi a cikin al’umma, da muhimmancin kulawa da su, da falalar da
ke cikin xaukar nauyinsu. Misali, Allah (Maxaukaki) Ya hana a zalunci maraya ko a nuna masa fin qarfi [Dhuhā, 93:9]; kuma Ya tsawatar
game da cin dukiyar marayu bisa zalunci [Nisā, 4:10], haka nan, Ya yi
umurni da a kyautata masu, a ciyar da dukiya wajen xaukar nauyinsu
[Baqarah, 2:215]. Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi) ya bayyana cewa kulawa da marayu da xaukar xawainiyarsu,
nau’i ne na jihadi [Bukhari a cikin Al-Adabul Mufrad], kuma kyautata
masu da kulawa da tarbiyyarsu, na jawo albarkar dukiya [Bukhari da Muslim] da taushin zuciya [Xabarāni da Silsilah As-Sahīhah, 854].
Haka kuma, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi) ya bayyana cewa yana tare da waxanda ke kula da marayu, da
xaukar nauyinsu, da yin masu tarbiyya, a ranar qiyama [Bukhari].
Babu shakka, maraici na daga qalubalen da ke fuskantar al’amarin
tarbiyyar `ya`ya. Kuma ko da ya ke abu ne da ba a son aukuwarsa, dole
ne ya faru ga waxansu daga cikin mutane, tun da dai babu shakka,
kowa zai mutu.
Rayuwa a cikin wannan duniyar na da iyakantaccen lokaci, kuma
lallai ne lokacin zai zo. Wannan rayuwar kuma, lokaci ne na jarabawa
domin a bambance a tsakanin waxanda ke yin qoqarin ganin sun
rabauta a nan duniya da can lahira, da kuma waxanda za su gina
rayuwarsu a kan sharholiya [Mulk, 67:2].
Mutuwa ita ce matakin farko na zuwa lahira, kuma babu makawa sai mutum ya mutu. Mutuwa babbar musiba ce [Mā’idah, 5:106], wadda ke
yanke jin daxi [Tirmidhi], kuma tana da raxaxin gaske [Qāf, 50:19].
Babu wani rai face sai ya xanxani mutuwa [Aal Imrān, 3:185]; babu
wanda zai kuvuce mata [Juma’ah, 62:8]; kuma ko’ina mutane suka shiga, kowa sai ya mutu [Nisā, 4:78] har sai duniyar ta qare gaba
xayanta, in ban da fuskar Allah [Rahmān, 55:26-27; Qasas, 28:88].
Kowane rai na da iyakantaccen lokacin da zai mutu [Aal Imrān, 3:145],
kuma babu wanda ya san lokacin mutuwar sai dai Allah [Luqmān,
31:34], to amma, idan lokacin ya zo, za a mutu, ba tare da qarin lokaci ko ragi ba [Munāfiqun, 63:11; A’arāf, 7:34], sannan, da zarar an mutu,
babu dawowa cikin wannan duniya [Mu’uminūn, 23:99-100].
Kusan kowane xan Adam yana zullumin mutuwa, galibi, saboda
rashin sanin abin da za a tarar bayan an mutu, ko da ya ke ana buqatar
mumini ya kyautata zato ga Allah (Mai girma da xaukaka). Wani
lokaci, zullumin na da alaqa da makomar `ya`ya bayan iyayen sun
mutu, musamman idan babu manyan `ya`yan da za su kula da qanana.
175
KAMMALAWA
Wannan shi ne abin da Allah (Mai tsarki da xaukaka) Ya
bani ikon rubutawa game da tarbiyyar `ya`ya a Musulunci.
Ina roqon Allah Ya karvi wannan xan aiki nawa, kamar
yadda ni ke roqonSa falalarSa, da karamcinSa, da
rangwamenSa, da gafararSa.
Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabanmu
Muhammad, da mutanen gidansa da Sahabbansa da
waxanda suka bi hanyarsa har zuwa ranar Qiyama.
Alhamdu lillah.
Sau da yawa, ana samun mugayen `yan’uwa ko dangi waxanda ke
tozarta haqqin maraya, da nuna masa bambanci, da rashin xaukar
nauyin karatunsa yadda ya kamata, da rashin damuwa da tarbiyyarsa,
da rashin kulawa da lafiyarsa, da yin rib da ciki a kan dukiyarsa, ta
yadda maraya zai shiga cikin wani mummunan hali. Irin waxannan
azzalumai, ba su tunanin mutuwa? Sun manta cewa za su mutu? Za su
so a yi wa nasu `ya`yan irin wannan zalunci bayan mutuwarsu? Ba su
tsoron haxuwarsu da Allah (Mai girma da xaukaka) a ranar qiyama? Ba
su gudun kunyata tun a nan duniya?
176
DAGA CIKIN LITTAFAN DA AKA YI AMFANI DA SU
Alqur’ani Mai Girma da Littafan Hadisi Abdullah Nāsih Ulwān, Mas’uliyyatut Tarbiyyatil Jinsiyyah
min Wijhati Nazaril Islam, Dārus-Salām lix-Xibā’ah
wan-Nashr wat-Tauzi’ wat-Tarjamah, Al-Qāhirah,
2003 Abdullah Nāsih Ulwān, Tarbiyyatul Awlād fil Islām, Dārus-
Salām lix-Xibā’ah wan-Nashr wat-Tauzi’ wat-
Tarjamah, Al-Qāhirah, 2005
Abdullahi Qādiriy Al-Ahdal, Daurul Masjid fit Tarbiyyah,
Dārul Mujtama’, Jeddah, 1407
Abdur-Rahmān An-Nihlāwiy, Usūlut Tarbiyyatil Islāmiyyah Wa Asālībuhah, Dārul Fikr, Dimashq, 1983
Ahmad Bello Dogarawa, Ni’imar Haihuwa da Haqqoqin `Ya`ya a Musulunci, Amanah Printing Limited,
Kaduna, 1426AH Ahmad ibn Abdil-Halīm ibn Taimiyyah, Hijābul Mar’ah wa
libāsuha fis-Salāh, Ta’alīq Muhammad Nāsiruddīn
al-Albānī, Al-Maktab Al-Islāmī, Beirut, 1985
Ahmad ibn Abdil-Halīm ibn Taimiyyah, Majmū’ul Fatāwā,
Maktabah Ibn Taymiyah, Al-Qāhirah, 1980
Ahmad ibn Abdil-Halīm ibn Taimiyyah, Iqtidā’us Sirāxil Mustaqīm, Wizārah ash-Shu’ūnil Islāmiyyah, Saudi
Arabia, 1999 Ahmad ibn Abdil-Halīm ibn Taimiyyah, As-Sārimul Maslūl
alā Shātimir Rasūl, Dārul Hadīth, Al-Qāhirah, 2003
Ahmad Musxafa Mutawalli, Al-Mausū’atul Āmm fi Tarbiyyatil Aulād fil Islām, Dār Ibnil Jauziy, Al-
Qāhirah, 2005
Al-Lajnah ad-Dā’imah lil Buhūth al-`Ilmiyah wal Iftā, al-
Idārah al-`Aamah lix-Xibā’i wat-Tarjamah, Saudi
Arabia, 1411AH As’ad Ismā’īl Aliyy, Usūlut Tarbiyyatil Islāmiyyah, Dārus
Salām, Al-Qāhirah, 2005
177
Bakar Abdullah Abu Zaid, Hadduth-Thaub wal Uzrah wa Tahrīmul Isbāl wa Libāsish-Shuhrah, Maktabah as-
Sunnah, Egypt, 2001 Bakar Abdullah Abu Zaid, Hirāsatul Fadīlah, Dārul Āsimah,
Riyād, 2005
Bakar Abdullah Abu Zaid, Tas-hīh Ad-Du’ā, Dārul Āsimah,
Riyād, 1999
Khālid Hāmid Al-Hāzimiy, Usūlut Tarbiyyatil Islāmiyyah,
Dār `Aalamil Kutub, Riyadh, 1421
Khālid Shantūt, Daurul Bait fi Tarbiyyatix Xifl Muslim, Dārul Maxbū’atil Hadīthiyyah, Jeddah, 1990
Laylā Bint Abdir-Rahmān, Kayf Turabbiy Waladak,
http://www.islamhouse.com/files/ar/ih_būks/single/ar
_How_raising_and_son.doc.
Mājid Arsān Al-Kailāniy, Ahdāfut Tarbiyyatil Islāmiyyah,
Mu’assasatur Rayyān, Beirut, 1998
Miqdād Yālijn, Ahdāfut Tirbiyyatil Islāmiyyah, Dārul
Hudā, Riyadh, 1989
Muhammad Abdus-Salām Khidir as-Shuqairī, As-Sunan wal Mubtadi’āt, Dār al-Fikr, 1352AH
Muhammad Ad-Duwaysh, Al-Asālibut Tarbawiyyah inda Rasūlil Bashariyyah,
www.quran.maktūb.com/vb/quran22761
Muhammad As-Suhaim, Min Akhxā’inā fi Tarbiyyati Aulādinā, Dārul `Aasimah, Riyadh, 1415
Muhammad ibn Abdillah al-Habdān, Al-Usrah baynal Islām wal Garb, Dār Ibn Khuzaimah, Riyadh, 2001
Muhammad ibn Abi Bakr ibn al-Qayyim al-Jawziyyah, Ahkām Ahliz Zimmah, Dārul Hadīth, Al-Qāhirah,
2003
Muhammad ibn Abi Bakr ibn al-Qayyim al-Jawziyyah, Al-Wābilus Sayyib, Al-Maktabuth-Thaqāfi, Al-Qāhirah,
2003
178
Muhammad ibn Abi Bakr ibn al-Qayyim al-Jawziyyah, Jilā’ul Afhām fis Salāti Wassalāmi ‘ala Khairil Anām, Dārul Arubah, Kuwait, 1987
Muhammad ibn Abi Bakr ibn al-Qayyim al-Jawziyyah, Tuhfah al-Maudūd bi Ahkām al-Maulūd, Maktabah
al-Qur’ān, al-Qāhirah, 1987
Muhammad ibn Ibrahim Al-Hamd, At-Taqsīr fi Tarbiyyatil Aulād: Al-Mazāhir, Subulul Wiqāyah wal Ilāj, http://www.sāid.net/būk/open.php?cat=82&būk=809
Muhammad Munīr Marsī, At-Tarbiyyatul Islāmiyyah: Usuluhā wa Taxawwuruhā fil Bilādil ‘Arabiyyah,
‘Ālamul Kutub, Al-Qāhirah, 1421
Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī, Jilbābul Mar’atil Muslimah fil Kitāb was Sunnah, Dārus Salām, 2002
Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī, Sifah Salātin Nabiyy,
Maktabah Al-Ma’ārif, Riyād, 1991 Muhammad Nūr Suwaid, Manhajut Tarbiyyatin
Nabawiyyah Lix Xifl, Maktabatul Manāril
Islāmiyyah, Kuwait, 1988
Muhammad Sa’īd Maulawiy, Kayf Yurabbil Muslim Waladah? Maxba’ah Ramādiy, Damām, 1995
Najīb Al-`Aamir, Min Asālībir Rasūl fit Tarbiyyah, Al-
Bushral Islāmiyyah, Kuwait, 1990
Sālih As-Sadlān, Al-Masjid Wa Dauruh fit Tarbiyyah Wat Taujih, Dār Bilansiyyah, Riyadh, 1994
Sālih ibn Aliyyu Abu ‘Arrād, At-Tarbiyyatul Islāmiyyah: Al-Musxalah wal Mafhum, 1426, http://sāid.net/Doat/arrad/17.htm
Sālim Aliyyu Rāshid ash-Shabalī da Muhammad Khalīfah
Muhammad ar-Rabāh, Ahkāmul Maulūd fi as-Sunnah al-Muxahharah, Al-Maktab Al-Islāmī,
Beirut, 1994 Samīr Abdul-Azīz, Manhaj al-Islām fi Tarbiyyatil Awlād,
Dār Ibn Rajab, Egypt, 1999
179
Shamsuddīn Az-Zahabī, Mukhtasār Al-`Uluw lil Aliyyil Ghaffār, Tahqeeq Muhammad Nāsiruddīn al-Albānī,
Al-Maktab Al-Islāmī, Beirut, 1991
Sihām Mahdiy Jabbār, Ax-Xifl fish-Sharī’atil Islāmiyyah Wa Manhajut Tarbiyyatin Nabawiyyah, Al-
Maktabatul Asariyyah, 1997 Ummu Hassān Al-Hulw, Akhxā Tarbawiyyah Shā’i’ah, Dār
Ibn Hazm, Beirut, 1994